Showing 111001 words to 114000 words out of 231718 words

Chapter 38 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt

28 Feb 2025

14811

Sai kusan Magriba suka tafi suna ta tsokanar ta wai kar Ango ya dawo ya same su ya yi musu korar kare, ita dai murmurshin yaƙe kawai take, sai ta ji dama kar su tafi.


Ba ta zauna ba sai da ta tsaftace gidan ta saka turaren wuta a burner, hakan ya sa gidan gabaɗaya ya karaɗe da ƙamshi. Bayan ta yi Sallah ta yi wanka ta shirya cikin wani tsadadden yadi mai kyau maroon color, ya yi mata sosai ya haska farar fatarta. Parlour ta fita ta jera abinci akan dinning sannan ta koma ta yi Sallar Isha'i da aka fara kira. Tana idarwa ta janyo wayarta dan ta kira Abbi amma ta tarar wayar a kashe, ta manta tun jiya wayar babu chaji ta mutu. Chajin ta jona ta zauna jiran ya ɗan yi, Salman ne ya faɗo mata a rai. A fili ta ce. "Kana ina My Faris? Me kake yi yanzu? Me ya sa ba ka kira ni ba tunda ka tafi? Yaushe zaka dawo ka zo gidana in gan ka ɗan ƙanina? Na yi tsananin kewar ka." Daga haka ta fashe da kuka.


Khamal na zaune a parlour'nsa shi da Na'ima wadda zuciyarta ke cike da tsananin farinciki, jin ta take kamar a mafarki yau Allah ya yi Abra ta bar mata gida, shikenan fargabarta ta ƙare. Sai dai tuno letter Salman da ta gani ya sa gabanta fad'uwa da ƙarfi, ta rasa me ya sa abun ya dame ta? Dan da farko shirme ta ɗauki abun, saboda sanin komai daren daɗewa dole Salman ya neme su, ba kuma zai taɓa iya yin zuciya da su ba, letter da ya yi mata dan yana cikin ɓacin rai ne, abun yana cin shi a lokacin shi ya sa, amma ta san idan tafiya ta yi tafiya komai zai wuce. Khamal yana duban ta ya ce. "Komai lokaci ne, kamar ba yau ake zancen bikin Daughter ba, ga shi har an yi an gama, ta tafi ta bar mu da kewar ta. Cikin kissa Na'ima ta ce. "Ta bar mu da kewa kam, don gidan babu daɗi yanzu ko kaɗan, ga ba Salman." Khamal ya nisa ya ce. "Har kin tuna mini kuwa, na kai sati ina trying his number ba ta shiga, amma na kira mutumin da ya kira ni da numbern shi lokacin da ya sauka a garin, ya ce mini neighbours suke, idan sun haɗu zai kira ni ya haɗa mu." Murmushi Na'ima ta yi ta ce. "Allah Sarki yaron kirki, Allah ya tsare mana shi." Khamal ya amsa da Amin tare da zaro wayarsa daga aljihu ya kira layin Abra amma sai aka ce masa a kashe, tun rana yake kira ta ba ta shiga. Numbern Adnan ya kira, dan ya san duk sabon ango i yanzu yana gida. Bayan ya ɗaga suka gaisa cikin mutuntawa, Khamal ya tambayi Abra, Adnan ya tabbatar masa tana nan ƙalau, wayarta kuma babu caji ne shi ya sa bai same ta. Khamal ya buƙaci Adnan ya ba wa Abra wayar, sai ya ce ya ɗan fita, idan ya koma gidan zai haɗa su, daga haka suka yi sallama.




