Showing 60001 words to 63000 words out of 231718 words
Chapter 21 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt
Angel" ta kallesa tace "And then?" Ya ware shoulder irin Nothing ɗin nan.
A tare suka jera kayan abincin akan dining room suna kammalawa Salman ya zauna yana faɗin "zuba min abincin" hannu tasa ta dungure masa kai tana faɗin "Food, food, food. stop eating too much" Salmanun-faris girgiza kai ya yi yana tsiyaya Juice a cup a hankali yake sipping Juice ɗin kafin ya ce "gwara na zama ƙatoto yadda za kifi yadda da abinda zan zo maki da shi" Abra tai shiru can kuma tace "like how?" Yana ɗaukan spoon ya ce "With time"
Kafin wani ya ƙara magana a cikinsu Mami ta ƙaraso wajan hannunta riƙe da waya cikin wani dakakken lace idanunta akan Abra tace.
"Ok zan turo ta yanzu, kada ki damu kawai ki Ajjiye min aini nace ina so kuma wannan haɗin ya yi" jim tayi sai kuma tace "Ni bani da damuwa, kuma nasan Man zai amince so kada ki damu kici gaba da tsara komai" shiru ta sakeyi alamar tana sauraran mai maganar daga cikin wayar tace "Shi ke nan, ki ɗan jira yanzu ne in sha Allah" tana faɗin hakan tayi hanging up na kiran Idanunta still akan Abra tace.
"Daughter"
Ba Abra ba hatta Salman sai da ya ɗaga idanunsa ya kalli Mami, abin yazo musu unexpected ya zama wani extraordinary a gare su, ko sunan Abra da wahala aji Mami ta faɗa amma yau ita take kiran Abra da Daughter? Tsananin murna yasa Abra har wani hawaye Idanunta ya tara muryarta na rawa tace "Na...n... na'am Mami" Mami tai Murmushi ta kama Hannun Abra tace "Be patient my dear, zan aikeki gidan Hajja Amina yanzu kinji" Abra ta ɗaga kai da sauri tace "Ok Mami bari na shirya" da sauri Salman ya miƙe tsaye.
"Mami aike kuma? Yaya zaki aika bayan Abbi yace kada ta dinga fita, kuma ba gani ba ki faɗa min aiken yanzu naje na amsu maki" Mami tace "ai na ganka ko ka taɓa ji ance ni makauniya ce, bana kula Abra ace bana sonta idan na nemi kusanci da ita kuma a fara wani zance, kada ka sake ina magana kana saka min baki Salman it will be the last time da zakai min haka" Salman ya buɗe baki zai magana Abra ta girgiza masa kai tace "No Faris,stop arguing with your mother. Ka bari yanzu zanje na dawo" idan ran Salman ya yi dubu to ya ɓaci idanuna tuni ya yi jajur sbd saɓar abinda yake ci masa zuciya, a fusace kuma ya nufi waje zai fita ganin haka yasa Mami faɗin "kada ka kuskura kabar gidan nan, tunda ni Matsayin Shasha ka ɗauke ni" juyawa yayi daga inda yake zuwa bedroom ɗin sa, ganin hakan yasa Mami kallon Abra tace "Kaya zaki amsu min wajan Hajja Amina, kada ki sake ki dawo ba kayan saura ki tsaya a hanya"
"Yanzu zan dawo, bari na ɗakko mayafina driver ya kaini" "A'a ba wani driver, ka kuɗi zan baki ki hau napep ok?" Ta ɗaga kanta 1k ta miƙa kuɗin napep tana bata ta nufi dining room. Abra kuma ta juya zuwa bedroom ɗin ta. Tana tsaye gaban mirror zata ɗauki turare ta fesa a jikinta ya yi saurin riƙe hannunta mai ɗauke da turaren, kallonsa tayi sai da gabanta ya faɗi ganin irin kallon da yake binta da shi. Wardrobe ɗinta ya buɗe ya ɗauki wani ƙaton hijab har ƙasa bakinta na rawa tace "Ni ba zan saka hijab ba gsky" idanuna cikin nata ya ce "Ni kuma nace sai kin saka" murguɗa masa baki tayi tace "Ni ba zan saka ba, kana wani abu kamar kaine yanae, shekara uku na baka yaro sai son girma da manyan can Masifa" Salman na warware hijab ɗin ya ce " say whatever you want to say, but kada ki sake ce min yaro age is just a number ba'a goshi ake rubuta su ba"
"Idan na kuma faɗa me zakai min? Kwana biyun nan naga ka fara raina ki ko? Sbd kana kallonka ƙato babu mai cewa nice babba shine kake son faɗa min abinda kayi niyya" bakinta dake ta motsawa yana zuba masifa yake bi da kallo sai da ta kama faɗan ta ce "kuma sai ka faɗa min abinda zakai min idan na sake faɗa" girgiza kai kawai ya yi ba zato taji gaba ɗaya ya ɗaga ta cak ya dire ta a gabansa tare da kama ƙugunta ya saka mata mayafin. Yana gamawa kamar sai saketa sai ya ɗora bakinsa a saitin kunnanta ta cikin hijab ɗin ya ce.
