Showing 231001 words to 234000 words out of 373688 words
Chapter 78 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
ce ba anty.
Amma kin san zaman su haka a gurin ki hatsari ne babba kuwa a gare ki ?
Yanzu dabanice nagan su akayan ki ba kuma nasan halinki may kike ganin zai faru ?
Nace nayi kuskuren barin su a tare dani amma na aje su don sheda kawai.
Tashi kiyi flushing din su yadda kikayi a ranan tun wani bai gani ba hankalin maji ya tashi.
Yadda tace din haka nayi na zubar dasu a cikin toilet suka bi ruwa suka wuce.
Nan na barta zaune tayi shiru tana tunanen dalilin da yasa na boye mata tasan cewa na yayan sune duk yadda akayi.
Da dare da Bashar yazo ta samay shi yadda ya fahinci bata cikin hayacin ta ya sa shi matsa mata da tambaya may yake damun ta hakane wai ?
Tace matsalan yayan mune yayana ina ganin kamar bai daina shaye shaye ba har yanzu.
Da sauri yace, kai may kika gani ban tsan mani yana sha ba kuma har yanzu gaskiya.
Tace koma may nene Bintu ta san komai sai dai tana boyewa ne, nan ta bashi labarin yadda mukayi da ita da rana.
Ya nisa bayan yaji maganan ta yace tabsa tunda kikaga taki fadi akwai magana gaskiya amma yaya akayi ta samu wanan abin a gurin ta in ma nashi ne.
Tace nima shi nake ta tunane nasan tayi hakane don farin cikin maji don kada hankalin ta ya kara tashi kuma ?
Tace nima abinda na fhinta ke nan hakan take boyewa don kada aji hankalin shi ya tashi amma ba matsala gobe da safe zanzo na kaiku makaranta anan zan fito mata da zancen muji.
Yadda suka tsara haka din ne kuwa da safe sai ga Bashar mun gani a jenction din gidan mu yana jiran mu.
Muna shiga muka gaida shi yafara hanya sai dai tuki yake a hankali, sai naji yace malama Binta ya garin dai nace lafiya kalau yaya Bashar.
Ya ce ranan sai mutumina ke fada mai ta,asan da kikai mashi da kayan shi ?
Da sauri na dago kai na kalli maryam sai na dukar da kaina nai shiru bance mashi uffan ba.
Yace Binta yaya akayi kika kwaso abubuwanan a gurin shi shiru nayi babu amsa.
Yace look Binta ba boyo ki fada min komai nai maki alkawarin bazan fada mashi komai ba akai don hanyan da zamu ceto rayuwan shi nake son mu bida a cikin sauki.
Nace shi may ya fada maka don nasan na daukan mashi alkawari bazan fadawa kowa ba wanan magana.
Sai Bashar ya nisa tare da buvun sitiyarin motar shi yace ina ganin baki fahince mu bane kawai.
Nace yaya Bashar kadai gane cewa nashine ne ko to abar maganan don Allah, kyau alkawari cikawa.
To shike nan na fahince ki yanzu, amma don Allah yadda Allah ya hore maki gane irin halin rayuwan da yake shiga ina son muyi amfani da wanan daman naki guri gano abinda ke saka shi a irin wanan halaiyar.
Sai yai kaman ya bari sai kuma ya koma ciki tsunbul dashi al,amari gaskiya akwai daure kai a cikin sa sosai.
Nace nima na fahinci haka amma gaskiya ban tsan mani zan iya ci gaba da wanan aikin ba saboda yai min warning sosai akan mashi shishigi ga al,amarin shi.
Zaki ya mana inji Bashar abinda nake so dake shine kamae yadda baki tsoron fada mashi gaskiya haka zaki daure ki ci gaba da fada mai a kai tsaye.
Murmushi nayi nace anya yaya zan iya hakan kuwa yace kwarai kuwa Binta ai zaki fitar da tsoro ne ga komai ki kama aikin ki,amma fa kuma kin san aikin nason jan mutum a jiki sosai.
Nace da sauri yaya zanhi in ja yaya sadauki a jiki mutumin da kullun yake cikin hattarana da tsangwama.
Yai murmushi kafin yace wanan kuma,wani haline nashi nan dai ya fara fada min ga yadda zanyi akai nace to ba matsala zan gwada nagani amma idan naga da,wahala gaskiya bazan yi ba.
Yace zakima iya tunda kina da hakkuri kawai ki dan sake dashi shine farko.
