Showing 81001 words to 84000 words out of 373688 words
Chapter 28 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,,
A LOKACIN MU KE,,,,,
MAJI ce kwance a,saman dogon kujeran dake cikin falon dakin ta, ziciyar ta a cacushe yake mata da bakin da bacin rai ga radadi da zugin da yake mata.
Bakomai ke damun zuciyar Maji ba sai irin halin rayuwan da Allah ya jarabi dan ta dashi.
Wanda a da can baya ba haka rayuwan shi take ba sai yanzu da girma ya fara shigan shi ne bakon al,amarin ya fara shigan shi haka.
Hayaniyar da take ji yana tashi daga cikin gida yasa ta sauri mikewa zaune da sauri, don ta saurara idan dai ba saudakine ya ja mata wani sabin maganan ba kuma a gidan.
Aikuwa jitayi mama tana fada tana cewa wanan yaro ya dai zama muna masifa a gidan nan yanzu.
Yaro guda ya zama alkakai acikin yan uwa wai mai saudauki ke son mayar da mutane ne haka wai, duk yaro abu ba abu ba ya kai mai duka bugu haka har na tsiya.
Sai muryan dayar kushiyarta da take biwa tana cewa ni wallahi karan shi zanyi akan takalman banza zakaiwa yaro mugun duka haka har ka fasa mai baki.
Anty watau amaryan su tace a,a kada ki karan shi kijira har shi mahaifin nashi da ya bata shi ya dawo ki fada mai muji ko muga abinda zai yi,
Basu suja batashi ba da so sun dauki son duniya sun dora akan shi yanzu ai ga abinda so ya jawo masu sun gani.
Maji dake daga daki takai zaune a hankali saman kujeran da ta tashi a kanshi tana maijin zafin maganganun su a ranta don dai ita tasan a iya yinta ba wani gatan da ta gwadawa dan ta, a baya fiye da sauran yan uwan shi.
Amma babu yadda zatayi don ance dan kuka mai jawa uwar shi jifa don da bai shiga harkan yaran su kamar yadda ta hore shi da zafin zuciyar shi akan ya rage da bai ja mata yawan magana na habaici ba ga kishiyoyin ta.
Wasu irin hawaye ne masu dumi suka fito daga idanuwan ta a hankali, a daidai lokacin Amira dake cikin daki kwance tafito falon nasu.
Ganin yanayin uwar,su yasata karasawa kusa da ita ta zauna tanavmai kura mata ido tace yaya sadauki ne ko maji.
Don Allah maji ki fita zancen su ki daina zubar mashi da hawaye malamin mu fa na islamiya yace muna ba kyau uwa tai kuka akan dan ta musan ma ma da namiji don Aljannar shi yana ga hannun ki mama don Allah ki yi hakkuri ai ya kamata ace kin saba da halin shi yanzu ki daina bata ranki a kan zancen shi hakana.
Suma ai daukan magana ne mai yakai su ga kayan shi tunda sun san bai son raini shi.
Baki maji ta bude da nufin tai magana sai kuma bacin rai ya hana ta iya furta komai sai taja bakin ta tai shiru, amma duk AmiraA yarinyace karama zancen ta ya shiga ran ta sosai don haka tai shiru kawai amma a zucuyar ta ba dadi sam wani kunci take ji sosai.
Har dare sadauki bai shigo gidan ba don yasan abinda yaiwa kanin shi yana can ana jiran shi dashi cikin gida.
Shi ko yanzu daidai yake jin shi dakowa don ya fahinci daga mahaifiyar su har su duyan ta ba mai kaunan su a gidan gaba dayan su.
Sai yamma kamar kullun malam Habu yadawo gida ko hutawa ba,a bari yayi ba aka tare shi da zancen sadauki akan yaiwa Abdul mugun duka wai don kawai yasa mashi takalman shi na kwallo yafita dashi gurin wasa.
Kai kawai malam habu ya kada yace wanan yaron wanan yaron ya kai min ko ina a rayuwana wallahi.
Daidai lokacin Maji ta shigo dakin saye da hijjab din ta mai ruwa light green.
Tana mashi sannu da dawowa amma bai karba mata ba,sai cewan da yayi Maijidda wallahi danki ya zama min masifa a rayuwana .
Kullun har zullumin dawo gida nake daga kasuwa don nasan da zaran nadawo da,wuya ba,a tareni da zancen shi wanda zai bata min rai ba.
Shiru maji tayi tana,sauraren kalamin maigidan nasu a gaban sauran kishiyoyin ta yana cewa ki fada mashi wallahi zanyi maganin shi don na lura kamar ma ya fara shaye shaye ne a rayuwan shi.