"Yaa Subuhanallah!
جعلنا الله معًا إلى الأبد"
Wato “Ubangiji ya Sanya mu kasance tare har abada” Abra hankalinta baya jikinta murna take yau Mami ta aiketa dan haka bata tsaya tantance maganganun na Salman ba tayi waje sanye da ƙaton hijab.
Abra na barin gidan motocin Major Khamal Khamis suna shigowa, wani soja ya buɗe masa ƙofa ya Fito dake gaba ma'aikatan gidan sojoji ne.
Cikin nutsuwa Abbi ke tafiya zuwa gidan yana shiga Mami ta miƙe tsaye, da ɗan sassarfa ta nufi wajan Abbi tare da rungomesa tana faɗin "Wlcm Back Yallaɓai na" Murmushi ya yi yace "Thank you Madam" Jin shiru yasa yace "Ina Daughter,ina Salman?" Tace "Salman na nan baya jin daɗi, Abra na aiketa tun ɗazo naji shiru amma nasan tana hanya"
Shiru ya yi yana son fahimtar zan can nata sai kuma ya ce "Ok, lemme take a shower" bayansu tafi har zuwa sashinsa ta haɗa masa ruwan wanka. Bayan ya yi wanka yana cikin cin Abinci yaga ta zabga tagumi yace "Meke faruwa Madam?" Ta girgiza kai ya kama hannunta ya ce "please" ajjiyar zuciya ta sauke ta ce "Ko Abinci yau Abra bata samu yi maka ba, jiya da yau idan na aiketa sai ta shafe wasu lokuta bata dawo ba" Ajjiye spoon ɗin hannunsa ya yi cikin damuwa ya ce "ita Abra? To ina take tsayawa?"
"I have no idea. Bari na kira Hajja Amina" wayarta ta ɗauka ta kira Hajja Amina tana ɗauka tace "Hajja Amina me Abra take har yanzu shiru?" Hajja Amina tai salati da ga cikin wayar kasancewar a Speaker Mami ta saka tace "Wacce Abra kuma ni Amina, yarinyar da ko minti biyar ba tayi ba ta amshi kayan ta fita tace akwai inda zata daga nan gidan" kashe wayar Mami tayi ta ce "To ina yarinyar nan tayi?" Kasa cewa komai Abbi ya yi sai miƙewa kawai da yai tare da nufar sashinsa.
Ana ƙwala kiran Sallar Magrib Abra na shigowa cikin Main Parlour sai da gabanta ya faɗi ganin Abbi tsaye fuskarsa babu walwala wani irin kallo yake binta da shi, musamman da yaga leder shopping a hannunta. Bakinta na rawa tace "Sannu da dawowa Ab..." Tau!!!!! Abbi ya ɗauke Abra da mari wanda ya sanya tayi baya zata faɗi cikin sauri Salman ya tareta ta faɗa jikinsa, Wani marin Abbi ya ƙara saukewa Abra daya sanya ta saki wata gigitacciyar ƙara tare da saka hannu gaba ɗaya ta ƙanƙame Salman. Wani irin kukan Abra ta fashe dashi bakinta sunan Faris yake faɗa akan ya taimaketa daga dokan Abbi.
"Wato har kinyi girman da za'a aikeki ki tsaya yin shopping da wani? Yaushe kika zama haka Abra? Ina tarbiyyar da nayi maki kuma yanzu yanzu ki haɗiye kukan nan ki faɗa min Shegen daya kaiki shopping Wlh yau a ɗaure zai kwana, ba zai taɓa yiyuwa ina tufka wani yana warware min ita ba, ba zai taɓa yiyuwa ba" bakinta na rawa jikinta na ɓari tace "Abbi kayi haƙuri, wlh babu wanda nabi ɗan gidan...."