Tana zaune takure a bakin gado ta yi tsumu cikin alamun tsoro, ita kaɗai a gida har tara ta yi amma babu Adnan babu labarin shi. Ƙwaƙwalwarta har ta gaji da tunanin dalilin da ya sa Adnan yake yi mata haka, kanta kamar zai tsage saboda ciwo. Unexpected ta ji an buɗo ƙofar ɗakin an shigo, lumshe ido ta yi cikin jin daɗi dalilin shaƙar ƙamshinsa, a hankali ta buɗe idonta ta kalle shi, yanda ta ga ya murtuke fuska ne ya sa gabanta mummunar faɗuwa, amma duk da haka ta daure cikin raunin murya ta ce. "Sannu da zuwa." Ta ƙarashe maganar hawayen da take ƙoƙarin ɓoyewa suna zubo wa. Bai kula ta ba, wayarta dake chaji kawai ya ɗauka ya fice. Da ido ta bi shi cikin kokawa da numfashinta dake barazanar ɗaukewa. Innalillahiwa'inna'ilaihirra'un ta shiga maimaitawa hannunta dafe da kanta, wani irin raɗaɗi da zafi take ji a cikin zuciyarta. Tambayar kanta ta shiga yi, dama haka Auren yake? Ko kuma ita kaɗai ta fara da matsala? Ina tarin ƙauna da soyayyar da Adnan yake yi mata? Ina tanadin kulawa da tattalin da ya ce ya mata? Ko dai mafarki take yi? Ta rasa da wanne za ta ji, da rashin Faris a kusa da ita ko kuma da kewar su Abbi ko da abun da Adnan yake mata? Sunan Allah ta dinga ambata har ta ji sauƙin radad'in da zuciyarta ke mata. So take ta tashi ta je gurin Adnan ta ji me ta yi me masa? Amma a yanda take jin jikinta kamar ba nata ba ta san ba za ta iya tashi ba. Kwanciya ta yi saboda juyawar da kanta yake yi mata.


Wannan shi ne dare mai tsayi da muni da Abra ta gani a rayuwarta, dan bacci duk iya satarsa bai sace ta ba. Nasihar Ammi da ta ce ta dinga tashi cikin dare tana yin Sallah ko raka'a biyu ce ta dawo cikin kwanyarta, hakan ya sa ta lallaɓa ta tashi ta shiga toilet ta ɗaure alwala ta raya daren, ta kai wa Ubangiji kukanta tare da roƙon ya kawo mata ɗauki. Bayan an yi Sallar Asuba ta ɗauko alƙur'ani mai girma ta karanta, bayan ta gama ta yi azkar ɗinta. Hakan ya sa ta ji sauƙin damuwar dake cunkushe a cikin ranta. Sai kusan takwas ta fita parlour bayan ta yi wanka. Gyaran gidan ta fara yi cikin matuƙar sanyin jiki, tana cikin yi Driver'n gidan Hajiya Mama ya kawo breakfast, ta karɓa ta yi masa godiya ta kai dinning ta ajiye. Tana zaune har 10 tana jiran fitowar Adnan amma shiru ko motsinsa ba ta ji ba.



Wasa-wasa yau har Magriba ba ta ɗora Adnan a idonta ba, sauƙinta yau ma ta yi baƙi har sau biyu sun ɗebe mata kewa. Sai bayan Magriba ya shigo gidan, lokacin tana zaune a parlour ta kunna kallo, a ƙoƙarinta na son ya ɗebe mata kewa, sai dai damuwar dake cikin ranta ta hana ta gane me firlm ɗin ma ya ƙunsa.




Duk yanda yunwa da ƙishirwar son ganin shi suka cika mata zuciya amma sai ta kasa ɗaga ido ta kalle shi, ƙasa ta yi kanta tana sauraren yanda zuciyarta ke bugawa. Karon farko tun bayan da aka kawo ta, ta ji muryarsa ya yi mata sallama, sai dai ba a yanda ta so jin maganar tasa ta ji ba, ba cikin soyayya da kulawa ba. Fuskarsa a murtuke tamkar aka yiwa saƙon mutuwa, cikin isa da gadara kamar an masa dole ya ce. "Je ki ɗauko hijabinki." A hankali ta ɗago ta dube shi idanunta cike da ƙwalla, kafin ta kai ga yin magana ya juya ya shige ɗakinsa. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka ta miƙe ta je ta ɗauko hijabin ta saka, tana cikin kashe kayan kallon ya fito daga ɗakinsa ya yi hanyar waje ba tare da ya kalli inda take ba. Bin bayansa ta yi cikin sanyin jiki tana sharar hawaye.