Niko bari kiji in har hasashe na ya zama
gaskiya to wallahi ba zan barshi a gidana ba ya bata min sauran yara na na kirki.
Allah ya tsare ya kare Maji ta furta a fili aidama haka kawai zaki iya cewa bayan shi baki da,wani abin fadi ai,
Bata ce komai ba,sai hadiyan bacin ran da tayi tare da juyawa tana fadin Allah ya kyauta.
Malam Habu yace ai zai zo ya samay ni zan mu hadu dashi don ba zan yarda ya,sabauta min yara ba ga banza.
Maji dai fita tayi daga dakin don tasan ko ta,tsaya,babu abin da,zataji banda bacin rai kawai.
Din haka taiwa kanta kiyamallaini tabar dakin don bazata iya jure sauraren kalaman mijin nasu ba akan ita da dan ta.
Tafiya take zancen mijin nasu gareta yana ci mata rai don zancen sadauki shi ne zance mafi muni dake hada ta,da maigidan nasu.
Duk irin kwaram din da,aka,sha a,baya baya akan kishiyoyinta da ita a baya, baya tayar mata da hankali kamar zancen sadauki da ya taso mata a yanzu,
Yanzu saboda shi tana ji tana gani duk wanda ya kwaso zancen shi akan tane zai yaba mata don halin dan ta kawai,
A kulun kalaman maigidan ta ga dan ta yanzu yana kona mata zuciyar ta da jikin ta ba ma zuciyar ta kadai ba,
Ita a,zaton ta ai wanan abin abinda ya shafe su ne baki dayan su bawai ita kadai za,a dorawa laifin ba don itace mahaifiyar shi ne kawai kowa ke ganin laifin ta ita kadai.
Abin da ya kamata su taru su nuna bacin ransu a kai su tayata bakin ciki amma sai gashi kowa ya,zamay yabarta da laifi ita daya.
Amma babu komai ta furta a,ranta tare da hade yawun bakin ciki a cikin ta, tana mai sauke ajiyan, zuciya kawai.
Bata ankara ba,sai hawaye kawai taji yana biyo mata a idon ta.
Gaskiya zancen Sadauki yana tayar mata da hankali sosai ta rasa wanda zata kai kukan ta gare shi ya tayata bata shawara a cikin gidan.
Don duk yanzu suna matukar nuna mata kyama akan zancen shi gabadayan su gidan har shi maigidan kan shi.
Shin may nayiwa Allah da yai min wanan mumunan jerabawan haka akan dan tilon da daya da Allah yabani namiji a duniya ?
Ni dai nasan harga Allah ban cuci dan kowa ba a rayuwana da wanan jerabawan yafado a kaina.
Duk da ni marainiya ce na riki maraici na ban kai kaina inda Allah bai kaini ba, ina zama a matsayina na mara galihu har a gidan aure na.
A hankali ta kara lumshe idanuwan ta tana tuno rayuwanta na baya da kuma irin kokatin ba yaran ta tarbiyan da takeyi.
Ba komai take kara tunawa ba,sai irin dafin bakin da maigidan su yake mata a,baya,
Da yakan ce maijidda duk da ba komai ke gare ki ba,a,duniya ni ina sonki a yadda kike.
Don kina da komai da nake bukata sabida ke ta daban ce acikin matana, ba zan iya jure rashin mace irin kiba .
Kallo daya in nai maki yana wanke duk kan wata matsalar rayuwana don haka nake kwadayin samun zuri,a dake don nai alfahari dasu koda bayan rayuwana ne.
Murmushi gami da hawaye ne yazo mata a lokaci guda ta furta namiji kanin ajali.
****** ********* ******
Akwana a tashi yau Bintu satin ta hudu gurin gwago Asmau a garin sokoto.
Kullun sauraren take raji gwago na mata zancen zuwa gida amma shiru kake ji ba zancen, har ranan ta gaji tai wa gwagonta zancen komawan ta gida amma sai gwago take ce mata.
Haba Bintu yanzu ke har kina sha,awan komawa gida gurin wanan bakar matan uban naki mai mugun nufi a kanki ko yaushe.
Nifa da mahaifinki mun yanke shawaran kiyi zaman ki a nan don yace hankalinshi yafi kwanciya idan kina a guri na ko kiyi ni sa dasu kadan.
Don haka ki kwantar da hankalinki kiyi zamanki a nan ba zancen komawa gida don hankalin mahaifinki ya kwanta.
Badon Bintu taso ba dole ta yarda da zancen gwago din don tasan haka zancen yake.
