Showing 354001 words to 357000 words out of 373688 words

Chapter 119 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

muji daga ni, imar su.
Yace haka yana da kyau sai kuma may kike gani ya dace ayi don kudin kwallon da na samu wanan karon ina son inyi amfani dashine a sadakatuljari,a
Nace akwai magidanta mabukata yaya da abinda zasu ci da iyalinsu yake masu wuya akwai kuma marayuwa da ke neman taimako don Allah ya kamata ayi awani abu akai yace insha Allahu angama queen.
Na kuma gode da wanan shawaran taki zan duba nasan abinda za, ayi na taimako ga alumma daya dace ayi.
Sai da mukai kwana uku na shirya na tafi gaida su mama don lokacin mutane sun dan tsagaita shigowa muna sosai gaida mu.
Wanda wasu gulma ne kawai ke kawo su gidan don suga yadda gidan namu yake ne.
Shiga nayi na alfarma dagani har Amir da Iyya muka tafi gidan namu sadauki ne ya jamu a mota.
Mun samu su lafiya sai dai gaskiya duk akwai sauyin canji a tare dasu mama ce kawai zaka kalla kasan bata da wani matsala a tare da ita.
Amma sauran gaba daya duk sun wani jemay kamar basu ba Umma duk kiban nan nata yanzu ya tafi tsufa ya taso mata sosai tare da ita.
Ga furfuran dole daya bata masu kansu ita da mama Asiya yanzu kana ganin su kasan suna cikin wani bakon yanayin da basu saba ba a baya.
Mama tai matukar farin ciki sosai da ganin mu ta shiga haba haba damu a gidan.
Kaunata dake gurin ta ta murje tayi kyau da ita sosai harda tsayi naga ta kara min da haske ga sabon da naga sunyi da mama sosai yanzu.
Itako yar bakin rai na kusa awa daya a dakin bata fito ba tana can tana ji da kanta a daki don suna da wata yar dattijuwan da ke masu komai a shiyan su basu ko kauda kara sai matar ce mai aiki.
Can tafito tana wani cika tana batsewa nace a, a anty Amira ai na zata kin fitane ban san kina ciki ba wallahi.
Ta zauna tana cewa ina ciki na kwanta ne ina jin shigowan ku bandai fito bane kawai.
Nace Allah sarki mun samay ku lafiya tace Alhamdullahi a takaice inda Amir yake zaune yana wasa ta kalla tace my boy kaine wai kazama wani bulele haka dakai?
Nace anty aiko yama ramay sosai don tun shekaran jiya da muka dawo bai faye lafiya ba baya son cin abinci sosai sai anyi da kyat yake dan shan tea.
Ai dolr kuyi kiba kuna cin gashin kanku kun manta da kowa kina kokarin raba muna dan uwa damu.
Nace kai haba anty ni na ma isa na rabaki da yayan ki kin dai fada ne kawai ra,ayinki.
Amma ai tsakanin ki da yaya sai Allah tace lalaikan gani nan bari nan takalmin kaza.
Murmushi yayi daga inda yake zaune kusa da mama yace wai ke yaya zance da mukayi ne na ma,aikacin bakin da kikace min kin samu.
Ta wani lumshe ido tare da bin lafiyan kujeran da take zaune akai tace yana nan yaya.
Naga baka da lokaci ne ai sai na matan ka yanzu shi yasa ban fito ma da zancen ba ranan da kazo.
Yace kin san Fatima yanzun queen ce lalaba abata nakeyi a hankali don banson ganin bacin ranta akan komai.
Haka kuma duk wanda yai niyar bata mata rai wallahi sai inda karfina ya kare akan mai shi don bazan dauki rozarci akan iyalina ba ko kadan.
Tasan da ita yake wa warning don haka taja bakin ta tai shiru tana sauraren shi har ya kare zancen shi.
Yace mata ki fadawa mutumin yazo mu gana gobe da dare karfe takwas don kafin aiki ya taso min idan son samu ne ma har aurwn nake son ayi akafin lokacin.
Sai ya mike tsaye yana fadin shi zai fita nace don Allah yaya rogo nake so da zogala na dade ina son cin sa tun muna turai nake kwadan shi wallahi.
Na juya gurin mama ina cewa mama akwai man shanu ai ko ?
Tace akwai shi fatima yace yau kuma abinda kuke son ci ke nan kuma kayan yan kauye.
Abinda aka samu a turai ina shi ina kwadayin abincin yan kauye kuma maimakon yai kwadayin kayan sanyi.
Mama tai murmushi don sai yanzu ta fahinci wanan mugun kyau din da nayi bana banza bane ashe dama tai hasashen hakan amma sai taga ai Amir ko shekara daya bai kaiba watan shi ma na takwas ke nan da haihuwa.