Ganin ya shiga Motor ta buɗe front seat ta shiga, wai mugun kallo ya watsa mata tare da faɗin. "Kar ki bari na ƙara ganin wani abu mai kama da hawaye a fuskarki." Ba ta ce komai ba ta share hawayen tare da lumshe idonta. Gidan Hajiya Mama suka je. Abba da Hajiya Mama sun karɓe ta cikin fara'a da soyayya, sai nan-nan suke da ita. Ita kam kanta na ƙasa kunya duk ta ishe ta, idan an yi magana sai dai kawai ta murmusa. Adnan kuwa sai shagwaɓa yake musu wai yanzu sun daina son shi Abra suke so. Abun da ya ba wa Abra mamaki yanda ya dinga yi mata magana cikin kulawa da sakin fuska a gabansu Abba, hakan ya jefa ta cikin tunanin me Adnan yake nufi da ita?


A nan suka yi dinner tare da su Abba, tun tana jin kunyar su har ta ɗan ware, saboda su babu ruwansu, musamman Abba he is so friendly, yanata jan ta da hira. Sai ta ji dama Adnan ɗinta ne haka. Hajiya Mama ta lura da yanayin Abra kamar wani abu yana damun ta, idanuwanta ma sun nuna alamun ta yi kuka. Ba ta yi tunanin komai game da hakan ba, sai ta alaƙanta hakan da kewar gida take yi da kuma rashin sabo na mu'amalar Aure. Kafin su tafi Adnan ya sanar da su zai yi tafiya zuwa Abuja akan wani muhimmin aiki da ya taso masa, za su tafi tare da Abra. Addu'a fatan isa lafiya sukai musu. Sai wajen 10 suka dawo gida. Bai ko kalle ta ba bayan ya yi parking ya buɗe Motar ya fice. Bin bayansa ta yi kallo cikin wani irin yanayi na ƙuncin zuciya. Ajiyar zuciya ta sauke tare da buɗe Motar ta fita. Tun daga lokacin ba ta ƙara saka shi a idonta ba sai washegari bayan Sallar Asuba ya shigo ɗakinta.


Time ɗin tana karatun Alkur'ani, bayan ta kai ajiye ta rufe tare da gaishe shi cikin girmamawa. Bai amsa mata ba sai bin ta da wani wulaƙantaccen kallo da ya yi. Cikin ƙaunshin murya ya ce. "Zan yi tafiya yanzu, ba na zo kuma dan in sanar miki ba ne saboda ba ki kai wannan matsayin ba a gurina, na zo in ja miki warning ne akan ko da wasa kar wani ya ji labarin ba da ke na yi tafiyar ba, idan kunne ya ji jiki ya tsira." Ya ƙarashe maganar tare da jan tsaki. Cikin kukan da ya taho mata ta ce. "Dan Allah kar ka tafi ka bar ni, ni kaɗai, wallahi tsoro nake ji."


"Abun da kike jin tsoron ya kashe shi."
Ya faɗi haka tare da juyawa da niyyar ficewa."

"Please where is my phone, ka dawo mini da ita Dan Allah." Ta faɗa cikin matsanancin kuka.

Ko juyowa bai yi ba ya yi ficewarsa abunsa.


Kifa kanta ta yi akan cinyoyinta ta shiga rera kuka mai ban tausayi. Why Adnan? Me nake yi maka da ka zaɓi mu yi irin wannan rayuwar mai cike da ƙunci da damuwa? Ya Allah ka kawo mini ɗauki akan sabon babin ƙaddarata da ya buɗe, Allah ka sassauta mini. Abun da take faɗa a ranta kenan cikin tsantsar damuwa.



Yau kwana biyar da kai Abra gidanta, wadda waɗannan kwanakin suka kasance kwanaki mafi muni da tsaho a cikin rayuwarta. Gabaɗaya ta rame ta fita daga hayyacinta, ga babu waya balle ta kira su Abbi ko ta ji sauƙi a cikin ranta, ga kewar Salman da kullum ƙara yawaita take a cikin zuciyarta. Alkur'ani shi ya zamto abokin hirar ta akodayaushe, sai kuka da kullum sai ta yi shi ba adadi.