Kullun adduan mahaifinte ke nan akan Bintu Allah ya kawo lokacin da zaki bar gidan nan zuwa wani guri ke ma ki huta hakana wa rayuwan ki.
Tunda mahaifiyarki ta barki bata damu da damuwar ki ba ko wani hali kike bata sani ba.
Gaki yarinya natsatsiya duk halarcin da kikewa matar nan da diyan ta kina bauta masu dare da rana ba gani take ba.
Amma kiyi hakkuri da irin rayuwan da kika tsinci kanki a ciki haka Allah ya kaddara maki taki rayuwan zai kasance a gidan uban ki.
Hawayen da ya silalo mata ne ta dan sa gefen hannun ta ta share a hankali.
Duk lokacin gwagon tana kallon ta a cikin muryan kuka ta dan dago kanta a hankali tace to gwago zancen karatuna fa ?
Wanan ba matsala bane ai Bintu zan yi magana a,samo maki makaran tar jeka kadawo dake can kasan layin mu ta gwaunati sai kici gaba da zuwa ko?
A hankali Bintu ta,daga kai alaman taji ta juya jiki ba karfi zuwa cikin dakin kwanan su don ta gyara masu saboda yamma yayi kuma,su basu sharan dare saboda ance baida kyau, yana kawo tsiya a gida.
A kwana a tashi ba,wuya a,wurin Allah Bintu tafara zuwa makaranta kamar yadda gwago tai mata alkawari a baya.
Da yake Bintu yarinya ce mai hazaka baiwanta daga Allah ne, sai bata sha wani wuya ba sosai a cikin karatun ta komai tana ganewa yadda ya dace.
Yawan aiken da take mata gidan malam Habu yadan sa tasaba da Maji da yaran ta don a gurin su kawai take dan samun fuska a gidan ko su ba wani can sosai ba.
Sai dai idan Maji ta aiko sayen masa in har Bintu ce a kan tandar suyan waina sai ta cika masu kula fam tace akaiwa maman ta.
Haka yasa watarana Maji tasa su Amira su dan yi kwalemar kayan su su ba Bintu don taga tana da bukatan haka saboda rashin wadatan da basu dashi ita,da,gwagon nata.
Gwago Asmau batai sanyi a kafa ba gurin shiga gidan don taiwa maji godiya ita da yaran ta, da suka ba yar ta kyautan kaya.
Ta shiga gidan bayan sallah azahar lokacin Bintu ta dawo daga makaranta ke nan.
Tare suka shiga ita da Bintu din, inda suka samu maji zaune a falon ta kasan tias din dakin nata tana gyara wani ganye da,alamar magani take hadawa dashi.
Sallaman su yasa ta dan gyara tana mai ansa masu sallaman su da fara,a a fuskan ta.
Sun gaisa da,gwago inda tafara zabga masu godiya tana mata fatan alheri akan alherin da sukai wa yarta, Bintu.
Cikin murmushi Maji take cewa ai Bintu yarinyar kirki ce halin alherinta ne yasa sukai mata haka.
Sun dan fara hira tsakanin gwago da Maji inda gwago ke cewa wallahi nakan so shigowa mu gaisa da ke, amma kuma yanayin gidan naku ne baida dadin shigowa don kowa idan ka,shigo sai ya,dinga ma kallon munafuki.
Maji tace haba dai hajiyan masa ai ba yau muke dake ba koma sun zarge ki da hakan ai su ma mutanen arzikin su suna shigowa gidan nan amma ban damu dasu ba ni.
Gwago tace ai babu komai insha Allahu zan dan dinga shigowa idan na,samu lokaci.
Suka mike suna,wa junan su sallama nan gwago ke cewa ina Sadauki ya yashiga kwana biyu bana ganin shi dai.
Murmushi Maji tayi tana cewa yana nan baidai zamane suna batun rubuta jerabawan su na karshe ne shi yasa ba,a ganin shi yanzu.
Allah sarki inji gwago Allah ya taimaka Allah ya bada sa,a Allah ya tsare muna su daga duk wani abinki dana sheri a rayuwan su.
Amin inji maji inda taji dadi sosai da addu,an mai masa da,taiwa sadauki wanda ta dade rabon da taji wani mahaluki yai mashi wanan adduan.
Har,zasu fita Maji tace su dan tsaya tazo inda tashiga daki ta dauko masu dan sabulun wanki da clean cikin irin wanda mijin su yake kawo masu duk sati don wankin tufafin su.
Gwago tana ta godiya da fatan alheri ga maji suka fito, a tsakar gidan nan suka hadu da amaryan su tana shigowa gwago na gaishe ta wani kallo ta,watsa mata na ke wacece ?
