Showing 207001 words to 210000 words out of 231718 words
Chapter 70 - Dare da Duhu Book Complete By Nimcyluv. Zeey Kumurya.txt
nasu tare da duban juna da sauri. Kasancewar ta mace mai fara'a sai ta sakar masa murmushi tare da faɗin. "I'm sorry." Cikin siririyar muryarta. Murmushin ya mayar mata tare da ɗaga mata hannu alamun babu komai, sannan ya bar gurin. Da kallo ta bi shi har ya ɓacewa ganin ta, ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da duba sarƙoƙin.
Tunda Rumaisa ta koma gida sai Bulama yay ta faɗo mata a rai, abin ya ba ta mamaki ba kaɗan ba, don duk da kallo ɗaya ta yi masa amma ta gane ba ƙabilarta ba ne, bai ma yi mata kala da fararen fata ba, ya fi mata kala da ƴan Africa, duk da fari ne tass shi ma. Bayan wasu kwanaki suka ƙara haɗuwa a hanya, a lokacin suna tare da ƙaninta Abdallah, amma duk da haka sai ta yi masa magana, abin mamaki shi ma ya gane ta, gaisawa suka yi cikin fara'a kamar waɗanda suka daɗe da sanin juna.
Watarana su Munnir sun je gurin da suke sayayyar kaya suka tarar kayan gurin duk an kwashe sai kaɗan, mai gurin ya ce su bari sai zuwa washegari za a jera wasu sai su zo su saya. Cikin rashin jin daɗi Munnir ya ce masa. "Ai kayan nan yau ake buƙatar su, saboda mahaifinmu yana ta kiran mu akan nasa sun kusa ƙarewa, kuma mun riga mun yi bucking Flight ɗin da zai tafi da kayan." Mai gurin ya ce musu babu damuwa, zai haɗa su da wata abokiyar kasuwancinsu, wadda Insha Allahu komai suke so za a su samu a gurinta. Ba su yi musu suka amince masa, bayan sun je suka tarar da fiye da abin da suka yi tsammani, don duk wani nauyi na Dubai gold akwai shi a shagon, kuma kayan gurin da sauƙi har ya fi na inda suke saya. Alokacin ba su haɗu da mai shagon ba sai yaranta, don ba ta zama ita a sati sau ɗaya take zuwa ta ga yadda abubuwa suke tafiya. Da za su ƙara sayan kaya sai suka koma gurin, saboda mahaifin Munnir ya yaba kayan sosai, ya ce idan za su ƙara saya su je can idan za a samu. A wannan zuwan Bulama suka ƙara haɗuwa da Rumaisa, ashe ita ce mai gurin. Ta yi mamakin ganin su sosai, shi ma haka. Tun daga ranar idan suka zo siyayya sometimes suna haɗuwa, har suka saba suka yi musayar contacts ɗin juna. Munnir ya dinga tsokanar Bulama yana cewa. "Ɗan fillo ko dai da ƴar Balarabiyar nan za a yi ne?" Idan ya faɗi haka sai ya yi murmurshi ya ce, babu ɗaya haɗuwar jini ce kawai.
Asalin Rumaisa Balarabiya ce Ƴar ƙasar Dubai, kyakkyawa ce don ko a cikin larabawan mai kyau ce, ita kaɗai iyayenta suka haifa, tun tana yar ƙarama mahaifinta ya rasu. Mahaifinta shahararren mai kuɗi ne, ya mutu ya bar dukiya mai ɗimbin yawa. Mahaifiyarta ta ƙara aure bayan rasuwar mahaifinta ta haifi Ɗa Namiji Abdallah.