Muna kaiwa school ya sauke mu tare da min fatan alheri nace Allah yasa muyi nasara dai.
****** ********* ******
Yana tsaye ya bada baya waya yakeyi kuma a handfree yasaka wayan nashi a lokacin.
Magana yake da wata mace sai dai magan tankar fada sukeyi yake cewa na fada maki ni mace bata a gaba na yanzu.
Don haka ki daina yaudaran kaki don baxan aure ki ba koma zanyi aure yanzu akwai qualities din abubuwan da nake so ga matar da zan aura ke kuma baki da ko daya daga cikin su so kima daina yaudaran kanki a kaina.
Ban san may yarinyar tace ba sai ji nayi tace wanan kuma matsalar kine ni da kika gannin ban taba zina ba a rayuwa ta kuma akanko ba zan fara ba.
Da sauri na juya don nashige ciki sai nai karo da dutse ina batun faduwa naji ya riko ni bai bar wayan ba kuma bai sake ni ba.
Nace a kakausan murya sake min hannuna kaji malam, wani kallo ta watso min na ki shiga taitayinki kinji ko.
Sai da ya gama wayan ya juyo gare ni yace ashe kuma banda sa ido harkin fara lebe ne kuma ?
Cikin tsiwa nace, akan may zanyi labe Allah ha rabani da annaminan ci ni fita zanyi nagan ka kuma zan koma.
Murmushi yayi yace idan ma baki taba ba ai yau gashi kinyi ko?
Amma anyway zan baki bashin na yau don kin min alkawari a baya don haka nima ya kamata nai maki uzurin na yau.
Nace aini ba don ka nayi ba don mama nayi amma ba saboda kai ba sake min hannuna na wuce.
Yai dan murmushi kadan abinda bai saba yi min ba yace ba abinda yakamata kice ke nan ba Fatima kice dai kin boyeni don baki son ace ni din mashayi ne ko ?
Amma ko banza dai ni koma maye aikin min alheri ko Fatima don haka nima zanso ace nadan yi maki ko na rana guda nane kamae yadda kikai min din.
Cikin wani shu,umin murmushi yace min tafi sai kin jini nan gaba, nima,
Na dan kalli hannuna da yai ja saboda riko da yasha a hannun shi nace mugu kawai ashe yajini yace may kikace da gudu na zura zuwa cikin gida kada ya kamani sai ganin mama nayi a gaba na tsaye.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,
ALLAH DUK WACCE TA KARANTA BATA BIYA BA KAINE SHEDA INA BINTA BASHI,,,,,
Zaune take duk abin duniya ya damay ta a ranta ga shi yanzu daga ita har dan ta sun zama abin magana a gari.
Ko a gaban ta zataji mutane suna bayar da labari yadda ma ba,ayi abin ba haka za,a zake ana labarata shi.
Kowa da,kalar abinda yake fadi a bakin shi ba dama yaron ya fita sai yara abokan wasan sbi su fara gudun shi kaman sunga dodo.
Haka zai dawo gida yana kuka yana fadin abinda yara yan uwan shi sukai mashi.
Abin duniya ya ishi mariya a ranta tai kuka har tagaji ta hakkura don kan ta babu wanda zata kai kukan ta gare shi.
Gashi zaman gidan kawai takeyi tun lokacin da aka dawo da ita daga gidan su daya tura ta manyan suka zo suka bashi hakkuri.
Ba don yaso ba ya hakkura da ita haka na amma zama takeyi ba abinda ke shiga tsakanin su.
Koma cefane ne idan ya shigo dashi sai dai ya aje mata a kofan daki ba tare da yai magana ba.
Idan kuma tana son wani abu sai dai ta tura yara su fada mashi abin da ake bukata a gidan.
Ranan dai taga yana ta gyaran wani kangon dakin shi a zaton maria shine zai koma ciki don ya bar masu dakin su sai bata kawo komai a ran ta ba.
Don dai tasan ba aure zaiyi ba mutumin da ko kudin cefane sai ya fita ya nemo masu abinda zasu ci.
Ranan wani laraba ta zaune tana wanke wanke taji wasu mata su biyar sunyi mata sallama.
Suka gaisa da ita sai suke fadin wani ne dakin da aka gyara daya daga cikin su tace, tana ganin wancan ne da ke da sabon siminti.
Basu bi takanta ba suka nufi dakin suka shiga ciki suna dan dubawa anan suka barta tsaye da mamaki.
