Showing 177001 words to 180000 words out of 373688 words

Chapter 60 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

shi tun lokacin.
Kwana bibiyu yana zuwa ziyar su idan yana gari don yaga how far jikin yaron yake yanzu bayan an mashi aiki.
Sai da malam yaga dan shi ya samu lafiya sosai ne wani yammaci yazo gida yai wanka ya samu maria ita kadai a,gida yaran sun fita zuwa makaranta.
Ya dauki bucket ya debi ruwan wanka sai tazo zata karba ta debo mashi yace a,a ki barshi don ni yanzu ba zamana kike a gidan nan ba.
Wanan kalman ya tayarwa maria da hankali har yafito ya shirya yafita daga gidan tana a cikin tunanen kalamin shi.
Ba bata lokaci ta samu uwarta da zancen daya fada mata nan uwar tahau fada tana fadin shi wani irin mutumi ne da bai san kaddaraba koda talla ko ba talla wanan al,amarin rubutace abune ga yaron nan.
Don haka kibarshi zan fadawa wa iyayyen ki maza su samay shi aji may yake nufi.
Saidai bata san ya riga yai magana da mazan gidan nasu ba tana samun su da zance sukace babu ruwan su suje su da suka bata su gyara da kan su.
Nan yaje gurin malamin shi ida yake daukan karatu har yanzu ai mashi cigiyar yar bazawara koda kauye ne yaura kawai ya huta da halin maria.
Shi ko sisko sai bayan kaman kwana ashirin yana ganin an manta da zancen sai gashi ya fito,
Dama akwai yan sandan farin kaya da ko yaushe suna zagayen shi suka cafke shi sai police station nan aka fara jibgan shege ana gana mashi azaba sosai.

****** ********* ******
Zancen auren mazan gidan mu su yaya imirana ance sai budurwan shi ta kare jaratun NCE da takeyi za ai masu aure saura,watani su kare karatun su abinda ya,dakatar da zancen ke nan .
Amma Umma kullun akan zancen in auren yaran nan ya,tashi zanyi abu kaza zamuyu abukaza take fadi ita da mama Asiya.
Wani lokaci sukanyi hirane don maji taji taji haushi ko takaici gasu a,kullun cikin saka kunne suke don suji ko sadauki na nema wani guri suje su suke zancen.
Wata diyar kawar maji uwar taso a,hadasu kamar may amma sadauki yaki yarda da zancen yace shi aure baya gaban shi tukun na.
Amma su Umma naji sai gasu gidan suka kai suka mai karfi matar tace tasan da zance ai itace matace a hada shi da yarta shi yaki yaron.
Suka taso da kunyan su suka dawo gida da kunya da ,bakin ciki