Misalin ƙarfe goma sha biyu na rana tana kwance a parlour akan carpet, idanunta a lumshe hawaye na zirara ta ƙasansu. Tana jin yanda cikinta yake ta ƙugin yunwa amma ta kasa tashi ta samar wa kanta abin da za ta ci, ga wani azababben ciwon kai da ya aure ta, kullum da shi take kwana take tashi. Kamar a mafarki ta ji an buɗe ƙofar parlour'n an shigo, ko ba a faɗa mata ta san Adnan ne ya dawo, saboda da zai tafi ya kulle ƙofar parlour'n ta waje, ta gane hakan ne a lokuta da dama da ta yi yunk'urin fita harabar gidan ko za ta ga abun da zai ɗebe mata kewa damuwar zuciyarta ta ragu. Ko matsawa ba ta yi ba da niyyar tarɓar shi, sanin da ta yi ko ta masa magana ba amsawa zai yi ba. Sai dai jin kamar ba shi kaɗai ya shigo ba ya sa ta buɗe idonta da sauri tare da goge hawayen fuskarta ta tashi zaune. Abun da ta yi tozali da shi ne ya sa numfashinta ɗaukewa na wucen gadi. Adnan ne tare da wata mace wadda kallo ɗaya za kai mata ka gane ƴar duniya ce ta ƙarshe, duba da yanayin shigar jikinta da uban bleaching ɗin da ta ci, ga kitson attachment a kanta gami da gashin ido maƙale a saman idanunta. Wannan duk ba shi ne abun da ya fi ɗagawa Abra hankali ba, jakar matar da Adnan ya riƙo a hannunsa da kallon da yake jifan ta da shi mai nuni da tsantsar soyayya, a ƙarshe kuma ya tsugunna yana cire mata hill shoe ɗin dake ƙafarta.





Littafin kuɗi ne,biya ₦300 via 0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank... Idan katin waya ne zaka Turo 500 shaidar biya 09047871750 or 08081012143.
[10/12, 7:18 PM] Abk: Mugun ganin da Abra ta yi, ya sanya ƙirjinta fara ɗa gawa zuciyarta tai mata nauyi. Rutse idanunta ta sakeyi tana ganin abin kamar almara, amma ta hana Zuciyarta gasgata abin da ta ke raya mata.

A hankali ta yi ƙasa da kanta ta shiga wasa da yatsun hannunta, jikinta duk rawa ya ke, ji ta ke kamar zuciyarta tai bindiga sbd fargaba. Juyawa Adnan ya yi tare da kallon budurwar ta ke tsaye a gefensa, cikin nutsuwa ya sakar mata wani kwantaccen Murmushi mai nakar da zuciyar ko wacce ƴar mace.
Fari ta yi masa da idanu tana girgiza ƙirji ganin hakan ya sanya Adnan, janye nasa idon ya lumshe kafin a hankali ya ce "My Surry" kashe murya wacce aka kira da Surry ta yi ta na shafa fuskar Adnan ta ce.

"Darling bee"
Hannunsa ya watsa yana ƙare mata kallo tare da ɗan matsawa kusa da ita he's trying to kiss her cheeks sai kuma ya ɗaga mata gira ya ce.
"Finally Bibina this is my house" "It's beautiful I like it but" hannunta ya kama ya ce "but what? Say it" rungomesa ta yi sosai ta ce "isn't ur house is our house okay" holding nata back yai ya ce "Oh! I almost frgt sbd ke ma na gina gidan".

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" sune kalaman da suka fita da ga cikin bakin Abra a wahale. Ta kasa fahimta, ta kuma kasa gane inda kalaman mijin nata ya dosa "My Surry? Bibina? Our house? What does that means?" Idanunta da suka sauya kala da ga farin da suke da shi zuwa launin jaa ta buɗe da ƙyar tare da zuba musu idanu.
Frm Head to toe ta ke kallon wacce aka kira da Surry, a ƙalla zasu iya age mate da Adnan idan ma zai girmeta sai da shekara ɗaya ko watanni, daurewa ta yi cikin sassauta muryarta tare da ɗauke damuwar da ke zuciyarta, but under her heart sunan Allah kawai ta ke kira, wasu har ƙwace mata suke.