Bata iya masu magana ba suka fita sai gasu da kaya suna shigowa dashi.
Kasa daurewa maria tayi tace wai bayin Allah daga ina haka bakuce min komai ba kun kama shigo da kaya cikin gidan mutane.
Dayar matar tace a,a shi mai gidan bai fada maki yai aure bane yau matar zata tare ma.
Ai mu amarya muka kawo yanzun haka munzo gyaran dakine ma kagin anjima mu kawo ta.
Allah ne ya taimaka maria bata fasa ihu a gaban su ba amma sai ta fada dakin ta can ta fasa abinta ita kadai tana fadin na,shiga uku yanzu da wani zanji halin da nake ciki ko da zancen kishiya kuma?
Bata fito ba sai da taji fitan matan daga gidan mayagin ta ta dauko sai gidan su ga girkin da ta dora a saman wuta nan tabarshi ta fita.
Da kuka ta samu uwar ta tana fada mata abinda ya samay ta nan uwar tashiga zagi tana fadin amma Atiku ya cika tsohon macuci wallahi.
Yanzu da yake nan yana yawo kaman almajiri ashe har yana da kudin da zaiyi aure, bamu sani .
Nan sukai ta kullawa ita da uwarta a tsakanin su har dare ya soma ta fito zuwa gida.
Koda ta koma ta samu har girki ta ya kone wuta ya mutu don kan shi nan dai ta kwashe shi haka na don bazata iya girka wani ba yadda take ji a lokacin.
Atiku na shigowa gida ta tare shi da masifa da jidali nan ya dakatar da ita yace.
Maria ki shiga hankalin ki wallahi kada na bata maki rai a gidan nan kin dai san ina da haushin ki dama to ki iya kan ki dani wallahi ko ayita a akare a gidan nan don dama kin kai min ko ina wallahi.
Nan ta shiga zage zage tana kiran shi macuci azzalumi dama ashe yana da kudi yake ce masu baida shi yanzun ina ya samu kudin aure.
Yace wanan aure kikace dole na samo shi don naji dadin rayuwa na kuma duk mata ta shigo gidan nan kikace zaki daga muna hankali wallahi sai dai ki koma gidan ku kinji na fada maki mara mutun ci da tausayi kawai.
Ke abinda kikai min a duniyan nan har kina da bakin magana don zan kara aure.
Kuma ai dole na kara aure na samu wace zata kwantar min da hankali na wadda zanji dadi da sanyin rai a gurin ta.
Ba irinki da kikai shekaru da shekaru kina gwada muna boni ni da diyana ba a gidan nan.
Don tsaban iya cutan ki harda dan ciki kika zalunta dakanki da kanki kin mayar damu abin zunde da kwantance a gari saboda tsaban kwadayin ki.
Yana fadin haka yai alwala ya fita, daga gidan ran shi a bace yana kutawa shi kadai.
Bayan sallan magariba kaman masu jiran a idar da sallah sai ga yan kawo amarya da gudan su sun shigo gidan.
A zaton maria za,a kawo mata amarya dakin ta irin na al,ada sai taga sabanin haka.
Sai ma jin da tayi lokacin yaran ta suna cin abinci a,waje matan na gardama a tsakanin su cewa.
Ko wanan ne akaiwa fyaden cikin su dayan tace karamin ne fa akace sai dayan tace a,a fa ance babban ne mai sayar da pure water uban ma bai ko san tana aza mashi tallah sai ranan da abin ya faru ya sani.
Kai amma wanan matar ta cika azzaluman mace ita tajawa dan ta wanan bakin sunan haka har ya mutu ana kwatance dashi a gari.
Wani irin zafi da radadi maria taji a ranta take ji kaman ta fito ta basu amsa amma kuma ita kadaice a gidan kada su taru su yi mata tsinanen duka don taga a tsaye suke su ma.
****** ********* ******
Haka kawai ranan na tsiro da tafiya kauye ba,shiri nacewa mama dake shirin zuwa gidan buki zan tafi garin mu yau.
Da sauri ta juyo ta fasa daurin dan kwalin da takeyi tace zaki kauye Fatima ?
Na dukar da kaina a kasa nace eh mama mamana ce bata da lafiya jiya ake fada min a waya da dare.
Tace assha amma gaskiya ban son tafiyan ki a motan kasuwa yanzu da zaki bari zuwa jibi idan angama bukin nan sai nasa a kaiki.
Nace mama yau nake son zuwa don na dawo da wuri insha Allahu ba abinda zai samay ni mama ki kwantar da hankalin ki.
