Showing 150001 words to 153000 words out of 373688 words

Chapter 51 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

dakin ya bude.
Bin dakin nake da kallo duk da dan sauyi da dakin ya samu an saka mai kayan zamani a cikin sa.
Kafin na fara gyara na fara aiwatar da nufina da yakaini dakin, daga nan daga can ina bude wani kwali dana gani saida naja baya da sauri don tsoron da naji.
Kwayoyi ne ciki irin masu tsada da,akai muna lecture a kasan makil a cikin kwalaye.
Gaba daya na kwashe su da,sauri nakai toilet din dakin na watsa ciki nai flushing din su suka wuce,
Haka nauwa sauran syrup din da nagani kai duk wani magani sai da na turashi a toilet din ya wuce.
San nan na,gyara mashi dakin tsab nafito da sauri kafin ya,dawo ina fitowa nazo na zauna ina jiran yadda zamu kwashe dashi.
Bayan wani lokaci muna zaune sai hira muke kwasa tsakanin mu ya fado dakin idanuwan shi sun kade sunyi ja dasu.
Yan uwan shi ke mashi sannu da zuwa amma ni ko kallo bai isheni ba don nama raina da,al,amarin shi gaba daya.
Magana suke mashi amma,bai iya,basu cikaken amsa sai cewa yayi Maji wa ya gyara min daki na.
Wani kallo ta,watsa mai kamar na tsana tace wakasan yake da,kokarin haka,ba Fatima ba.
Inda nake zaune da,waya ina game ya,kalla kamar zaiyi magana sai ya kuta kawai mikewa yayi har yakai kofa yace tare da kallon inda nake zaune.
Ke kawon min abin karyawa na daki zan watsa ruwa ne yanzu.
Maji tace bana son suna shiga dakin ku idan kuna gida bari mana ta mika mai maji Amira ta fadi hakan a lokacin har na mike ko tsaye don na,shiga kitchen.
Ance abu ga manya ashe uwar ta dan fahinci da,akwai wani abu don haka ta kyale mu.
Saida na dauki kayan zuwa dakin ta saka hijjab din ta tabiyo bayana batare da sanin kowa ba.
Ina shiga ban san yana tsaye daga kofa ba sai ji nayi an kai min shaka da karfi yana fadin Uban wa ya baki izinin shigowa dakina ki kwashe min kaya.
Ina kikai min pills dina yar iskan yarinya kawai mara mutunci.
Idanuwa na,sun futo sunyi ja don matsan da nasha jinake kamar zan shude.
Yakara cewa uban wa ya,aikoki ki kwashe min kayana?
Muryan maji mukaji daga bayan mu tana cewa, ubanka ya turo ta ta,kwashe mara mutunci kawai sake min yarinya kaji.
Ya sake ni da sauri sai da naji wani iska mai sanyi ya ratsani lokaci guda, ta juya tana kallona take cewa ina abinda kika kwashe mai din?
A hankali nace mata na,yi flushing din su a toilet sun wuce, tace kwayan ke nan ko nai shiru ban bata amsa ba.
Ta nuna min hanya tace zoki wuce kinji rabuda dan iska mara mutunci kawai, da,sauri na,fita zuwa part din mu a hirgice dani.
Azuciya ta ina cewa anya zan iya kuwa wanan irin shaka haka kamar zan shude lokaci guda.
Na zauna jiki ba karfi sai mazurai nake da idona can sai ga maji tashigo na zaci zatai min magana amma sai naji tayi shiru batace min uffan ba.
Ina nan zaune sai gashi ya shigo dakin cikin shigan shi na mutunci zaka dauka wani mutumin kirkine can idan ka gan shi a lokacin.
Magana yake wa Maji babu wanda yaji may yace mata sai dai mukaji tace Allah ya tsare kawai.
Ba irin yadda ta saba mai addua ba idan yace zai tafi wani gurin.
A,a yayana tafiya kuma zakayi yau bayan jiya kadawo?.
Yace ba dadewa zanyi ba kaduna zan tafi akwai wasan da zamuyi ancan yau da yamman nan gobe zan dawo.
