Showing 303001 words to 306000 words out of 373688 words
Chapter 102 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
ina ruwana da bukatan shi may ya rageni dashi na rayuwa da zance zan hanashi nashi kalar rayuwan.
Har barci ya dauke shi bai gama tunanen abinda ya dace ya aiwatar a kaina ba hakanan.
Washe gari ma kafin ya dawo motsa jiki har na bar gidan ko na fita yai mamakin hakan shi da kan shi ya nemawa kan shi abin karyawan da zaici.
Da wuri na dawo nai girki na aje mai saman table nashige ciki abina ban kara fitowa ba.
Yana shigowa a lokacin idon shi akan table yaga abinci a gurin yakai kallon shi ga kofana yana saye yasan dai ina ciki a lokacin tunda babu inda nake zuwa.
Dakin shi ya shiga yai sa,a yau ma na gyara dakin bakamar jiya ba da na hau sosai.
Murmushi yayi kawai ya shiga wanka a lokacin yafito yasaka kayan shan iska don zafi akeyi sosai lokacin.
Dakina ya nufa don ganin har lokacin ban fito falo ba ina dakina a kwance nake kasa saman ties idanuwa na a rufe ina bin kira,an dake tashi a wayana a hankali.
Ya dan dade tsaye sai jin nauyin mutum ya shigo dakin danayi yasa ni bude idanuwa na da suke min a rufe.
Yana tsaye a kaina ya saka hanayen shi a cikin aljihun wandon shi tare da kura min idanuwan shi.
Ganin shi tsaye a kaina bai sa na bude idanuwan nawa ba sai kara lumshesu danayi kawai.
Dan tsugunowa yayi tare da rage tsawon shi ya tabo kaina da sauri na bude idona na watsa mai wani irin kallon tsana da ban masan lokacin da nai mashi shi ba.
Yace ki taso muci abinci nace akoshe nake ya mike tsaye yana cewa to sai kizo ki zuba min ai.
Nace ai banice mai zuba maka kwayan ka ba idan zaka sha don haka sai kaje mai baka kayan mayen ka ta baka amma bani Fatima ba.
Da mamaki ya kalleni yace ke kada ki soma kice zakiyi min rashin kunya wallahi.
Nace da ke nan da nake daukan ka a mutum ba yanzun da ka zube min ba.
Ke ni kike fadawa haka watau kin raina ni ko don kin ga kamar ke kin isa ko may wai.
Nace aini ban isa ba kuma ba kowa nake ba don haka kowa tashi tafishe shi kawai.
Kaman zai yi magana sai kuma ya juya yafita daga dakin ran shi a bace yana ci yana kallon kofa na ko zan fito daga dakin amma shiru har ya gama babu alamana a falon.
Gaba daya taji gidan ba dadi ban fito ba sai ma da naga tara da rabi na dare kawai na kulle kofana na kwanta kawai.
Goma da rabi ya kashe kayan kallon da komai na falon ya shiga daki sai da yasa kayan barcin shi har ya kwanta ya mike zuwa dakina ya murda a rufe kofan yake a lokacin haka ya juya ya koma don yasan bazan bude ba.
Bai taba tsanmanin cewa akwai shakuwa haka a tsakanin mu ba kuma ba zai iya daure rashi na ba a yanzu sai da yaga yai rabin kwana yana lalaban gefen da nake kwantawa bai jini ba.
Nima a nawa bangaren kusan hakane na kwana da kewan shi duk da haushin shi da nake matukar ji a lokacin.
Kowan mu da tunanen dan uwan shi ya kwana a ran shi cikin damuwa muke .
Tun da safe ina kitchen ina hada abinci yazo bakin kitchen din nai matukar mamaki da bai fita motsa jikin shi ba yau.
Kamar ban san yana gurin ba na share shi ya tako har zuwa cikin kitchen din inda nake tsaye ina motsa dankalin dake saman gas.
Ganin da yayi bazan mai magana ba yasa shi cewa kin tashi lafiya ?
Nabashi amsa da lafiya kawai.
May yasa kike rufe min kofan ki kwanan newai Fatima ?
Dagowa nayi muka hada ido kawai sai na kawar da kaina naci gaba da abinda nake yi ina tunanen watau bai masan abinda yayi ba ke nan koko tsaban rainin wayyo ne hakan ?
Ke nake tambaya ya maimata min .
Kaina na girgiza mai nace ina kwashe dankalina a tunkuya a hankali.