Kusa da Adnan ta ja ta tsaya idanunta akan Fuskar sa, shi kuma yana kallon Surry. "Sannu da hanya" shirun da ta ji ne ya sanya ta ƙara cewa "Wlcm Bebbb" dry Surry ta yi kafin ta kalli Abra sai kuma ta kalli Adnan ta ce "Bebbb ana kira" haɗe fuska ya yi sosai ba tare da ya ce komai ba. "Is she your wife?" "Waa?" Da hannu ta nuna masa Abra ta ce "I think tana buƙatar ka"

"Kin taɓa ganin wuta da ruwa sun haɗu?" Surry ta ce "A'a never" juyawa ya yi gaba ɗaya wajan Abra a hankali ya ja idanunsa ya lumshe kafin ya buɗe a nuste ya kai kallonsa ga fararen yatsun hannun ta wanda suka sha henna sai ɗaukan idanu suke, dugun wuyan ta maƙale da wata siririyar necklace mai ɗauke da red ɗin stone.
Jajayen laɓɓan ta wanda suke rawa da karkarwa sbd tsananin tsoro da kuma abin da zai iya zuwa ya dawo.

"Idan har wuta da ruwa ba zasu haɗu ba, ta ya ya ki ke tunanin zan iya kiran maid ina nufin ƴar aikin gidan da matsayin mata? Maid ɗina ce"

"Dam!" Zuciyar Abra ta buga a hargitse kuma ta ke duban Adnan muryarta na rawa ta ce "Ni... Ni... ni ce ƴar aikin naka? ina matsayin matar ka mene maka wacece ita?" Ta ƙare maganar tana riƙe ƙirjinta sbd yadda ya ke ɗa ga mata tamkar zuciyarta zata tsaga ƙirjinta ta fito haka ta ke ji, bai ce mata komai ba sai kallon Surry da ya yi ya ce.

"Lemme take a shower" tana rangwaɗa tare da juya ƙugu wanda duk shan magani ya fara lalata su ta Ƙarasa wajan Adnan ta na kama hannunsa tare da kwantar da kanta a jikinsa ta ce.
"Can I help you?" "Sure Bibi" kama hannunta ya yi suka nufi part ɗin sa, sai da suka nisa Surry ta juya ta kalli Abra ta ce.
"Ki haɗa min Indomie with egg ta ji Attahiru"

Zubewa Abra ta yi tare da zaman ƴan buri a wajan kamar mahaukaciya haka ta fara kuka tare da kunce ɗaurin kanta tana hargitsa kanta, ko idanunta bata iya buɗewa sbd nauyin da Zuciyarta ta yi mata, a wahale ta riƙe ƙirjinta da hannu bibbiyu ta na ƙoƙarin hanasa ɗagawa, sbd ji ta ke tamkar ranta zai fita idan numfashinta ya shiga tare da ɗagawar ƙirjinta. Tun tana addu'a har ta kasa faɗin komai sai idanunta dake lumshewa bakinta na rawa a hankali ta sulale ƙasan carpet kamar sumammiyya.

Saukar ruwan mai tsananin sanyi a jikinta shi ne suka taimaka wajan farfaɗo da numfashinta wanda ya bar jikinta, kafin dawowa cikin hayyacinta taji saukar wani ruwan a jikinta wanda yafi na baya sanyi tamkar wanda ya ke ɗauke da ice sbd sanyi.
Jikinta na kyarma da ɓari ta buɗe idanunta a tsaye ta gansa da ga shi sai farar Armless da 3Qauter sai ƙamshin Pur oud, Kallon sa ta ke kafin ta ce.

"Ka dubi girman Allah ka faɗa min abin da nai maka, bana da kowa a nan kai kawai na sani mene yasa zaka juya min baya a lokacin da nake tsanin buƙatar ka? Ka ɗauke min dukkan wani farin ciki da jin daɗina ta hanyar nuna rashin kulawa a gareni, kada ka manta a ni amana ce a gareka,ka faɗa min abin da nai maka nayi maka Al'ƙawarin zan gyara kuma na baka hqr" ta faɗa tana sakin kuka tare da kallon sa ta na haɗe hannaye waje guda alamar roƙo.

Kallon tsaf ya yi mata kamar ba zai magana ba, sai kuma ya ce "Ina girkin da sweetheart ta ce ki mata? Ko kin mata aikin ki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login