Har kofa suka,rakashi cikin jin dadi a ran su suna tayi mashi adawo lafiya yana daga masu hannun shi.
Maji batai min magana ba sai da rana na idar da sallah ta kwala min kira nazo da sauri ina fadin gani mama.
Samu wuri ki zauna tace min ida na na kai zaune a kasan ties din dakin nata.
Fatima fada min komai kada ki boye min don naga ke kina da hankali kinfi sauran tunane.
Nafara magana,saiga Amira tashigo hakan bai hanani fasa maganan da zan fada mata ba.
Nace tun fitan shi cikin dare jiya ana ruwa nagan shi ta,window dakin mu har ya dawo a cikin maye banyi barci ba.
Naga kuma yashigo da leda yana tangadi haka yasani sanin cewa da kayan mayen ne ya dawo a hannun shi.
Shiyasa da,safe nace zan gyara dakin nashiga ba fara neman su sai gasu na gani nan na nuna mata hoton su dana dauka a,wayana dakuma yadda nai flushing din su.
Allah yai maki albarka Fatima, da yanzu duk wanan abin shaye su zaiyi a cikin shi tayaya wanan bazai wa mutum illa ba wai.
Nan take fadawa Amira tun da yazo rai a bace yana tambayan wa ya gyara mai daki nasan akwai magana shiya da yace takai mai abinci don ban taba jin yace haka ba nasan akwai wata a,kasa.
Bin su nayi na,samu ya shaketa wai sai tafito mashi da kayan shi sai gani.
Amira tajuyo inda nake race kai Bintu akwaiki da karfin hali wallahi ai danice sai kawai na,suma.
Nace niko muddi ina gidan nan anty naga yayi abin shan sa na dauki alkawari sai nai mai magana.
Baki, gani zai kashe muna uwa da bakin cikin shine anty?
Murmushi Maji tayi sai ta kara jin Bintu ta,shiga mata a,rai sosai fiye dama baya yanzun saboda ita tai wanan kasadan haka.
Amma a fili cewa Maji tayi kiyi a hankali Bintu kin san karfin ku ba daya,ba dashi badon Allah ya kawoni ba da Allah kadai yasan irin dukan da zai maki kan kayan mayen shi.

****** ********* ******
Tuki yake amma zuciyar shi sai faman tukuki takw mai yana kitayatta idan ya samu sa,an Bintu irin dukan da zai mata watarana.
Haka ya isa ya kira maji tana kallon kiran shi amma taki daukan wayan nan ya gane har yanzu fushi take dashi ke nan.
Da yamma ma bayan sun gama,ball yakira sai Bintu dake falon ta dauki wayan tasan shine amma sai cewa tayi mai wayan bata kusa ta kashe wayan kit.
Haushi da takaicin yarinyar suka rufe shi a lokaci guda yace a fili, I will deal with dis girl.
Bari na dawo zata sha mamakina don naga akwai raini a kanta.
Ance kowani mahaluki danasa irin baiwan sai dai wanda ya,rena nasa kawai amma kowa da irin wanda,Allah yai mai.
Hakane ga,sadauki don yanzu yana cikin matasan da kasa ke alfahari dasu a fagen kwallon kafa.
Don idan yana a cikin kwallo Allah na bashi sa,an jefa kwallo ga raga, yaci duk tsananin wasa idan ya kama sai yakai gola.
Suna gama wasa washe gari ya kamo hanyan sokoto bai iso garin ba sai zuwa yamma sosai ya iso gida.
A lokacin muna,gyaran falon Maji duk da,ba aikina,bane amma ina tsaye ina,taya anty maryam mofing din kasa.
Sallaman shi yasa gaba daya suka juyo kan shi suna,mashi sannu da zuwa.
Amma banda ni da na zage ina,aikina hankali a,kwance.
Sadauki ya samu kujera ya zauna akan daya daga cikin kujerun falon nan suke ta tambayan shi ya hanya ya wasan su na can.
Naso na share shi don ina cike da takaicin makuran da yai min jiya kafin ya tafi tafiyan dayayi.
Sai nai tunanen bari dai nagaida shi kodon mahaifiyar su dake zaune din bata,rage ni da komai ba na rayuwa.