A haka kwanaki ke shudewa,suna komawa sati zuwa watanin karatun mu sai ci gaba yake sosai ba kama hannun yaro.
Yau ni kadai nafita zuwa makaranta don maryam ta gama exam ita banjin dadin fita amma haka na daure nafita.
Sadauki da yakai wata biyu kasan turai yadawo wanan tafiyan tafiyan arzikine sosai yayi don yasamo makudan kudi a can.
Sai dana dawo na samu sunyi bako dan takura ya dawo ban samay shi a gida ba ya fita don sunce tun safe suka sauka garin.
Amma na samu tsaraba masu kyau harda waya da maryam tace ya canza muna ya sayo muna.
Sai da dare kusan tara ya,shigo gidan da sayayan abubuwan bukatu irin su sheltox sabulan wanki abubuwa masu yawa yace a,raba,abawa kowa nashi tun a bakin motan shi ya dinga ba,almajira suna kaiwa sauran part din gidan wakowa nasa.
An shigo da na Maji ke nan sai gashi ya shigo yana waya yai wani irin haske ga,wani dan saje daya bari a,fuskan shi, daganin shi komai ya zauna.
Har ya zauna bai daina,wayan da yakeyi ba sai da,ya dauki lokaci a hankan yana,wayan shi.
Jin ya gama waya yasa na fito daga dakin mu don naimai sannu dazuwa da kuma godiyan tsaraban mu daya kawo muna.
Still da,waya a hannunshi haka dai na daure nace yaya sannu da,dawowa?.
Mun ga tsaraba mun gode sai lokacin ya dago kai daga abinda yake a wayan shi.
Idanuwan shi masu kama da shi ya zana su da kan shi, yaba min sai kace wani tsohon maye.
Yana son ya bude baki ya ansa min amma kuma ya kasa maga a lokacin saboda gaba daya na canza mai nai mai wani kwarjini a fuska.
Har nabi ta gaban shi na,wuce zuwa gurin TV na dauko littafina amma bai samu damar amsa min ba.
Ina ba da baya ya lumshe idanuwan shi a hankali tare da,saurin kawar da idanuwan shi akaina.
Yace a ran shi may maji kebawa yaran nan ne haka,wai suke canzawa lokaci guda haka.
Ya manta cewa da bazarshi muke taka rawan mu yanzu gaba daya gidan don yanzu ko abinci baba ya daina saye sadauki ya dauke mashi nauyin haka ko.
A hankali ya sauke wani sanyayan ajiyan zuciya yana kuma kan aikin shi.
Ashe lissafi yake don ya fara business wanda ba kowa yasan da hakan ba a gidan.
Sai fili da yasaya ana mashi wani irin mamakeken ginan gida har an kusa kammala aikin ginan ba wanda yafadawa don zurfin ciki irin nashi.
Ya dawo da kwana biyu Kabir yazo gurina mama tasa akai mashi girki hadade wanan zuwan akan zancen auren mu da take son ayi badadewa ba yazo gida.
Sun gaisa da mama harda hjy kubura da suke daswa naciki na ciki da mama tazo sun gaisa yai masu alheri.
Bayan tafiyan sune muna zaune da Kabir saman Carpet dana shimfida muna can gefen wani dan lungun shigowa gidan .
Sai faman hira yakw min kamar kullun irin yadda ya kamu da,sona farat daya haka.
Yau sai nake jin hiran nan shi kawai banjin dadin shi sosai don yadda yake magana sai umm a,aa nake bashi amsa da eh.
Yake sheda min zai fara turo da kayan lefe a gurin maji don ai mata halarcin da take min a nuna mata itama uwace gareni yace daga baya zai turo mota akaita kauye gurin iyayyena da kayan sai a saka muna rana.
Yace ko hakan bai maki ba nace yayi kwarai da gaske don in anyi haka nafi kowa jin dadin hakan irin yadda mama take nuna min kauna abin ba,a cewa komai.
Yace Fatima ina tausayin rayuwan ki naji duk irin rayuwan da kikayi a,wajen matar babaki shine yasa na kara kwadaituwa da na aure ki Fatima.
Ban san lokacin da,wasu hawaye masu dumi suka fara silalo min ba a fuskana.
Ni dai ina godewa Allah don Allah yana sona ko yaushe yana hadani da masu kaunana sosai.
Kabir na ganin na fara kuka hankalin shi yai matukar tashi sosai yace subbahanallahi Fatima ko magana ta batai maki dadi bane yasakaki kuka haka.
Ban daina kuka ka ba,sai kara dan sauti danayi yace cikun murya karyyaya don Allah Fatima kibar kukan nan ki fada min abinda nai maki haka har yasaki kuka.
Hankici ya,dauko yasa yafara dan goge min hawayen dake silala a idanuwana yana bani hakkuri.
Har yaya sadauki ya shigo get din gidan bamu san ya shigo ba, yana ganin abinda kw faruwa da hanzari yaja da baya numfashin shi yaji yana fita da sauri da sauri idanuwan shi yaji sun rufe mashi lokaci guda bai ganin wuri sai can ya samu ya furta innalillahi wa,inna alaihin rajiun.
Yaji wata natsuwa tazo mashi yaji lokacin da kabir ke fadin Fatima ki daina,wanan kukan haka kada ki sakani kuka a gidan mutane.
Da kyat nai dan shuru cikin muryan kuka nake cewa ni kukan godiya nakewa Allah da ya hadani da abokin zama wanda yasan kimata da daraja dana iyayyena akullun Allah yana,min gata a,rayuwa na.
Haka mama ta rikeni amana duk da batasa koni wacece ba har tazo tasan kowa nawa ashe don may bazanyi kuka ba yaya kabir.
Kabir ya sauke ajiyan zuciya yana cewa wallahi duk kin daga min hankali Fatima,
Ashe kuwa zan iya rabuwa da mace kamarki a,rayuwa na,macen da,tasan dadin halarci irin haka.
Nan dai muka dan kara hira mukai sallama dashi sai mun hadu a gida garin mu akan zancen auren mu.
Yai min salama yatafi na dauki kayan da ya,kawo min niki niki zuwa cikin gida dasu sai ganin yaya sadauki nayi yana exercises a kofan shi kusa da inda muka zauna.
Ni dai na ratsa shi na shige da kayana ciki yace yar iska muna fuka kamar wanan yarinyar wai tasan soyayya irin haka kiji dashi mara kunya kawai.
Ina,shiga gida mama tace ,a,a har surukin nawa ya tafine nace eh, yace sauri yake ya isa gida kada yamma tai mashi a hanya.
Nan su maryam suka shiga bude kayan maji tace kai maryam baki da kunya,wallahi tace kai maji nima ranan da,aka,kawo min kaya ai haka tai min matace kun fi kusa ai ba a,shiga tsakanin ku sai mutum yaji kunya.
Nace Anty kowa ya dauki abinda yake so aciki amma turare abawa Baba da mama shi.
Mama tace aiko wallahi Alhaji ya yaba wacan da,yakawo maki kika,bashi .
Nace mama baba yana son turare tace sosai ma,wallahi shi ko yashe cikin saka turare yake.
Nace ai yaya sadauki ya biyo shi don ko shin yana part din nan tun daga waje mutum ke gane cewa yana gi,,,,,
Sai ganin mutum nayi a gaba na ya,watso min idanuwan shi yace munafuka kawai aikin ke kenan sakawa mutane ido kullun.
Dariya su Amira suka kwashe dashi sukace ai munki fada maki ya shigo ne tun da shi dodon ki ne ko yaushe.
Na,turo baki ina cewa ni wallahi ban son kalman muna fukan nan an tashi daga yar kauye amayar dani kuma munafuka yanzu.
Yace dama may kike ba yar kauyen ba munafukan banza kawai ka ganta sumu sumu da ita kamar ba shakiyiya ba a baya.
Kai yafa isa haka kai ke nan in kana gida yarinyar nan bata da,shakat ga rayuwan ta kawai wani irin miskilin mutum ne wai?
Yace may yakaita fadin sunana don kawai taja min fitina mara kunyan yarinya kawai shigewa nayi ranan harda kuka sai da nayi ban futo falo ba har dare ina ciki kumshe shikuma yana gida zaune.

