Showing 171001 words to 174000 words out of 373688 words

Chapter 58 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

ai na fada maka zan baka surprise dama to gani yau a,sokoto kuma dakin mummcy.
Yace saukan yaushe ? tace wallahi dazun nan na iso dama nasan bazan sha wahala ba gurin gane gidan ku don sha haranka.
A kaduna na kwana shiya ka gan mu a wanan lokacin, amma fa gaskiya akwai nisa.
Yace to ya hanya?
Tai wani har da idanuwanta tare da langabe kan ta tace hanya lafiya kalai tunda na gan ka.
Sadauki ya juya inda maji take zaune ta hade rai ba yabo ba fallasa a fuskan ta a lokacin.
Ni dai na,aje abinci ina cewa, ga abinci nan tace yauwa sannu little sister wai ya sunanki ne tunda nazo kike wahala dani.
Sai da na dago daga duken da nake nace Bintu tace wawwwo, sunan mu daya dake ashe.
Amma ki daina cewa kanki Bintu kamar wata yar kauye akiraki da,Fatiman ki kawai ai nice, name ne sunan mu.
Sadauki dai yakai zaune daga dayan kujeran nan bakuwar ta mayar da hankalin ta a kan shi suna dan hira jefi jefi.
Wanka na,shiga na fito na saka wani dogon riga light gren mai kamar bubu daga sama kasa an mashi sharp yafito da sura na na,daura dan kwalin shi a kaina.
Sam na ma manta cewa da bakuwa a falon nan nafito ina cewa Anty Amirah wai yaushe ne zamu tafi gaida baban su Amata.
Wai wanan pretty din itace last born din mune gaskiya tana da kyau sosai wallahi.
Kamar bazai bata amsa ba sai can yace No diyar sister din maman mu ne ita ga dai sisters dina Amirah ga maryam itace yanzu a,matsayin last born din mu.
Yanzu ita wanan din ba blood sister dinka bace yace a dan hasale na fada maki yadda muke da ita ai ko.
Take ta hade fuskan ta, tace there's problem here yace akan may fa tace No barshi ina dai magana ne kawai.
Maji bata falon tashiga ciki don bata iya,karasa hadiyan takaicin da yazo mata har dakin ta yau.
Wanan abin haka ba kimtsi ke kiran kanta da,suna wai sarakuwarta ta ina ?
Kai duniya kowa da,tashi matsalar dai kenan yanzu ita haka duk rabin jiki kusan tsirara shine wai tazo nuna kanta a gurin sarakai a haka.
Kai wanan tanbadewar da fitsara da may yai kamane haka wai tundaga wata uwar duniya yarinya ki taso kice wai kinzo gurin na miji.
Ban kai ga zama ba naji muryan maji tana kirana daga ciki da sauri nake na nufi gurin ta.
Zaune take saman gadon ta hannunta yana rike da caunter na zikkiri take ce min har yanzu wanan fitsararar bakuwar taku tana nan ke nan bata tafi ba ko?
Nace ai zaci anan zata kwana ne don naga daga nesa ta fito.
Tsaki taja tare da kawar da kanta a gefe tace yaro zai jamin wani sabon abin fade a gida yaya zanyi na fada mashi yai gagawan fita da ita gidan nan kafin mutanen gidan nan su ankara da ita.
Nace mama bani wayan ki ta mike min gurin sunan shi nai mashi massage kamar haka.
Ka gagauta fita da ita kafin mahaifinka ya dawo yasamay ta nan.
Na tura mai ina turawa nafito daidai ya fara karantawa wani kallon ke ko yabini dashi.
Nace sannu da zama ko wani kallo ta watso min kamar tasan nice na turo mai da sako yanzu tace yauwa.
Amirah tace, yau zaki koma dai ko?
Murmushi tayi tare da,gyara zama tace a,a har kun gaji da nine ke nan ko Amirah tace a,a ha mutum ai bai gajiya da bakon shi.
Yana gama karata massage din ya dagi kan shi sai kai mukai tozali dashi ina kallon matar .
Harara ya,kara watsa min niko nai mashi dariyar mugunta a fakaice.
Muryan shi mukaji yana fadin Fatima muje na kaiki inda zaki sauka kafin dare yayi cikin diriricewa.
May kake nufi da hakan ba a nan zan sauka bane gurin mummcy ?
Yace baki da hankali ne a cikin gidan namu zaki sauka don baki da kunya to mu nan ba haka al,adan mu yake ba
Yace so ki tashi na kaiki kafin dare yayi ban son daddy na ya dawo ya samay ki a gidan nan haka.