Shaƙuwa mai ƙarfi ce ta shiga tsakanin Rumaisa da Yusuf Bulama, daga baya kuma ta rikiɗe ta koma soyayya. Tsakani da Allah Rumaisa take ƙaunar Yusuf, shi kuma yana son ta ne saboda tarin dukiyarta, amma ko kaɗan ba ya nuna mata hakan, don in ta ba shi abu ma ba ya karɓa sai ta nuna masa ɓacin ranta. Ƙauna da kulawa yake nuna mata sosai, wanda hakan yake ƙara dilmiyar da ita a cikin ƙaunar shi. Cikin haka aka janye strike ɗin da aka tafi na watanni goma sha uku, lokaci shekara guda cif da haɗuwar Rumaisa da Bulama. Ranar da za su dawo Nigeria ba ƙaramin tashin hankali da damuwa Rumaisa ta shiga ba, Yusuf ya dinga pretending as ya fita shiga damuwa, da ƙyar ya lallaɓa ta ɗan kwantar da hankalinta, a haka suka rabu zuciyoyinsu babu daɗi. Bayan Rumaisa ta gama cika shi da kayan arziƙi. Sun cigaba da soyayya kamar babu gobe ta waya, Rumaisa ta ɗauki dukkan yarda da k'auna ta damƙa wa Yusuf. Rumaisa macece mai kirki da addini da sanin ya kamata, matsalar ta ɗaya tana da zazzafan kishi, wanda wannan kamar a jinin larabawa yake. Tana mugun kishin Yusuf sosai, a kodayaushe cikin nanata masa kar ya ci amanarta take ko ya kula wata mace bayan ita, zuciyarta ba za ta ɗauki hakan ba, sannan ta yi masa alƙawarin tana nan tana jiran shi, ko shekara nawa zai yi kafin ya kammala karatunsa za ta jira har ya gama su yi aure. A tarayyar su ba ƙaramin kuɗi ta ba wa Bulama ba, duk da a zahiri yana nuna mata ba ya son ɗawainiyar da take shi amma ba ta fasawa. Lokaci ɗaya Bulama ya fara samun kuɗi, ya saya Mota da abubuwan more rayuwa. Inna ta san da zaman Rumaisa, amma ba ta san soyayya suke da Yusuf ba, a yadda ya faɗa mata abokiyar kasuwancinsu ce kawai suka saba da ita.
Bayan kammala karatunsu da N.Y. S.C Ta turo masa kuɗin jirgi ya tafi Dubai ya ɗora karatu, Rumaisa ce ta ɗauki nauyin karatun da gurin zamansa da abin da zai ci da komai na buƙatun rayuwa. A lokacin Rumaisa ta sanar da danginta Yusuf take so, wanda a karon farko suka ce ba su amince da wannan maganar ba, duk larabawa da ƴan'uwanta da suke son ta, ta rasa wa za ta ce za ta aura sai bak'ar fata ɗan Nigeria. Jin haka ya sa Rumaisa shiga cikin tashin hankali da damuwa, ta dinga koke-koke da roƙon su akan su amince, ita a haka take son Yusuf ko ma ɗan ina ne, amma suka ce ba ta isa ba, tun wuri ma ta rabu da Yusuf kafin su saka a ɗaure shi. Mahaifiyarta ce kawai ta goyi bayanta a lokacin, duk da ita ma ba ta so, amma tausayin 'yarta da ƙaunar ta ya sa take supporting ɗinta. An yi badaƙala da ja'inja ba kaɗan ba tsakanin dangin mahaifin Rumaisa da mahaifiyarta kafin su amince ta auri Bulama, amma sun ce babu ruwansu duk abin da ya biyo baya mara daɗi kar ta neme su. Ba a yi Auren ba sai da dangin mahaifiyarta suka zo Nigeria suka ga asalin Bulama, shi kuma ya yi cike-ciken takardu na yarjejeniya a Dubai ɗin. Al'amarin ya ba wa kowa mamaki a Adamawa, musamman Inna da Murja, Yusuf da auren Balarabiya, abun kamar almara.