Don yan magana,sunce ko lahira wani tana cin albarkacin wani, na dan waiga gurin da yake zaune ya wani lumshe idanuwan shi nace.
Sannu da dawowa ?
Tankar a mafarki ya tsinkayi zakkakan muryan na ina,gaidashi.
Da sauri ya,wani bude idanuwan shi, yana kallo na na zaci ba zai karba sai naji yace yauwa.
Ban kara bin ta kan shi ba naci gaba da,abinda nakeyi a lokacin, ganin da nayi bai bar cikin falon ba yasa na aje mopan ina cewa anty maryam ki karasa sauran zan shiga ciki.
Dakin mu na nufa duk da magariba ne amma sai na,fada kan gado in tunanen ashe kuwa zan iya taimakawa Maji kuwa.
Shigowan Anty maryam din daki yasa ni dakatar da,shawaran da nakeyi a lokacin.
Tace lalai ma Bintu watau gudowa kikayi kikaki karasa,min aikin ko?
To tashi yaya yace ince ki hado mai abin sha yasha kafin ya tafi sallah.
Nace anty ke mai zai hana ki hada mashi nifa ban iya masifan shi wallahi.
Mutum ko yaushe a murtuke kamar mugu sai faman bakin rai da hararan mutane.
To naki yake so ai yana ganina,baice na,hado mashi ba,sai ke, yake son ya,wahalal.
Ta fadi hakan cikin yanayin zolaya tare da yin dariyar keta a fili tana ta darawa.
Nace wallahi anty badon mama ta haife shi ba,sai nace yayi gadon mugun ta,sosai.
Maryam ta juya tana fadin lalala haka,kikace mashi bari naje na,fadawa Maji kince yayi gadon mugun ta a,gurin ta don haka,baki hado mashi.
Da sauri na mike na,sha gaban ta ina cewa don Allah anty yi hakkuri kada ki hadani da mama barin fito na kawo mashi.
Dariya tasa min tace koke fa aikw ce da shegen rashin ji kike taba mai kayan shi.
Na,jera ruwa a jug da,cup cikin dan tiren su na,roba nafito mashi dashi falon .
Yana zaune a,falon har wanan lokacin ya,dauki kafan shi daya,ya,dora,a,dayan yana,kallon news din da ake a,tashan NTA.
Na kai turen gaban shi na aje da zuman na bar gurin.
Yace waye zai zuba ruwan da kika girke kamar wata,bakauya haka dake sai shegen sa ido.
A ya,tsine nace ai dama yar kauye ce ni.
Yace ke baki da kunya fa don naga kina,son raina ni a gidan nan don kin samu guri.
Nace a hankali badai a,guri ka,na,samu gurin ba ai, da hanzari na,mike na,shige ciki kafin ya,furta,wani abu.
Nan na barshi baki bude yana mamakin da,alajabina sai ya kuta,
Yana kutawa daidai Maji tana,fitowa da,alwalan ta,do ita,saidai ta jira kiran sallah kullun haka dabian ta yake.
Ta bishi da harara tana cewa kada ka,soma taba min yarinya wallahi za,ajimu dakai a gidan nan.

Da,dare muna,zaune abinci kowa ke ci sai gashi ya shigo falon wanan karon ya canza kayan jikin shi zuwa wasu kanan kaya masu matukar kyau na maza.
Ya zauna ba,wanda tai azancin mikewa ta bashi abinci nima da nake taimakon shi ina,bashi sai na,share shi kawai don yanzu ban ganin kimar shi kaman da can baya.
Waya na dake gefe yai kara don haka nakai hannuna da sauri na dauka don ganin kowaye mai kira,na.
Kabir ne, yake kirana da,sauri na dauka don kada kiran ya tsunke a lokacin.
Da murmushi a,fuskana nake cewa Assalamu alaikum sahibi rayuwa,
Ya,amsa da cewa haba Fatima kishin ruwan rashin jinki da,ganin ki yana,son illantani amma,ke ko a jikin ki baki damu daki kirani ba.
Na dan langabe kaina kamar yana,kusa dani nace, cikin yanayin tausayawa.