Don mu ba haka al,adan mu yake ba ya mike don dale itama bashiri tamike tare da daukan hand bag din ta tana cewa ina mummcy muyi sallama yace ta shiga alwala ke nan.
Yana gaba tana bayan shi suka fice daga gidan aiko basu dade da fita ba sai ga Baba ya dawo daga kasuwa a lokacin.
Sai da suka bar uguwar ya sauke ajiyan zuciya tare da cewa look Fatima bai nai maki wullakanci bane da hakan amma idan har mahaifina yadawo ya samay ki a gidan akwai matsala babba wallahi.
Kakanki kin sani wanan tsarin da kikazo dashi ba tsarin mune na hausa fulani ba.
Tai wani wal da idanuwan ta tace nima nasan da hakan amma ban dauki wanan a wani abu can da zai iya kawo maka matsala kamar ka babban yoro haka.
Yace wai ma ba wanan ba may yakawo ki garin nan ne wai Fatima ?
Fatima tai wani marairaicewa tare da kallon shi cikin wani yanayi tace,
Matsala aka samu danaji kace an maka mata agida ana batun auren ka shiyasa na kasa zama naga gara nazo ayita a kare a gaban iyayyen ka.
Sadauki ya katseta da cewa dakikazo gaban iyayyena kice masu may ?
Yace look Fatima da farko na so na karbi bukatanki gare ni amma yanzu hakan da kikai min duk kin jagula komai don haka idont think zan iyaci gaba da zama dake kuma again.
Ran Fatuma ya,sosu da jin maganan da sadauki yai mata sai dai dole yasa ta daure don tana son guy din.
Da sauri ta juyo gare shi tana cewa cikin hada hannayen ta biyu guri guda tare da marairaicewa tace don Allah U F kada kayi fushi dani.
Yin fushin ka akaina zai iya jefani cikin mawuyacin hali a rayuwana sosai wallahi don na mutu da son ka sosai wallahi.
Yayi wani guntun tsuki tare da kawar da kan shi gareta yana cewa don may zaki biyo ni har garin mu don baki da hankali.
Tace kayi hakkuri wallahi duk na,rude ne da ka fada min zakayi aure na,rasa may zanyi akai shiyasa nabiyo ka har nan.
Sadauki ya kara jan tsuki ya kalleta a wullakance yace na fada maki cewa anyi min mata a gida kuma bazan canza maganan iyayyena ba insha Allahu akaina.
Yace kuma ki sani na kyaleki ne yanzu don garin mu kikazo don haka yasa na kyale ki idan badon haka ba da na dauki mataki a kanki sosai.
Don bazan yarda ki hadani fada da iyayyena akan ki jamin wullakanci a gidan mu.
Ya farka mota da karfi cikin five star hotel da suka shiga da alama ran shi yakai kololuwar baci a lokacin.
Nan Fatima ta kifa kai tafara kukan tana rokon shi akan yayi hakkuri ya,aure ta zata zauna da wata su zama matan shi su biyu.
Tace na gane wanan far yarinyar dana gani itace proposer taka don naga tafaye shegen kyau.
Yanzu akan wanan karamar yarinyar kake min haka may zaka,gane a gurin yarinya karama haka ne please cikin kuka take magana.
Yace look Fatima na fada maki tun farkon haduwan mu ni ba mazina ci bane kuma ban iya,neman mata ba ina under control din iyayyena .
So kike akan ki na saba dasu ne for god sake don haka ki sauka na sama,maku masauki da safe ku kama hanya ku tafi.
And kuma na roke ki tun magana bata kaimu ga bacin rai ba kada ki kara,shiga harkata is over hakana.
Nan ya bude mota da zuman tafito su shiga ya kama mata masauki sai ma kunya da yake ji kada wasu su gan shi da mace azaci yazo yin wani masha,ane.
Cikin kuka tace no kabarshi zamu koma kaduna mu kwana gobe na koma Abuja.
Yace is better for you.
Nan tafito tashiga motan ta driver yajata tana kuka suka kama hanyan kaduna da yamma lis sosai.
Ya sauke numfashi duk da yaji tausayin ta yasan wanan shine kawai hanyan da zaibi yasamu kan shi daga shu,umancin ta akan shi.

A gida kuwa maji takai kololuwa da bacin rai sai jiran shi take ya dawo da yadawo yara yaba sokon maganin mama da kuma kaji da drinks da yasayo masu sanyi.
Yace ace yana massalaci zaiyi sallah mamatace koma may zaiyi ai zai shigo ya samay ni gidan nan.