Nace ban da amfanin komai a gare ka don shaye shayen ka yafini daraja a gare ka nagani.
Don haka kaje kayi abinka kabarni na yarda na zama ma yar aiki kawai a gida don shine ya dace dani.
Murmushi yayi ganin zan wuce ya dan ja dabaya ya bani hanya yana fadin wanan kuma maganar kice amma ni shana baida alaka da kusantar ki a gare ni.
A ganin ka ba amma ni bazan taba mu,amula da mutumin dake a cikin sabon Allah insha Allahu.
Ido ya zuba min don jin abinda nace ya fahinci a shirye nake na zuba mai bakaken maganganun dake a bakina a lokacin.
Shiru yayi ya dan dade tsaye a gurin yana kallon yadda nake aikina a cikin tsabta da gwanewa sai ya juya kawai yabar kitchen din zuwa falo ya zauna cikin damuwa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
A LOKACIN MU KE,,,,
Gaba daya na daina kwaliya a gidan na daina fitowa falo yadda na saba na zauna a tare dashi, gashi wasa wasa mun fi sati daya haka sai zaman yar tsama mukeyi a tsakanin mu.
Shi kan shi har bashar ya fanhici yana da yar matsala a tare dashi sai dai bai san daga ina matsalar take mai ba.
Tunda zurfin ciki irin nashi bai bari ya fadawa kowa halin da yake ciki balle a bashi shawaran da ya dace dashi.
Zaune suke ga system ya aje a gaban shi amma ya kasa sauraren bayanin da bashar yake mashi a lokacin.
Shiru bashar yayi yana kallon shi can yake cewa wai may ke faruwa ne sadauki naga fa duk kwanan kana cikin dan damuwa.
Guntun tsuki yaja yace may ga nine wai lafiya kalau nake bashar ya hade hannayen shi biyu guri guda ya tagumi dasu ta kasan gemun shi yana kallon abokin nashi na tsawon dan lokaci.
Can yace tabbas akwai matsala a tare da dakai wanda nake gani kamar daga gida ne ko gurin kaunata Fatima?
Nace maka babu komai murmushi bashar yayi yace wallahi akwai komai kan don ni nagani kafada min may ye matsala please ?
Don nima shawarana da matsala bata wuce ka akan may kai zaka dinga boye min damuwan ka wanda a gaskiya banjin dadin hakan wallahi ko.
Kallon bashar yayi yasan abinda yafadi gaskitane har cikin ran shi ya dan ja tsuki ya mike tsaye tare da saka hannin shi a cikin aljihun shi ya nisa gurin window office din ya nufa yana kallon waje can ya nisa kadan ya juyo inda bashar yake zaune yace.
Bashar wallahi Fatima tana son jefani a cikin wani hali saboda dan dalilin ta mara amfani.
Ai tasan yadda nake ta amince ta aure ni amma kuma may zai sa yanzun sai da na yarda da ita zata bijiro min da,wasu akida nata na daban can.
Bashar ya ce tare da mikewa ya dan tako zuwa inda sadauki yake a tsaye yace ban fahinci tasan halinka ba ta yarda ta aure ka haka nan ?
Yace kai tsaye kwarai eh ai tasan koni waye tasan ina sha aiko ?
Bashar ya rintse idanuwan shi don takaici yace haba haba man kaida bakin ka har kake ikirari da sabon Allah haka why why please.
Lokaci yayi fa da zakaiwa kan fada kafin ai maka yau tun kuna kubiyu kaida Fatima inaga sai yaran sunzo an fara masu gori a makaranta akan shan ka.
Idon shi ya rutse yace kaga abinda yasa ban sha,awan auren ba hausa tun farko amma maji tanace akan wanan yarinyar sai nayi.
Ita Fatima har ta isa ta hanani abinda nakeyi ko nai niyar yi kamar ta who is she bad way ?
Itace ko wani abu don gashi saboda ita ka shiga bakon yanayi kana gani Fatima ba wata haske bace a rayuwan ka halan.
Ya dago ya kalli bashar ido da ido yace haske haske fa kace yace to haske may Fatima take a gare ni kuma?
Bashar yai yar dariya tare da dan buga kafadan sadauki yace ko wani irin haske nw a yanzu kafi ni sani wallahi.
Halan ka shawo har ta fahinta da hakan ko yace wai shine takewa fushi kwata kwata yanzu ta daina kulani har yar kwaliyan nan ma ta daina yin shi kullun tana daki a kumshe tana hadiyan bakin ciki.