Nace wayyo Muhammad Kabir dina,wallahi ba,haka,na,bane kasan yanayin karatun dana,fara ne ba hutu yanzu, amma nima na damu da na gan ka ai.
Ya ce hummm saika ce dagaske Fatima keda har yanzu baki iya,sakewa dani idan ina kusa dake.
Ni dai yanzu ina,rokon ki rage wanan masifan kunyar taki haka,na adan bani gurbi nima.
A hankali na,dan saki wata,yar dariya mara sauti nace yadda kake jin rashi na a kusa dakai hakana nima yanzu nake jin naka ai.
Yace aiko danafi kowa sa,a a duniya zukekiyar yarinya kamar ki tana jin kewan tsoho kamana haka.
Maganan shi ta,sani yar dariyar da ban tashi yi ba tare da langabe kaina a hankali saman kujeran da nake kusa dashi.
Wani irin tsaki mukaji ya,sake tare da,mikewa tsaye yana fadin maji ni zan dan shiga gari sai da,safe.
Tace abincin fa,bazakaci bane yace No abarshi kawai tea zan sha idan nadawo.
Ya fita maji na fadi zaka gurin mugun halin naka ko don nasan dai can ka nufa.
Baice uffan ba sai yar guntuwar murmushin da yayi iya yake.
Yana fita daga falon maryam tace Bintu yanzu gaba,daya kin canza daga Bintu kin koma wata mara kunya,can dake.
Wayan ma,a,gaban mutane kike ba,kunya,ba tsoron kowa, Amira tace barta sai watarana yaya ya,fasa wayan nan din karamar aikin shine hakan tambayi maryam kisha labari.
Nace aiko da,ya,biya ni koda yake inma ya,fasa,aishi ya,saya,min dama shikw nan yayi amai ya lashe ke nan.
Nan suka,sani gaba suna min sheri wai suna son gani Kabir din nan daya sace min zuciya haka,ya,mayar dani wata,mara kunya haka.
Nace anty Amira,bafa yaro bane matan shi biyu da yara,biyar.
Kafin nakara,furta wani abu sukace a lokaci guda mata,biyu da yara,Bintu ?
Shine har kike wani rawan kai haka akan mai mata da,yara baki tsoron kishiya ne ke?
Nan na,basu labarin irin takakan da matarshi takawo min hargidan mu a,kauyen mu.
Cabdijam wallahi kin fara,gani ke nan may ke cikin auren mai mata yanzu banda,tarin rashin kwanciyan hankali.
Nace cikin yar murya,to anty wanda ya samu badashi za,ayi ba idan hakane yafi min zama,alheri arayuwana Allah ya,tabbatar min.
Amira,tace wallahi kina,da karfin hali ashe haka Bintu nikan danice da tun zuwan matarshi gidan mu mun rabu dashi wallahi din alama,ya nuna ko a gida,akwai matsala,ke nan.
Kafin nai magana,sai mukaji maji tana cewa, ke kada ku zugata Alkah ya,hana,auren mai mata,ne halan.
Idan ku bakuyi ita da,tasan ciwon kanta ai bataki abinda Allah ya, kawo mata,ba.
Maji aini wallahi yadda,naga,kunayi a,gidan nan bani ba,auren mai mata,kuma.
Tsuki uwar tayi tace tunda,kece Alkah basai ki zabawa kanki abinda kike so ba mugani.
Nan dai mukai tahira,akan Kabir da iyalin shi dakuma inda yake aikin shi.

Washe gari tunda safe muka,tashi da,raba tsaraban mutanen kaduna ashe dankalin Iris ya,sayo mai yawa inaga,buhu guda ne da,manjan miya,wa kowan su saida safe mukaita kasawa,aka kaiwa kowa nata,kason suka,karba,suna,godiya cikin basarwa.
Maji tana da,wanan halin komai kankantan abu sai ta,rabashi tabawa kowa agidan sai dai in abin ya tsaya,wamu, yaran tane kawai.
Bai shigo gida,ba,sai misalin sha,dayan rana,lokacin mun fita,zuwa gidan wata kawar Amira da,matar yayanta ta haihu.