****** ********* ******
Haka ya kwanta tunanen halinda ya gan mu da kabir yai matukar tsaya mashi a zuciyar shi inda ya,rasa may yasa abin yadamay shi haka a rai.
Wata zuciya tabashi amsa da don itama yanzu ta zama kaunan ka kada wani abu ya samay ta ya samu mahaifiyar ka ke nan.
Bai samu barci ba sai dare so sai gashi zuciyar shi tana faman azazzazalar shi kan ya dan sha wani abu ya samu relief tun da ya dawo yakw jin yadan sha wani abu kawai a ran shi.
Haka duk yana gida bai da natsuwa inba ya dan samu abin bugarwa ba ko yaya yake ya dan shawa ran shi yake samun shakat.
Yanzu kuma gashi dare yayi sosai yan san ko ina kafa ya dauke babu inda zai samu wani dan abu ya taba.
Haka ya kwana a wahalce ga tunane ga kuma son shan maye ya addabe shi a zuciyar shi sosai.
Washe gari da kyat ya samu jam,i don saura kiris ya rasa jam,i da yanzu ya zama mai jiki haka yasa a uguwar da yake gina saida yai massalaci babba a gurin don mazauna uguwan.
Zazzabi mai zafi ya rufe shi da safe yinin ranan bai fita zuwa ko ina ba saboda sana din rashin shan mayen da bai samu yi da,dare ba.
Ganin har kusan biyu bai fito ba yasa mama cewa maryam yau ko yayan ku lafiya gaba,daya bai leko gidan nan ba,fa yau.
Amirah tace aiko naga breakfast din shi a kitchen dana dawo kila kuma ya fitane tun da safe zuwa wani guri.
Mama tace ba halin shi bane hakan in yana gari ko yayane yakan shigo kafin yafita zuwa wani guri.
Maryam jeki ki dubo min dakin shi idan baya gidan ne mu sani ko kai maji zai zauna daki har wanan lokacin bai fita,ba,biyu saurafa yanzu.
Jeki ke ki du bo min shi ki gani in baya gidan ne musan bayanan yafitans ban son shegen gadamar tsiya kinji.
Maryam tana,tura kofan taji a bude yake sai dai bataji motsin akwai mutum a cikin dakin ba sai ta fara dan kwankwasa kofan da hannun ta.
Da kyar ya iya bude bakin shi yai magana yace waye ?
Tace nice yaya maryam ce,
Yace shigo kofan a bude yake ai.
Maryam ta tura kofan ta,shiga ta hango shi kwance saman katifan shi ya rufe jiki lif da katon bargon shi.
Tace yaya lafiya maji ce dama tajika shiru tace nazo na dubaka ?
Yace cikin muryan marasa lafiya,
Kice mata yau bana jin dadin jikina ne sosai amma yanzu zan kokarta na fito ai.
Da sauri maryam ta juya zuwa cikin gida tana shedawa maji halin da ta samu sadauki a cikin sa.
Maji tace subbahanallahi shi ne ko waya ya kasa dagawa ya kira yafadi baida lafiya nan maji ta mikw tare da daukan hijjab din ta ita da Amira sai dakin.
Yadda maji ta samu dan nata kwance hankalin ta yai matukar tashi sosai ta haushi da fada haba babana.
Baka da lafiya baka sanarwa mutane asani a taimaka maka sai kashige daki ka rufe kai ka dai a ciki.
Can tace wai may yake damun kane haka ?
Cikin dauriya yake ce mata murya na,rawa,
Zazzabine sai amai da nake dan yi tace subbahanallahi shi ka kwanta haka ba,wani magani ko taimako.
Barin kira Alhaji aje asibiti yace da sauri No maji barshi barshi kawai zan kira wani yakira min likita abokina yazo ya dubani yanzu.
Maji ta juya gurin amira tana fadin ke dauko min wayana a gida da sauri kinji.
Jin sunce amai da zazzabi yana jin sanyi yasa na tsaya ban tafi ba sai dana hada mai tea mai kauri sosai naje masu dashi.
Na samu sai rawan dari yake yana cikin wani hali sosai a lokacin.
Na ce wa mama ga tea mai zafi na hado mashi yasha ko sanyin zai dan rage mashi da kyata ta samu ya tashi ya wanke baki ya zauna bakin katifan daya kwance akai.
Ya sha tea din sai yacire baki maji tace ai gara kasha kafin likitan yazo ko ?
Muna tsaye daga gefe kofa cirko cirko muna kallon shi ya,shayen tea tsab kamar yadda uwarshi ta umurce shi dayi.
Sai ko a take, ga zufa ya karyo mashi a lokaci guda yana gyatsa alaman dan sauki ya samu.
Maji tace Fatima ki fimu dabara aini duk na rude wallahi komai na kasa yi ma gaba daya.
Shigowan likita da abokin shi Bashar yasa duk da halin ciwon da yake ciki ya dagi kai ya,watsa muna harara kowan mu tagane nufin shi haka muka juya sukuku damu kamar munafukai muka bar dakin sai maji ce kawai ta rage a ciki.
Likita ya duba shi ya,rubuta magani Bashar yaje ya sayo masu, bai dade ba,ya,dawo da maganin da allurai a leda akai mashi yamike wai zaiyi alwala a lokacin.
Sukace ya dan bari ya dan samu sauki sai ya,tashi yayi sallah haka ya koma ya kwanta yana numfashi guda guda.