Gap da zasu fita daga get din gidan suka hadu da sadauki yadawo ko kallon arziki basu ishe shi ba sai ma gwago ke ce mai Umar sanda mazan fama andawo daga bokon ke nan ?
Ya wani sha toka fuska babu walwala ya ansa ciki ciki Maji dake tsaye daga bayan su data rako su take ce mai bakajin hajiyan masa tana gaida kai ne sadauki
Yace cikin wani murya ai na amsa mata mana ya shigewan shi part din su na,samarin gidan.
Allah ya shirya ka inji maji ta furta a fili sai gwago tai dan murmushi tace amin ke dai ai yaran yanzu sai addua kawai.
Ke dai kibi abinki da,addu,a Allah yasa halin iya kurciya ne kawai .
To Amin hajiyan masa halin wanan yaron sai shi wallahi haba bari fafin haka mana inji gwago ke zaki kara jan abinki ga jiki kina lurar dashi dasannu zai bari ai wanan kurciya ne Allah yasa takara fadi tai masu sallama ta tafi.
Bayan sun tafi maji taga yadace tabishi dakin shi suyi magana tunda Allah yasa yashigo a gaban idon ta.
Yana duke yana hada wayan tv tashigo dakin abinda yasa shi saurin dagowa ke nan daga inda yake duke.
A hankali take bin dakin dake hargitse da kallo sai warin dakin irin na,samari ke tashi daga dakin.
Cikin ya mutse fuska take ce mashi, yanzu kaiko inda kake kwana baka iya gyarawa babana ace dakin dan musulmi ne haka inda ake ibada?
Wai may ke damun kane haka babana na zaci kaine mutim na,farko da za,ayi koyi da halin shi nagari a gidan nan sai dai kasshh ban samu hakan daga gareka ba sadauki.
Naga alamar abinka ba mai yankewa bane, sai a lokacin yadago kai yadan kalli mahaifiyar tashi yana fadin may kuma nayi yanzu maji?
Yanzu fa na dawo daga makaranta tun safe da nafita gidan nan .
To babana shine baka iya,gyara muhalin ka haka dubi fa kagani ai wanan wani abin cutarwa ma yana iya shigo maka baka,sani ba.
Zan gyara ya bata ansa a takaice don yasan duk lokacin da tai amfani da kalaman babana a,gars shi maganace ta kwantar da hankali da fahinta take nufi a gare shi.
Don ba ko yaushe take amfani da kalman babana a gare shi ba tafi kiran shi da,Sadaukin da kowa a gidan yake kiran shi kamar yadda mahaifin shi yake kiran shi dashi tun yana karamin shi dashi.
Ta,dan dade a,tsaye tana kallin shi a cikin tausayawa dan nata ga,irin rayuwan shi ta bahagon halin da ya,fada ciki.
Hawaye ne ya,gangaro mata a,daidai lokacin da ya,dan dago kan shi ya kalleta don jin da yayi tayi shiru a,tsaye bata fita ba daga dakin.
Shiru yayi yana kallon ta sai ya dan dukar da kan shi gareta, tace babana ban son ganin rayuwan ka haka .
Wanan rayuwan da kake yi ba,shine irin rayuwan da na,soka dashi ba a,rayuwan ka.
Don Allah babana ka canza rayuwanka a gidan nan ka koma kamar ko wani yaro na gidan nan.
Ina son naga ka canza ka koma normal life din ka kamar kowa a gidan nan wanan halaiyar dakakeyi ba,rayuwan alheri bace a gare ka damu ma kan mu da muke naka.
Katai maki rayuwanka saudauki ka canza halinka don Allah kazamo min abin alfahari a,duniya, gama kowa dake tare damu.
Zan so ace na zamo uwa abin alfahiri ga duniya na nasamu da dan albarka a,rayuwana, kamar yadda sauran uwaye suke alfahari danasu diyan.
Zan so ka,sasauta halaiyar ka akan wanda kake a yanzu don samun natsuwar hankalina dana mahaifin ka.
A hankali maji ta fashe da kuka,wanda kuka ya sa ta kasa karasa maganan da take son ta fada mashi.
Maji ya ce cikin sanyin murya nifa ban san wani hali da nake yi ba,wanda har zaisa ki zubar da hawayenki haka akaina.
Kallon shi maji tayi a cikin mamaki don watau shi bai fahinci ma yana,da nakasu ba ke nan tare dashi.
Tace kako san har mutanen gidan nan sun fara zargin wai kana shaye shaye ne,
Ya,dago kai da,sauri ya,dan kalle ta sai kuma ya dukar da kan shi yace maji nifa wa yan nan mutanen sun fara isa ta,sun fara saka min ido