Bai shigo ba sai da suka sallamay isha,i yashigo cikin gida kannen shi na gaida shi amma bai iya amsawa ba idon shi yana kan mahaifiyar su don jira yaji may tace mai yakeyi.
Ya zauna Amira tana fadin yayana kadawo ya bakuwar ta mu take, nan ma shiru yai mata baice mata uffan ba sai take cewa, a can ka barta ne ?.
Don Allah Amirah ki barni na huta haka na wanan tambayan ya isheni wallahi haba gaki kamar yar jarida.
Zama yayi ba,wanda yace kallah a cikin su sai zuwa can Maji ke fadi a da can baya idan ance min kana hurda da mata bazan taba yarda ba koma waye ya fada min.
Amma yanzu da yake ka fara rike kudin kanka gaskiya nai mamakin ganin wanan irin yarinyar ace wai da,su kake harka.
Allah yaceceni in ba kuma wani sabon rayuwan ne ka bulle min dashi ba aji dadin yin min sabon zagi a gidan nan.
Maryam na gaba ina bayan ta muka fito daga cikin daki mun samu mama tana mashi fada sosai kan wanan sabon halin da tagani a gare shi.
Maryam tai tsagal tana cewa ni dai kwata kwata,batai min ba mace haka yar bariki gata nan da ita sai wani iskanci take wai wayewa ke nan.
Maryam ba ga ku nan da irinta ba a gida ina yanzu Nafisa haka take shiga sai kaya ya matse ta sosai duk suran jikin ta a waje.
Amirah ke fadin haka wa maryam tace idan zagine kuma ai akwai shi a gidan ku.
Maji dai fada sosai take mashi akan mutum yayi hankali da duniya kafin ta kure mashi don duniya,ba matabbaci bace.
Baiyi magana ba sai chartting da yake da,wayar shi a zaton mu da bakuwar shi yake fira kafin ya fita zuwa gurin ta.
Amma har dare muna dakin zaune tare dashi sai hira yake da wayar shi kawai da amsa call.
Maji tace daka bar yar mutane acan may zataci sai a lokacin yai magana yace sun tafi maji.
Tace acikin daren nan suka tafi haka basu gudun dare yai masu a hanya.
Bai ce uffan ba yana zaune har dare goma da wani abu yamike yana fadin zai tafi ya kwanta sukai mai sai da safe kaina na duke ina karatu tun zaman shi ban yi magana ba a falon.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,

A LOKACIN MU KE,,,,

Sun shirya tafiya zuwa lagos gurin Michael don haka Nafisa itama ta nace akan cewa dole sai tabisu.
Tare sukai tafiyan inda ya turo masu da kudin suka shiga jirgi sai lagos a gida kuma tace zata gidan wata kaunan mamanta ne ta,kwana biyu.
Ranan da takwana uku da tafiya Umma ta kira waya tana tambayanta cewa yaushe zata dawo ne don tace ga jiya zata dawo bata dawo ba kada Alhaji yasan bata gida fa.
Tace sai gobe nan uwar tai mata fada kan dole ta dawo ranan don gujin bacin ran su gaba daya.
Amma har dare Nafisa bata dawo ba haka yasa Umma ta tayar da wani wanta guda yabi bayanta gidan yar uwarta ya dauko ta.
Yaje gidan yar uwar maman nasu tace ai Nafisa batazo ba ma gidan ta kwata kwata.
Nan hankalin Umma ya tashi sosai gashi kuma ko sun kira wayan Nafisa basu samu a lokacin.
Tun tana boye damuwarta har uwar kwakwaf mama Asiya ta fara ganewa yan dakin na cikin wani tashin hankali amma da ta tambaya sanin hali sai Umma take cewa, bakomai bane dama.
Kwanan ta biyar suka dawo sokoto haja haja cikin kudi, nan uwar tasata daki da tambaya ido ya riga ya bude tace buki suka tafi na wata classmate din su gusau ta san ko tambaya Umma bazata bari ba shiyasa tai karya.
Imirana ranan kamar ya make ta yai mata fada sosai sai dai basu sani shiga yake yana fita inda ya shiga.
Don Nafisa tayi nisa ko batajin kira yanzu don kar take kallon su tasan abinda basu sani bako.
Nan uwar taga yadda take facali da kudi take tambayanta sai cewa tayi wani Alhaji ne dan canji ta hadu dashi a gusau shine yabata kyautan dollars kuma yace ma zai zo gida yaga iyayyenta.
Umma ta fara jin dadi har ta fara sake magana ita yanzu arzikin bana yaci uban na da don yarta tayo babban kamu sosai .