Ko iya sai lokacin tagane ciki gare ni tace kai masha Allahu uwar dakina Allah ya raba ku lafiya yasa wanan karon ba dan zama asibiti bane kuma aka samu kamar maigidana cewa Amir.
Au ita yanzu cikine kuma da ita ina ruwan naga banza wai kina nufin kiyi saurin cika gida da diyan ki kafin wata ta shigo ko may?
Banza kuma Amira wai ke wata irin shashan yarinya ce mara wayo haka dake ?
Abin arziki ya samu maimakon kiyi farin ciki da karuwan da aka samu amma mugun halinki yakaiki ga hasashen banza kuma.
Kai maji nidai ba dama nai magana akan Bintu sai an zageni don tabi ta hada mutane da ku baku ganin kowa sai ita haba maji.
Nace nima anty wallahi ban so cikin nan yanzi ba Allah dai ne ya kawo shi don ban manta da wuyan da nasha ba gana wanan din.
Amma to yaya zanyi Allah ya riga da ya kawo shi basai na yi hakkuri ba da ikon Allah.
Amira kada fa naji kinzo kina karamin murya naba yara suzo maki weekend na hanaki kice zakiyi fushi ya fada mata hakana.
Komai Amira tai mai yana kokarin shanyewa ne don ya fahinci ita haka Allah yayita da bakar magana.
Shi kadai ne kawai nasu ke zuwa masu daya koshi don baya biye mata ne kwai suke zaunawa lafiya amma ita haka take da kowa ba dadi nata kalar rayuwan ke nan kuma ita.
Shi dai ya fita da yaji fadan mama ya tsanan ta akan Amira din yana cewa haba mama kiyi hakkuri da yar sister na ta dai kusa wucewa tabar maki dakin ki itama ta huta hakana kamar kowa.
Bai dade da fita ba sai ga yaro da rogo cike da zogala nan na zauna da kaina na shiga gyarawa hankali kwance kowa sai da yaci banda Amira da take ta faman fushi ita kadai.
Mukan sai faman hira muke da mama da su iyya da yar aikin mama din don mama bata dauke ta wata yar aiki ba can.
Ina basu labarin abubuwan mamaki da na gano a tafiyan mu da irin daulan da na gani a gidan Abu sifiyanu mai kudin duniya.
Duk sun natsu ina ta basu labarin irin daukakan da yaya sadauki ya samu a duniya ta wasan kwallo.
Tsukin Amira mukaji ta mike fuuu ta shige ciki cikin bacin rai dama kuma don ta kule ne nake kara bada labarin tunda na gane ita yar hassada ce a rayuwan ta.
Don maganan da tayi kan cikin dake jikina ya bata min rai dakewa kawai nayi kada mama ta fahince ni ta kara mata fada.
Baba ya aiko yana kirana nan na mike na saka gyale na nufi dakin shi nan na samay su zaune da mummy kusa dashi.
Na shiga da sallama na tare da gaishe shi yake cewa yanzu kubura take fada min cewa kun shigo ina barci nace takiraki mu gaisa.
Nace eh baba ance ka samu barci shine nace a barka tunda anan zamu wuni mun samay ku lafiya ko ?
Yaya karfin jikin naka kuma yace Alhamdullahi Fatima ai iyayyen ki gasu nan suna bani kulawa sosai wallahi.
Kinga ita wanan ma yanzu ta aje aikin ta don lalura na itace take min komai ita da hauwau.
Jiki kan naji sauki sai dai tafiyan da ban iya yi ne kawai har yanzu matsala koshi likita yace insha Allahu da sannu zan dan iya fara takawa.
Nace Allah ya nufa baba ya amsa da Ameen Fatima yaya maigidan naki kuna dai lafiya ko?
Nace lafiya muke baba ai tare ma muka shigo dashi ya tafi ys dawo ne yabar mu anan.
Fatima Allah yai maku albarka a rayuwan ku ina mai alfahari da kasancewar ki mata a gurin sadauki.
Don nasan wani abin tare da taimakon ki ne yake yin shi a rayuwan shi yasa Allahda Annabinsa sukace ku auri mataye na gari don ku sama ma diyan ku uwaye na gari a rayuwan su.
Ke alheri ce sosai Fatima a rayuaan dana wanda ina matukar alfahari da hakan ko yaushe kasancewan shi tare dashi yasa sadauki gaba daya ya sauya daga sadaukin da muka sani a baya.
Duk wani mumunan halaiyar shi yanzun yazama tarihi a gurin mu da bakece ya aura ba da sai dai muce Allah ya kyauta kawai.
Gashi natashi kudi suna shigo mai ta ko wani hanya may zai sashi tunanen gyara wani mugun halaiyar shi can na baya da basu da kyau da ai saidai kawai yaci gaba da gurbatacen rayuwan shi babu mai kwabon shi a kai.