Buri ya cika bayan fitar da rai da hakan, farincikin da Bulama da Rumaisa suka yi a lokacin Aurensu ba zai misaltu ba. Musamman shi da ya jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, yana son Rumaisa sannan kuma ya san dukiyarta yanzu za ta koma tasa da ta ƴaƴan da za su haifa. Soyayyar da Bulama ya nuna mata a zaman Aurensu ya sa ta ƙara yarda da shi da ƙaunar shi. Bayan ya kammala karatunsa ya shirya don komawa Nigeria, a nan mahaifiyar Rumaisa ta ce ba zai tafi da ita ba, ba za ta yarda yarta ta yi nesa da ita ba. Shi ma ya ce ba zai fasa komawa Nigeria ba, saboda Mahaifiyarsa da ƙanwarsa shi kaɗai suke da shi, suna buƙatar shi a kusa da su. Ba don Rumaisa taso ba ta bar shi ya tafi. Dawowar shi ba jimawa ya fara aiki a wani babban asibiti a nan Adamawa. Bayan wasu watanni ya koma ya ga Rumaisa, a lokacin ta raba dukiyarta biyu ta ba shi rabi, ta ce ya je ya yi duk kasuwancin da yake so a Nigeria ya juya kuɗin. Kusan haukacewa Bulama ya yi saboda tsabar murna da farinciki, ranar ƙaunar da ya nunawa Rumaisa bai taɓa nuna mata kamar ta ba. Bai jima ba ya ƙara dawowa Nigeria, anan ya yi deciding ya buɗe Babban Asibiti nasa na kansa. Bai buɗe a Adamawa ba saboda wani dalili nasa ya buɗe a Kaduna, ya saka masa sunan mahaifinsa GARBA YUSUF BULAMA. A lokacin ya haɗu da Saudat suka fara soyayya. Saudat irin matan nan masu feleƙe da iyayi da son sabgar ƙarya. Farkon haɗuwar su da bulama ba ta zata yana da mata ba sai da ya faɗa mata. Ta ji takaici da baƙincikin fara mallakar wata da ya yi kafin ita, amma haka ta daure suka cigaba da soyayyar su. Sai dai cikin ranta ƙiyayyar Rumaisa ce fal duk da ba ta taɓa ganin ta ba sai dai a hoto. Abin da yake ƙara ƙona mata rai yadda Bulama ya ɓoye wa Rumaisa tarayyar su, ya nuna ba ya son ta sani. Kammala ginin G.Y HOSPITAL AND MATERNITY Ya yi daidai da lokacin bikin SAUDAT da BULAMA, don haka aka sha shagali ba na wasa ba. Auren ya kasance tamkar na cin amana, tunda ba da sanin Rumaisa aka yi ba kuma da dukiyarta. Bayan bikin da wata biyu Bulama ya koma Dubai, a wannan zuwan Rumaisa ta samu ciki, bai jima ba ya dawo Nigeria saboda yana son ya kula da Hospital ɗinsa, sai dai bai sanarwa da Rumaisa ya buɗe asibitin ba.
Watan cikin Rumaisa takwas ta kira Bulama ta ce za ta zo Nigeria ta gaishe da Inna ta zazzaga danginsa su san ta, ta san su. Bulama bai so hakan ba saboda gudun tonuwar asirin Auren Saudat, amma bai nuna mata ba saboda kar ta yi tunanin wani abu, dama tana ta complain akan yana daɗewa yanzu kafin ya je ya gan ta.
Bayan sun gama wayar ya fara haɗa kayansa, cikin mamaki Saudat da ta shigo ɗakin da yake ta ce masa. "Lafiya kake haɗa kaya da sakaliyar yammar nan Doctor?"
"Adamawa zan je."
Ya ba ta amsa a tak'aice
"Adamawa kuma? Shi ne ba ka sanar mini na fara haɗa kaya ba ni ma?"
Yana zuge zip ɗin trolley ɗinsa ya ce. "Ba da ke zan tafi ba, Rumaisa ce za ta sauka a ƙasar nan gobe, kin kuma san ba ta san da zamana a Kaduna ba balle aurenki da na yi, don haka dole ya zamana a Adamawa za ta same ni." Cikin takaici ta ce. "Sai yaushe kuma za ka dawo?"
"Sai ranar da ta tafi."
"Asibitinka kuma fa."
"Akwai masu kula shi kamar ina nan ai."
"To amma ni haka zan ta zama ni kaɗai, kana ƙasar ma amma ba za mu haɗu ba har sai ranar da ta tafi?"
Cikin fusata ya ce. "Haba Saudat ya kike so in yi ne? Ke duk watanni da nake yi a gurinki ban je wajenta ba, ba kya gani? Sai yau ɗaya za ki ɗaga mini hankali. Rumaisa tana buƙatar kulawata a halin yanzu sosai fiye da ke, saboda tana ɗauke da juna biyu, don haka ko da ba za ta zo ba ni zan je. And lastly kar ki kuskura ki kira ni ko ki mini text, ni zan na kiran ki da kaina, sai na dawo, zan miki transfer ɗin kuɗi idan na ƙarasa." Ya ƙarashe maganar tare miƙewa ya fita.
Da wani irin kallo ta bi shi cikin bugawar zuciya da tsananin tashin hankali har ya fice. Gwauron numfashi ta sauke tare da furta "Ciki?" Tana gyaɗa kai, lokaci ɗaya ta miƙe kamar wadda aka tsikara ta shiga kaiwa da komowa a cikin ɗakin.