Wasu ko sai dai su zauna idan dan su ya tafi yayo fashi ya kawo masu kowa a gidan yasan Nafisa ta samu dan canji don sai facaka suke da kudi abinsu.
Uwar bata san cewa yarta ta wuce sanin ta ba yanzu da ita da iyamurai take hurda su ko suna son yaran hausawa don sunce sunfi iya making, love.
Idan kuma ta fita su da su Raiha sufita susha kayan mayen su suyi tatil dasu ta dawo taita barci.
Ranan Amira zata shigo taga su Raiha sun dawo da ita yanayin data gan su a ciki sai bai mata dadi ba tashigo maji na ciki take fada muna nace Anty kiyi shiru kada wani yajiki ace kina hassada da samunta tace wallahi hakane amma may zanwa hassada a wanan gurin haka.
Yanzu har takai sun fara neman junan su idan sun sha ko kafin su sha sai sunyi masha ansu a tsakanin su sannan su koma,suyi tatil dasu.
Idan abinta yai nisa ita Nafisa har kwalba take dagawa don zuwa lagos din da,sukayi saurayinta Johnson mashayi ne sosai a can takoya shan giya.
Gashi sai dare ya tsala zata dawo ba,wanda ya sani sai mahaifiyarta ce zasu bude mata gida ta shigo.
Amma har lokacin Umma hankalinta baikai ga cewa yarta ta samo sabon rayuwa ba ita gani take gajiyace dai take dawowa dashi.
Don Umma na da,wani hali indan ta,dawo aiki ta zube guri guda bata motsa jikin ta, dan damadama,idan ita ke da duty a gidan ranan zata danyi kiza kiza.
Hjy kubura ta fara jin zance Nafisa a gurin wata kawar aikinta, amma sai bayata yarda da zancen ba ta dauki maganan ba gaskiya ba tunda kawar tace har gari suke bari zuwa wani guri yawon banza kuma ita tana ganin Nafisa a gida.
Kuma abokanta su Raiha sun riga sun gagari iyayyen su babu maijin kwabo su, suji yanzu.
Ganin bata san labarin ba yasa kawarta cewa kai kila dai ba gaskiya bane kama daine suka gani suka ce itace.
Sai dai Umma ance laifi tudu ne, take naka ka hango na wani,
Zance ta shine sadauki yana can kasan waje ya zama tattacen dan iska, yana hurda da,turawa yana sayar da kwaya da fashi.
Inda Allah zai kashe mata bakinta ranan sai ga danta ya shigo da sauri yana cewa su Maji dasu mama Asiya ku kuna,tv tashan sport yau su sadauki zasuyi wasa.
Nan kuwa suka shiga kunnawa suka kai tashan wasan kwallo har falon Baban su, sai da ya kunna suna zaune aka fara fitar da yan wasa sai gashi saye da kayan wasan shi sun fito, yana saye da rigan shi an rubuta mai Umar sokoto, Nomba 9,,,
Haba take yaran gidan gaba daya suka dauki ihu suna,wallahi ga yaya sadauki ga yaya sadauki.
Nan aka fara wasa ranan duk gari ya dauki ihu sosai don ganin dangida kuma haifafen dan gari yaje fitar masu da sunan su.
Ba atashi wasan ba,saida yai masu ci biyu dada fa ihu ba kama hannun yaro wani haushi yakama Umma tace kai ku kashe min wanan shegen abin sai kace wani abin kwarai wai kwallo kafa kukewa wanan ihun haka.
Tasa aka kasshe mata TV ta baba daga dakin shi ya aiko mata su kunna Tv su ga Umar nan ana hira dashi a TV.
Rananta baiso ba amma dolen ta, ta kunnawa daidai Sadauki yana fadi cikin turanci da ba,wanda yasan cewa ya iya ta haka slays English irin na turawa yana fadin.
Yana mika gaisuwan shi da godiyan shi ga mutanen kasar shi Nigeria dakuma iyayyen shi da,sukai mai tsaye yakai ga wanan matsayin.
Haba gida ya kara daukan ihu da murna sai bugo waya mutane keyi suna cewa ku, kunna TV su gan dansu ana hira dashi a NTA sports.
Dakin Maji kan ranan ba a cewa komai don farin ciki da murna maji saida tai kwallan hamdala ga Allah.
Yayi kyau yai fari sosai hasken shi ya fito da kyau kana ganin shi kasan dadi da ni,ima ya sauka mashi.
Kwana da kwanaki bakajin komai sai zance UF kawai ke tashi a gari nan sauran yaran gidan su, suka,shiga barazana da daukan kai a gari.
Baba ya kecewa su mama bayan ya tarasu yace yana


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login