Maji kawai ya,samu a part din tana,zaune tana, gyara,tasbahan ta,daya,tsinke ya,shigo.
Su gaisa take tambayan shi sai a lokacin ke nan yatashi ko yace Maji kin san na kwaso gajiya shiyasa da,muka dawo sallah na,kara kwantawa.
Yace ina yaranan suka,tafi ne ina,son a danyi min aiki ne kadan wani magani wani mutum ya bani na,hausa nake son su dafa min.
Sun fita,zuwa gidan kawar Amirah yanzun nan amma,aiba jimawa zasuyi ba a can din.
Shiru yayi sai zuwa can kuma yace amma maji wanan yarinyar sai naga kamar fitsarta, ya,fara yawa fa?
Maji tace wake nan kuma ? duk da tagane wa yake nufi din.
Yace wanan bakuwar yarinyar taki mana,
Wa wai Fatima kakw nufi kowa dai?
Ita din ke nan don ban san sunan taba ni.
Fitsaran may tai maka,ko don ta,ceci rayuwanka da,halakan shan kwayoyin data,kwashe a,dakin ka shine fitsaran da,kake gani tana dashi.
Kai haba Maji ni ba nufina,ke nan ba,wallahi amma ki duba,yadda,take waya,da,namiji a gaban mutane babu kunya a,idon ta.
Au to idan batai waya da mai sonta,ba,dakai zatayi ke nan ko?
Koko anan zan tabbata,dasu basu aure su a,rayuwan su.
Kai ni Maji ba haka,nake nufi ba,fa kawai dai ina gudun kada ta bata,sauran yaran nan ne kawai da irin fitsaran ta.
Ita Fatima ce zata bata yaran ko kai dakw abin kunya a gaban su suna,kallo kuma,babu yadda zanyi dakai.
Akwai fitsaran daya,fi yau da,girmanka,ana ganin ka a cikin maye babba da,yaro ana min dariya.
Dukar da,kan shi yayi kasa yana,dayasanin maganan dayayi a,lokacin daya sani kawai ya dauke matakin daya kudurta a,rayuwan shi final.
Nan tace gaba da,fada mai maganganu masu tsuma zuciya na irin zabar mata da mutuncin ta,da,yakeyi ga idon mutanen duniya.
Kanshi na,duke sai tafasa,zuciyar shi takeyi yarasa irin son da Maji takewa wanan baren yarinyar haka wai.
Wani irin zafin rai yakeji a lokacin tankar aradu ce ta,sauka,mashi a kirjin shi duk sanyin AC dake ratsa falon hakan bai hanashi zufa ba .
Muna,shigowa gidan da murnan mu yanayin da,muka,gan su a ciki sai da ya,tayar muna da hankalin mu.
Suna gaida shi ya,dago idon shi da,suka kada,sukai mashi ja kamar garwashin wuta ya amsa masu.
May yafaru kuma,yaya Amira take tambayan shi tare da,duban fuskan uwar su dake zaune tana abinda takeyi.
Yace babu komai Amirah kaina,ke ciwo bari naje nasha,magani dakina.
Yana,fita Amira ta juya, gurin maji tana tambayanta da,cewa anyi wani abin ne kuma,Maji ?
Shi dai ya,sani inji maji gaskiyane baiso k8n san da,anyi mai fada,sai ya,koma kamar wani namijin zaki dashi.
Shiko yana fita gidan sashen shi ya nufa yafada kan katifan shi yai lamo dashi kamar wanda,yake barci,sai dai ba barcin yake ba .
Damuwa ce ke damun shi na baisan abinda zaiyi ya,farautawa uwar shi rai yaji dadin ta,ba.
A hankali wasu siraran hawaye ke zubo mashi yasan Maji tana,da,gaskiya don yau ba mai son cikin dubu ace nashi ne ya lalace.
Ya juya,yana,cewa,wayyo ni wanan rayuwan may nayi rayuwana,ya,koma,haka,alokaci guda.
Ba dadi ga,uwana,ba,dadi ga yan uwana,haka ma wasu al,umman garin danake tare dasu ada can baya.
Shi dai yasan yayi iyawayin shi akan ya,daina wanan harkan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login