Bashar yace da sauri kagani kagani zaka kashe yar mutane saboda mugun halin ka ko ?
Yace oh nima ma zan kasheta ba itace zata kashe ni ba ita da takasa bani hakkina dake a kanta.
Wallahi ta shiga hankalin ta don tasan idan yau nace zan cika uku a gida na zan iya wake da hasara ba ita ba.
Dariya bashar yayi yace wallahi da watan kunyan ka ya kama a garin nan don kafin ma ka gama zagaye dakin su ka dawo gareta gari yasan ko kaiwaye ko ?
Jeka auro mata uku yau kagani waye a matsa in ba kai ba zata kwabe mawa.
Kana zaune kalau da matar ka kai mata abinda bata so ta dauki mataki maimakon ka bata hakkuri ka lalashi abinka tunda kaine baka da gaskiya amma wao kai shine har kake neman hanyan kuntata mata Allah ya baka sa an auro mata ka tara a gida tinda kana da kudin hakan .
Wallahi batin fada maka mata da kake gani suna da nasu ranan idan kace bazaka bari ba itama rana da hanyan rama cutar ta akan ka sai ka shiga hankalin ka.
Fatima dai ce ba yadda zakayi da ita don tai maka zara a zuciya kuma muddin bakane me shiri ba har mama taji naka ya samay ka kuma ji zarayi tunda inta gidana ta samu labarin halin da kuke ciki.
Dariya yayi yace ashe kaima kasan maryan magulmaciya ce ke na kyashan ta manne da sarki.
Yace to dakata don kawai tana gyara shine zakai mata mugun lakanin suna kawai wallahi yanzu zamu saba dakai akan maryam.
Kallon bashar yake yana dariya yace kai dai ka fadi da bakin ka bashar yace ai mantawa nayi a gaban makiyin mu nake.
Yace wallahi kaje kasan yadda zaka rarashi fatima ku fahinci juna idan ma kana fasa wanan shan yafi maka alheri don ko wata mace bazata ji dadin ace mijin ta ko dan ta yana sha ba ga mata da gorin tsiya wallahi.
Sun dauki lokaci suna musayan magana kan zancen karshe bashar yai mashi sallama akan zai tafi gidan Inna ya gaida ita bai samu zuwa da safe ba.
****** ********* ******
Yashigo gida fuskan shi a sake ya samay ta zaune a falo ta kunna tv sai kida da rawa na yan iska ake a wani tasha na kasar ghana.
Zama yayi a gaji saman kujera ta watso mashi harara tace kasamo kudin ne da ka dawo min gida haka?
Kallon mamaki yai mata yace cikin karfin hali wai Jamila may yasa baki son a zauna lafiya ne ke ?
Tace lafiya kudi kaima kasan idan ba kudi ni ba zaman lafiya gare ni don dasu nasaba.
Kasan wallahi inda ba kudi kai Ahmed baka isa ka aure ni ba don kasan da wa yanda nake hurda a baya.
Murmushi yayi yace Jamila ke dai in ba kudi sam babu zaman lafiya dake ni yanzu fa ban son abinda ya taba min rayuwan yar matata don ashirye nake akan duk bukatanki ko ina zan shiga na samo maki don kiji dadi kawai.
Hararan shi tayi tace in kana son kaji dadi na mike min su kawai inji dumus sai kaji dadin nawa.
Hannu ya tura a cikin aljihun shi yana fadin angama inda za a bar ni yau na shafi wanan body da ake min kwalelen ka dashi kwana biyu.
Kudi ya mika mata da sauri ta fisgi kudin tare da sake wani murmushi tace dama nasan kana dasu ai boyewa kawai kayi don kaji may zanyi.
Ajiyan zuciya ya sauke a ranshi yace don baki san zubar da kaina danayi na samo su bane don kwadayin ki da masifan ki kawai.
Yana matukar son jamila a ranshi do ba laifi yarinyar ta iya gado sosai gurin ma irin hakane suka hadu da ita har yaji ya kamata ya aure ta kawai yanuna mata karya ya auro ta din duk da mama asiya taso kawo cikas ga maganan amma yai sa,a ba ya yarda akayi abin.
Ranan kan yasan ya kawo kudi don tun wurin suka fara harkan ma,aurata a tsakanin su duk bashin da ke kan su na kewan junan su sai da suka biyawa kansu.
Don jamila irin matan da basu iya kwana biyu ba tare da namiji bane ya kusance ta.
Tun a gaban shi bayan sun huta tafara kashe kudin gurin sayen banza da wofi yana kallo ba yadda zai yi don son da yake mata.