Ni dai tun wanan zuwan da nayi gaidashi ban kara zuwa ba,suke ta faman rawan kai da abin su.
Amira ce mai jinyan shi sosai da yan uwan shi don va laifi sun nuna mashi karamci don suna zuwa gaida shi sosai gaskiya mutanen gidan.
Can cikin ran sadauki mamaki take yadda tun ranan bai kara ganina ba zuwa gaidashi ba.
Gashi har su umma suna zuwa duba shi balle ni da yasan ina da kokari sosai gurin kula da mutum.
Amma gashi duk wanan rashin lafiyan dayayi ban shiga gaidashi ba ko sau daya tun randa yafara ciwon nakai mai tea ban koma ba.
Har ya fara samun sauki sosai yana dan fitowa ya,sha iska wajen gidan su.

Tun da safe aka kirani wai babana baida lafiya kwana kusan uku ke nan bai masan inda yake ba.
Ban,san, lokacin da na kama kuka ba na tayar da hankalina sosai maji ta fadawa baba yabani dubu hamsin yace naje nagani idan abin yai nisa kwarai mukawo shi asibitin gari.
Na kama hanyan tun da,safe nai sa,a na samu mota sai kauyen mu gaskiya na samu Baba yana matukar jin jiki wai ma yaji sauki ke nan daga gona ciwon ya kamashi aka kwaso shi zuwa gida.
Na sa aka kai shi asibitin nan gari sukace gado zasu bashi mama tabawa tace aikaji irin ta idan an bamu gado wazai biya kudin magani nace ba matsala a kwantar dashi kawai.
Tun ranan na kashe kusan dubu goma sha takwasa ga magani da allurai da,za ai mashi.
Sai yamma maji ta samu waya na don tayi kira yana kashe bayan mun gaisa take tambayana yaya mai jiki nace mai jiki da sauki gamu asibiti an bamu gado ma.
Tace asha ashe jikin ko sosai ne nace wallahi mama duk baba ya ramay yakoma kamar bashi ba wallahi.
Nan dai tai mashi fatan alheri tare da,Allah yaba shi lafiya na ce amin mama tace duk abinda ake ciki na,bugo masu su sani.

****** ********* ******
Sai washegari bayan na,tafi ne sadauki ya uya,shigowa cikin gida a,falon maji ya zube bai jin karfin jikin shi ko kadan sai yawan jin amai da yakeyi.
Yakai awa biyu baiga gilmawa na ba yace maryam maryam daga inda take zaune ta amsa mashi ta mike tazo gurin shi.
Sai da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login