"Shut up" Mami ta daka mata tsawa tare da faɗin "tun ɗazo na kira Hajja Amina tace ko minti biyar baki ba a gidanta, shine yanzu zaki shirya ƙarya domin kare kai fita a nan kiban waje" da gudu ta saki Salman ta nufi bedroom ɗin ta, Salman kallon Mami kawai yake domin har ransa bai yarda da wannan zan can ba akwai abinda yake faruwa. Juyawa ya yi zuwa masjid ɗin domin yin sallar Magrib.
Kuka kawai Abra take lallashin duniya Salman ya yi amma taƙi yin shiru, da ƙyar ya lallaɓata tai sallah ya faki Idanunta ya saka mata maganin bacci cikin ruwa tana sha bacci ya yi gaba da ita.
Da Subhi bayan ta tashi da ƙyar saboda nauyin da Idanunta ya yi mata, bayan tai wanka tare da yin tana zaune saman sallaya aka turo ƙofar ɗakin tare da shigowa. Ƙamshin turarensa da taji yasa bata ɗago kanta ba, haka kurum ta tashi da ƙuncin zuciya.
Zama Salman ya yi a gefen inda take zaune Murya a ƙasan maƙoshi yace.
"Sabahul khair Angel"
Ba tare data kallesa ba Idanunta akan Azkar ɗin da take tace "Ka tashi lafiya?" Bai amsata ba domin shi kaɗan yasan yadda yake bacci kullum shiru ne ya biyo baya kafin Salman ya kau da tunanin zuciyarsa ya ce.
"Wane ya yi maki shopping?" Sai a wannan lokacin ta ɗago kanta suka haɗa idanu ita kanta tai Mmkin yadda fuskar Salmam tai jajur idanunsa ya kumbura Sbd rashin bacci.
"Ina tambayarki kin tsaya kallo na kamar baki sanni ba?" Juyowa tayi baki ɗaya tare da kallonsa cikin sakin fuska tace "Maybe bana ɗaya daga cikin mutanan da za su yi farin ciki a duniya, ƙilan rabona sai bayan bana numfashi Salman" tana faɗin hakan ta miƙe tsaye hannunta riƙe da Alkur'ani bayan ta Ajjiye ta juya zata fita zuwa kitchen. da sauri Salman ya rufe ƙofar tare da murɗa key a jiki. Hannayensa ya harɗe a ƙirji idanunsa akan Abra da tayi tsaye tana binsa da kallon Mmki.
"If I am alive, you must be happy" a hankali ya matsa inda take idanunsa cikin nata ya ce "Ki faɗa min wanda ya yi maki shopping da kuma yadda kika daɗe a waje" banza tayi masa. "Ki faɗa min" a hassale tace "Salman ka barni dame zanji ne pls? Ka barshi a wani nabi shi ke nan....," gigitacciyar tsawar da Salman ya daka mata ya sanya tayi sauri rufe bakinta jikinta ya ɗauki rawa da ɓari, shi ne karo na farko da ya ɗaga mata Murya harda tsawa bata san lokacin data fashe da kuka ba tana durƙoshewa a wajan.
Ran Salman a ɓace gaba ɗaya ta gagara fahimtarsa, idan har bai Ajjiye girmansa da tayi ba, to ba zai iya kulawa da ita ba kamar yadda ya yi zuciyarsa Al'ƙawari, durƙosawa yyi tare da ɗago ta tsaye muryarsa babu wasa ya ce.
"You will not cry for me. Amsa zaki bani Abra amsa nake buƙata" muryarta na rawa tace "Bayan naje gidan Hajja Amina muka gaisa tai shigewarta ɗaki a nan naita zama, sai dab da magrib ta saka ɗan ta ya ɗauke ni wai shine zai ban saƙon, ganin Aiken Mami ne ban damu ba, shine ya kaini Sadaraki store yai shopping tare da bani wai shine aiken...," Kukan da yaci ƙarfinta ne ya sanya ta kasa ci gaba da magana wani irin kuka take wanda ta daɗe ba tayi kamarsa ba.