Ranan da dare ma tare suka fita yawo da ita ya kara kashe mata dan canjin dake hannun shi kuma.
****** ********* ******
Ina zaune a dakina kayana da aka wanke nake kokarin nikewa a lokacin don najera su a wardrobe dina.
Dakin ya shigo saye yake cikin kayan barcin shi sau daya na daga kaina na kalleshi na kawar da kaina tare da ci gaba da abinda nakeyi a lokacin
Karaso yayi bakin gadon da nake zaune yai tsaye akaina tare da kura min idon shi na wani dan lokaci.
Can naji muryan shi yana cewa kina ganin kamar wanan abin da kika zaba zai fishe mune Fatima.
Banyi magana ba illa mikewan da nayi tsaye na kwashi kayana zuwa cikin wardrobe dina dasu.
Ina ajewa na juyo ban san yana tsaye a bayana ba sai ji nayi ya rike ni kawai na dago idanuwa na da sukai ja don bacin rai nace may ye haka malam.
Oh tambaya ma kikeyi don na taba mata ta ko may ?
Zan wuce daga gefen shi sai naji ya kamoni yace ina zaki sai kin fada min may ye wai matsalar ki ne a gidan nan.
Nace cikin kukan da ya kubce min kai yaya kai kaiyaya sadauki kaine matsalata yaya.
Murmushi yayi ya jawo ni zuwa jikin shi duk kubce kubcen danakeyi sai saman gado na ya dire ne.
Nan ya shiga kokarin cire min kayan dake jikina har yai nasara rabani dakayana.
Nan ya shiga sarafani yadda yake so raina yai matukar baci tankar da dutse yake amfani a lokacin .
Har yagama abinda zaiyi ya koma gefe daya yana mayar da nufashi a hankali.
Kuka nake sosai don abinda ya aiwatar min a yanzu yai matukar bata min rai.
Nace cikin kuka abin yakai kuma har da fyede ka koma yi min kasani wallahi idan ka zalunce ni sai Allah ya isar min.
Dagowa yayi da mamaki don bai taba jin makamancin wanan kalman ba a gare shi yace.
Fatima nikike jawa Allah ya isa don na taba ki kawai ko may ?
Nace bayan na dan daga ina kallon shi da idanuwa da sukai ja nace kai bakaji kunyan tabani ba kana cikin rashin tsarki?
Nine banda tsarki Fatima nace ina kaga tsarki mutumin da ya mayar da sabon Allah abin yin shi.
Mutumin da bai tsoron haduwan shi da Allah cikin ko wani irin halin zai riske shi ko a maye ko a kalau.
Mutumin da baida mu da halinda na tare dashi suke ciki ba akan mugun halinda yasa wa kan shi don son zuciya.
Ni wallahi yanzun ko da ake cewa wai yimaka akayi kake halin nan ban yarda ba har da hali ma.
Ka cuce ni wallahi daka kusance ni a cikin rashin tsarkin zuciyan ka wama yasani ko ka shawo ne kazo min a haka tunda ba imani ke gare ku ba.
Idan kace wanan halin baza ka daina ba nima wallahi bazan iya zama da mashayi ba tubur na haifi diya ana masu gori na fita gidan buki ana zunde na nashiga mutane ana nunani.
Kuma wallahi,,,,
Ke ya ishe ki hakana nagaji da jin mugun kalamin ki a kaina haka na ko don kinga na damu dake ne zaki tsaya kina fada min magana son ranki.
Damuwa damuwa fakace yaya da kadamu dani dabakai haka ba wallahi dakaso abinda nake so maka a ranka.
Ni dana damu dakai aina fahinci abinda kake so da wanda baka so kuma na kiyayye su don azauna lafiya.
Yadda kake ganin an tursasa maka aurena wallahi nima haka aka tursasa min auren ka badon ina so ba.
Amma nai hakkuri na zauna ina maka addua a kullun na Allah ya shiryaka kamar yadda mahaifan ka suke maka a kullun.
Amma kassh kai yaya baka sawa ranka daina wanan halin mayen ba kaduba fa yadda kainan ka Nafisa maye ya mayar da rayuwan ta.
Idan badon Allah ya nufa mamatana tsaye da addua ba akan ka da yanzun ka fita lalacewa a hakan.
Nikan gaskiya ba zan zauna da dan maye ba don idan akwai abinda na tsana shine maye a rayuwana amma kuma ina kaddara ta riga fata yau gani