Littafin kuɗi ne, ku biya kafin ku karanta. 09047871750
[11/25, 10:36 AM] Abk: Maganar samun cikin Rumaisa ya ɗagawa Saudat hankali, zuciyarta ta fara saƙawa kwakwalwarta mugun tunani. Ta ɓangaren Rumaisa ta samu iyayen Dr lafiya cikin karamci da walwala hakan yasa ta saki jiki har ta ce zatai wasu kwanaki. Tana saura kwana uku tafiyarta naƙuda ta kamata cikin gaggawa suka nufi asibiti tasha baƙar wahala ƙwarai har an fara tunanin za ai mata C.s sai Ubangiji ya sauke ta lafiya ta haifi twins.
Murna ta kama Dr G.Y sai dai murna ta koma ciki domin awanni wajan biyu da haihuwar aka dawo da jariran a hannu Allah ya yi musu rasuwa, daman da aka haife su ba wanda yaga kalar su sai da suka rasu. Haka akai musu suttura ba tare da mahaifiyar su ta gansu ba. Lokacin da Rumaisa ta samu labari kusan hauka ta kusa yi uwa uba akace ba zata sake haihuwa ba Wannan dalilin ya sanya ta saka damuwa a ranta ƙwarai da gaske.
Bayan sati biyu ta tattara ta koma Dubai hakan ya yi wa Bulama daɗi ya ƙara samun damar da zai zauna da Saudat, a lokacin ne kuma labarin rasuwar P.A ɗin Rumaisa ya riskesu ya yi hatsari ya rasu da shi da motar gaba ɗaya suka ƙone ƙurmus.
Bulama ya sanya wa ransa samun dukiyar Rumaisa ko ta halin yaya ne ta zama mallakinsa. Lokacin guda ya shiga amsar kuɗi wajanta da niyyar zai buɗe wasu, kamfanoni wani lokacin yace kuɗin sun gaza wani lokacin ya ce za a ƙaro kaya, wani lokacin ya ce ta bashi rance. Yarda da amincin da tai masa sai ta kalle shi tare da yin murmushi ta ce "Wanne irin rance ya kai Yusuf dukiyata taka ce dani da duk abin dana mallaka naka ne" idan Rumaisa ta faɗi haka sai Dr Bulama ya rungume ta tsam a jikinsa tare da maganganun masu daɗi.
Ganin abubuwa sun fara runcaɓewa Rumaisa ga P.A ɗinta ya rasu ya sanya ta ɗakko Abdullah ƙaninta ta dawo da shi wajanta, tare da ragama wasu gefe na dukiyoyinta yana kulawa dasu ta bashi matsayin sabon P.A
Daga nan ganin Dr Bulama ya ƙara yiwa Rumaisa wahala a cewar shi aiki ne ya yi masa yawa sosai, lokacin kuma tuni Saudat ta samu cikin Meenal farin ciki wajan Bulama ba a magana, ya tattara ya manta da batun ya taɓa haihuwar yara bai kuma damu da rashin haihuwar Rumaisa ba.
Da Meenal ta girma ya ƙara himma wajan kwashe dukiyar Rumaisa lokacin Abdullah ya tsaya tsayin daka akan kuɗin da ƙyar suke fita, sbd a kaso goma na dukiyar Rumaisa bai fi kaso huɗu ya rage mata ba. Babban dalilin daya sanya Rumaisa shiga tashin hankalin har ta saka aka rufe sabon companyn data buɗe. Wannan kenan.
Waje ya yi shiru cikin kuka Rumaisa ta ce "Wace kuma Meenal daga ina aka sameta shin itama yarinya ta ce?" Dr Bulama ya kasa cewa komai zufa na yanko masa sosai. A hankali Adnan ya sauke numfashi yana ƙara rungume Little a jikinsa ya ce.
"Ƴar ce wacce matar shi ta haifa masa"
"Ƴa tare da wata matar Yusuf? Da gaske ne abin da ake faɗa Ya kai Yusuf kada kayi mini ƙarya na amince da kai"
Gaba ɗaya mutanan parlourn suka zuba wa Ummi idanu cike da tausayawa ya aka ƙare da kishiyar daka sani ma balle wacce akai a bayan idanun ka, uwa uba auren cin amana anyi mata kishiya da kuɗin ta.