Ganin yadda take kuka har tana shiɗewa kamar numfashinta zai fita ya sanya a fusace Salman ya jawota jikinsa tare da rungometa Tsam-tsam a jikinsa, zuciyarsa na wani irin bugawa kamar zata faso ƙirjinsa ta fito idanunsa ya yi wani masifar jaa kamar gauta jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa saman goshinsa numfashi kawai yake fitarwa.
"You shouted at me,after I am innocent" ta ƙare maganar tana sakin wani irin kuka tana ƙara ƙankame jikin Salman, domin a wajansa kawai take samun sauƙi. Faɗa masa ne kawai ba tayi amma tuntuni ta yarda cewa shine ragamar rayuwarta da babu shi ta tuni Zuciyarta ta buga.
Muryarsa bata fita sosai ya ce "I'm sorry Yaya" yana faɗin hakan ya zareta daga jikinsa kamar walƙiya haka ya ɓace daga ɗakin yana zuwa bedroom ɗin sa, Wayarsa ya ɗauka tare da kiran number Ammi bayan sun gaisa ya faɗa mata dake faruwa. Granny dake gefe hankali tashe tace. "Huhuhu idan ban kaɗa Na'ima gidansu ba yau to wlh kuce ƴar banza ce ni, Ubangiji ya yi gutsi gutsi da Zuciyar Na'ima. Zan aurawa Kamalu Babura sai naga ƙaryar iskanci" tana faɗin hakan ta miƙe tsaye yana ɗaukan mayafi tace "A'isha kike kowa masa kira salamamman drivern can ya kaini gidan Kamalu a yau shima shi ya gane cewa ni ba tsohuwar banza bace duk yadda ka ke da kiyaye harshenka sai an saka kayi saɓon Ubangiji" sai kuma ta fashe da kuka tace "Da ƙyar Na'ima taga Ubangiji da ƙyar ne ta kansa".
Tahir guest palace.
Room 36.
Yana kwance sanye da red ɗin Armless wacce ta bayyanar da faffaɗan ƙirjinsa. A hankali ya mirgina tare da yin rufda ciki yana ɗan lumshe idanunsa.
Ta cikin system ɗin dake gabansa Muryar Abba ta fito yace "Na faɗa cewa zani England,Follow the flight today and come back to Kaduna" Sp Adnan ya ware idanunsa dake cike da bacci a hankali ya Kalli fuskarsa mahaifin nasa ta cikin vedio call ɗin da suke "Abba ba yau zan dawo ba, kuma akwai mota tare dani" cike da damuwa Abba ya ce "How many times do I have to tell you that I don't like long car journeys" Murmushi Adnan ya yi cike da so da ƙaunar mahaifin nasa ya ce "Abinda Ubangiji ya ƙaddara zai samu bawa dole ya samesa ko a jirgi ne, just pray for me"
"Ok I'll, When will you come back?" Adnan na hargitsa sumar kansa idanunsa rufe ya ce "Ni ọsẹ kan tabi meji" Murmushi Abba ya saki yana kallon Hajiya Mama dake gefensa ya ce "Yau ɗanki ya tuna da yaran mahaifiyarsa" Hajiya Mama tayi dry tace "kyan ɗana daman ya gado mahaifiyarsa" Abba yana kallon Adnan ya ce "Idan ɗan ya kasance mace ko? Ɗa namiji kam Ubansa yake kwaikwayo" Murmushi kawai Adnan yake wa iyayen nasa
"Me zaka zauna yi a Kano har bako guda?"
Miƙewa zaune Sp ya yi cikin kwaɓe fuska ya ce "
"An investigation brought me to Kano, who I suspect is in the University" Abba ya ce "Ikon Allah. To Allah ya taimaka ya yi maka jagora please My son is rage zafin zuciya" da idanu kawai Sp yabi Abba "yanzu yaya za'ai ka kama criminal ɗin?" Adnan ya ɗan yatsuna fuska ya ce "I have a plan Abba.. bye take care of yourself" yana faɗin hakan ya kashe system ɗin tare da Miƙewa ya nufi bathroom, wanka ya yi ya shirya cikin wasu ƙana nan kaya Sleeveless tank top da tracksuit trousers ya ɗora white p.cap a saman sumar kansa, sai Ƙamshin Pur oud yake.