Ta je gun jakkan ta na hannu ta dauko min kudi sun kai dubu goma tace gashi kiyi kudin mota dashi idan min tafi yadda kika samu jikin nata sai ki min waya nace nagode mama.
Sai da na gama shiri na tsab na fito falon lokacin su Amira ne kawai a falon ganina da jakka kamar may shirin tafiya suke tambayana.
A,a gaki kamar may shirin tafiya mana Bintu ?
Nace eh anty zani kauyen mu ne yau, gurin mamana har ma gurin babana zan leka na kara dubo shi insha Allahu.
Maryam tace yaushe zaki dawo nace sai na kwana biyu gaskiya to Allah ya kiyayye hanya.
Har kofan gida inda zan hau Napep din da zai kai ni tasha maryam ta rako ni na tafi.
Sai dai a cikin ranta bawai ta yarda da zanyi tafiya bane don ganin mahaifiyata kawai dai na gudu ne don kaucewa yayan su sadauki.
Amma sai ta sa a ranta zata saka ido taga shi wani reaction zai yi akan tafiyan nawa.
Takira Bashar din ta take fada mashi da kuma abinda itama take kullawa yace haka daidai zan tayi saka ido nima insha Allahu.
Ban isa gida ba sai da yamma don ban fito da wuri ba kuma motan bata tashi da guri ba.
Ina isa gida sai ganina mama tayi kwatsam tace a,a ke kina hanya ne ashe nan muka gaisa nafito da dan tsaraban da na kawo masu aka shiga rabawa.
Dakin da bakowa suna aje tarkace a cikin shi sai wani dayan kani na da ya dan tasa ya dan girma.
Nan na gyara na kai yar jakata a ciki tare da shimfida tabarman kaba sabo da mama ta bani na dinga kwantawa akai.
Ranan haka na kwana ina juyuyi don yaushe rabona da kwana saman tabar ma, zaman birni ya fara bata ni yanzu.
Sai tunane nakeyi ko may su maryam suke yanzu don nasan dai basu kwanta ba saboda a can dare baiyi ba sosai kila suna can suna kallon season film din da muke bi a zeecilmer .
Miskili jarababbe mugu azzalumi na furta a fili nace yanzu ai sai ka samu wata ka lalata ba dai ni Fatima Binta ba kuma.
Nace ko hutu ya kare ban dawowa sai naji ka tafi kabar kasan zan dawo macuci kawai.
Allah kadai yasan irin iskancin da yakeyi can bariki idan ya tafi babu kowa nan ma gida ya yi shaye shayen shi balle can inda babu kowa tare dashi.
Mazina ci kawai mai boye kama ashe shiyasa yake wani kallon mutane duk shakiyai ne irin shi gashi kirkiri ya rabani da Usman ba wai ban son usman bane amma saboda bakin zargin shi dole na rabu da Usman din ba don naso haka araina ba.
A haka har barci ya dauke ni ban sani ba sai washe gari kiran sallah da ya tayar dani a lokacin.
Bayan na idar da salla ban kwanta fitowa nayi na gyara gidan ko ina don yana bukatan gyara.
Ga karan gidan da akai danni duk ya tsufa har ya dan dadare daga yadda aka jera shi da farko.
Makewayin su ma haka tsufin tsumane na wani tsohon babban riga aka tare bayin dashi.
Ga kwata ya taru sai diyan sauro da kuda da gurin ya tara ya wani canza launi duk da kasa ne yashi amma rashin samun gyara yasa gurin ya canza launin shi.
Nan ma sai dana gyara nasa musa kanina ya debo tsakuwa da yashi muka zuba ya dauko wani falalen dutse muka kara dagwarawa a saman gurin don mutum ya samu gurin hawa yai wanka.
Kafin dan wani lokaci gidan ya koma tsab dashi kaman bashi kaca kaca da farko na dora ruwa muka dama kunu ina gamawa na dora sauran tuwo na gyara ma ma yaran don dashi suka saba karyawa.
Sai dana gama nai wanka na shirya tsab dani dakin da nake na gyara kafin lokacin sa girkin rana yayi.
Sai da mijin mamana naji ya fita daga gidan don bai tashi sai rana ya raba wani lokaci ma alokacin zaiyi sallah.
Na shiga gurin ta na samu tana nade kayan wankin da na samu tayi jiya da na zo.
Nace ta bari dakin na zo na gyara mata