Cikin gunjin kuka sosai Ummi ta ce "Yusuf ka cuce ni kaci amanata, kaci amanar yarda da amincin da nayi maka na tsayin shekara da shekaru, kayi aure da dukiyata without knowing everyone Wallahi Wallahi Allah.....,"
Da sauri Abba ya ce "A'a Hajiya Rumaisa kada ayi haka, kiyi haƙuri don Allah ai ba a tabbatar auren ya yi ba" ya juya kan Adnan yana nuna shi da hannu ya ce.
"Kai kuma kada na sake jin bakinka manya na magana"
"I'm sorry Abba"
Abba ya watsa masa harara ya ce "sorry for yourself Adnan Aliyu Matawalle" Adnan yai shiru.
Abbi ya sauke numfashi yana mamakin rayuwa yadda bata da tabbas ɗin nan cikin nutsuwa ya ce.
"Yanzu Dr da gaske dai kana da wata mata bayan Rumaisa?" kan Dr a ƙasa ya ce. "Gaskiya ne ina da mata Saudat na aureta ba tare da sanin Rumaisa ba, amma ita Saudat ta san da zaman Rumaisa ina da yarinyar Meenal ita ce wacce nake cewa wani ma'aikacina bashi da lafiya"
Ya juya gaba ɗaya zai magana Ummi ta girgiza kai tana ɗaga masa hannu alamar bata buƙatar jin komai. "Ina yarinyar tawa? Kuyi haƙuri na kasa jurewa"
Murmushi kawai Abbi ya yi ya shiga faɗin "Daughter, Afra... Come here your parents are here" da gudu Afra ta fito daga cikin ɗaki kamar me jira. Tana fitowa Ummi ta miƙe tsaye hawaye na zuba daga cikin idanunta ta warewa Afra hannu muryar ta na rawa ta ce.
"Masha Allah, Allahamdulillah ta'al ya ɗiyata" Ummi ta faɗa a bayyane farin ciki ya sanya Afra kasa motsa wa ta durƙushe a wajan ta shiga rusa kuka da dukkan ƙarfinta. Ummi da kanta ta kama Afra ta rungome itama hawayen take sosai. Bulama ya kasa koda motsi sbd matsanancin kunya da kuma tsoron matakin da Ummi zata ɗauka. Shi kansa kallon Afra yake yana ji tamkar ya rungume ta.
Murmushin fuskar Abdullah ya kasa ɓoyewa kusan yafi kowa jin daɗi a yadda fuskarsa ta nuna, at least Yayar tasa zata samu nutsuwar zuciya.
Bayan komai ya lafa Abbi ya kalli Afra ya ce "Daughter inama kika ce an tsinceki" tana jikin Ummi muryar ta har lokacin rawa take ta ce
"Baba ya ce wai ko wata rana yaje daji neman wani magani aka fara harbe harbe ya labe wani waje ya daɗe a wajan kafin ya fito daga inda ya ɓoye, yana fitowa idanunsa ya sauka akan wani mafarauci wanda yake kwance anyi masa harbi wajan huɗu, daga gefen shi kuma yaga wata jaririya kwance tana kuka, hakan yasa ya ɗauki Jaririyar taho hanyar gida shi ne yaje wajan ƴan sanda amma ya ɓoye labarin kisan yace kawai tsinta ta ya yi"
Adnan ya kalleta domin ba haka ta faɗa masa ba, kamar mai karantar zuciyarsa ta ce "Wannan shi ne gaskiyar maganar Baba ya ce na ɓoye duk wanda ya tambaya na dinga faɗar abin da ya faɗa mini, sai na samu iyaye na gsky zan faɗi gaskiyar Abin"
Cike da gamsuwa Abbi ya jinjina kai ya ce.
"Babu mal wanda suke kashe mafaraucin nan sune kidnappers ɗin da muka kama cikin daji a can muka samu Abra, har wani yace mini wancan tasu ce kada na taɓa ta babu ko shakka a wajansu ta rayuwa tsayin shekaru uku har ta samu matsalar kunne, Allah mai iko Al-hakkumu bowayi gagara misali Allah mai yin Yadda ya su, ina ganin matsalar mu ta zo kusan ƙarshe"
"Gaskiya kam abin da yake ɓoye ya fito, saura nemawa Salmanun-faris auren Afra yanzu a gaban iyayenta" Abbi ya yi saurin cewa.
"A'a ba za a yi haka ba, ina da