Wayarsa ce ta fara ringing ganin sunan Fayyad ya Sanya bai ɗaga ba, hannunsa ya miƙa ya ɗauki I.d card ɗin dake gefen gado, ƙyakkyawar Fuskarta yabi da kallo kafin a hankali yaja idanunsa ya rufe yana sauke numfashi. I.d card ɗin ya saka cikin Aljihu kana ya fita daga Room ɗin cikin sassarfa ya fara sauka daga kan strains ɗin 3 floor. Ganin zai ɓatawa kansa lokacin ya tsaya ya shiga elevator tare da danna 1floor. Yana sauka reception Wayarsa ya fara ƙara ganin sunan Abba yasa ya tsaya tare da ɗaga kiran.
"Son ka kula da kanka, ka rage zafin zuciya. Shine Abinda zaka faɗa ko Abba na riga na haddace fa" ta cikin wayar Abba ya yi Murmushi ya ce "ba zaka gane ba, Allah ya yi maka albarka" Adnan ya ce "Amin, Bye." Motar gabansa ya buɗe tare da shiga yana ji Fayyad ya daki kafaɗarsa ya ce. "Ban taɓa sanin baƙar fata duniya bace sai a kanka Adnan, kaga yadda kayi kyau"
Adnan dai bai ce komai ba.
"Jiya ka kirani kana son magana dani"
Adnan ya jinjina kansa yana rufe idanu, Fayyad ya ce "Ok bari muje gidana muyi magana, da ga nan sai ku gaisa da Madam"
Adnan dai bai ce komai ba, Fayyad ya ƙarawa motarsa wuta babu jimawa suka kawo cikin estate ɗin Motar Fayyad na shigowa ciki Motar Granny da driver ya kawota na danno kai cikin estate da sauri Fayyad ya daka burki ganin motar dake bayansu ta tawo da sauri ta nufi gidan dake kusa da nasa. Adnan ya buɗe idanu da sauri yana jan tsaki. Fayyad ya ce "Wannan driven mahaukaci ne" Adnan ya ƙara jan tsaki ya ce "Ƴan Nigeria ke nan" kafin Fayyad ya yi Magana sunga wata tsohuwa ta tsaya gaban motarsa ta fara Masifa.
"Wani gantallan ne wanda bai san darajar rai ba ke neman salwantar da tawa rayuwar? Kasan nawa ɗana ya sai motar nan kowa? Mutane suyi ta abu daka kamar marasa wadataccen ilimi. Nifa daidai nake da ko wanne ɗan kwalta Alkur'an sai na kwaɓe mu daku kawai kowa ya yi ta kansa" Salman da ya fito daga cikin gidansu ya yi saurin kama hannun Granny sukai cikin gidan. Adnan dai idanunsa a ƙasa Fayyad babu abinda yake banda dry yana buga cinya. Adnan ya ɗaga idanunsa ya ce "Old version ce fa motar masifaffiyar Tsohuwa" kamar ya faɗa a kunan Granny sai gani sukai ta fito daga cikin gidan a guje ta ce "Kaga masifa akanka wallahi li'ilafi qurash" tana faɗin hakan tai cikin gidan tana Masifa son ranta. Shi kansa Sp sai da abin bashi Murmushi kasancewar ba ɗabi'arsa bane sai kawai ya Girgiza kai. Fayyad ya Ƙarasa shigar da motarsa cikin gidan nasa gaba ɗaya suka nufi ciki.
Tunda daga bakin ƙofa Granny ta gyara zaman ɗan kwalinta. Kai tsaye Granny ɗakin Na'ima ta nufa babu jimawa ta dawo hannunta riƙe da mayafi, cillawa Na'ima tayi ta koma ta ƙara ɗakko hand bag itama ta cillawa Na'ima.
"Maza maza kama gabanki wlh Wlh yau koni ko ke, ke babu ruwana ni ba ƴar banza bace dole ki yi yaji yau"
Abbi ya ce "Mene ya faru Granny?" Granny ta runste idanunta ta ce "Ni da Ubangiji na kawai muka san abinda ya faru, kuma a satin nan zanwa Kamalu aure. Idan ki kaga banwa Kamalu aure ba cikin satin nan kice ni ba haifaffiya bace cikin uwata"....
LITTAFIN DARE DA DUHU NA KUƊI NE, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank.
KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750
DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 07063065780\09047871750
MUNGODE.
[10/1,