Amma duk irin kokarin da kikeyi a kan shi ina da labarin komai a kunne na Fatima.
Allah dai yai maku albarka yasa ku gama da duniya nan lafiya yabaku zuria dayyaba masu maku biyayya kamar yadd kuke muna.
Na amsa cikin kunya da Amin baba na gods nima da kuka mai da rayuwana haka don kune silar komai da nake ciki a yanzu.
Yace kai haba dai Fatima ai mune dai da godiya a kanki yadda kikai muna biyayya haka yau gashi ya zama muna alheri ga baki dayan mu ko.
Haka dai nabar gurin baba yana ta saka muna albarka da fatan gamawa da duniya lafiya a rayuwan mu kamar yadda ko wani da ke bukatan addua ga mahaifan shi kullun.
Sai dare ya dawo ya kwashe mu muka bar gidan zuwa gidan mu cikin farin ciki a ran mu yadda iyayyen mijina suke zuka ma rayuwan mu albarka haka.

Muna hanya nake cewa ashe mummy tabar aikinta ne akan rashin lafiyan bab ?
Yace wallahi fa haka sagir ya fara fada min da kuma naje gun baba din shima yake fada min haka din.
Nace ai ko ta kyauta wallahi don haka shine zama tare yace ai zan duba akan al, amarin don asan abin da za, ai mata akan haka din.
Nace yaya bafa mummy ba kawai dukkan su sun bukatan taimako wallahi don alama ya nun sun a cikin wani hali wallahi ba dadi da ganin su.
Yace nima nai tunanen hakan amma banji kince komai ba shi yasa nai shiru nima.
Nace kai haba yaya nice kuma zanyi magana akan taimakon iyayyen mu yace bakece P A ba ke ce ya kamata ki tsara abinda ya dace a kan su ai.
Nan na shiga zaiyano mai abinda ya dace ai masu din don a taimakawa rayuwan su har muka kai gida kowa ya shiga part din shi don watsa ruwa ajikin mu ko zamuji dadin hakan.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: I'mIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH,,,,



Washegari aka hada lifaya, don taya murnan samun nasaran da sukayi akan wasan su da suka buga na kwallo.
Mun sha kwalliya sosai a lokacin in cikin wani dogon riga mai launin dark blue wanda yaji duwatsu a jikin shi sosai.
Nai rolling din kaina da dan kwalin shi wanda shima yana da duwatsu da aka jera mai a jikin bakin shi.
Ga zobunan gold sun cika min yatsu na dama duka hudu, daya sayo min wuyana saye da English gold.
Na saka wani takalma mai dan tudu akafana sai yar karamar jakar hannu dana rike.
Shigar tawa duk wanda ya ganni sai ya yaba da ita shi kan shi sadauki dana fito sai da ya kasa boyewa a ran shi ga kamshi dake tashi na jikina saboda mayukan danake amfani dasu a can yanzu.
Haka Amir shima yaji kwaliyan shi irin ta yara maza mai tsada sosai tare da saka mai hula irin ta yaran turawa.
Wayan shi ya dauko ya fara daukan mu hoto dashi, yana yaba kyawon mu ni da yaron.
A cikin wata irin dirkekiyar mota muke tafe dagani sai shi sai Amir wanda yake rike a hannun mahaifin shi yana waya.
Muna Isa gurin munga karamawan ban girma a gurin mutanen da muka samu suna jiran isowar mu gurin.
A gaskiya wanna mutane suna matukar girmama yan was an kwallon a rayuwan su.
Yana fitowa ya zagaya a bangaren da nake zaune ya bude min motar da kan shi yayin da idanuwan mutane yake a kan mu caaa.
Wasun su da yawa a gurin basu san cewa sadauki yana da aure ba don su ganin su a gurin su shekarun shi yai karami da aje iyali haka.
Hannun shi harde acikin nawa muka shiga babban holl din wanda yake makil da jinsin mutane kala kala.
Duk wanda yake da iyali acikin su tafe yake da iyalin shi a gurin.
Nan aka shiga gaisawa da mutane ana introducing din juna ga manyan masu kudin kasan turawa.
Inda matan dake gurin suka shiga kallon kalar shiga ta wanda ke baiyyana musulunci a fili.
Don haka aka shiga gimamani don suna matukar daraja matan musulmai sosai.
Ga wasu flowers da ake watsowa daga sama sai shagali suke suna shaye shayen su irin na al,adan su.
Nan sadauki suka hade da wani balarabe mai kudi dan kasan Dubai mutum ne mai tsananin arziki da tarin dukiya acikin nahiyar Arab side.
Gaba daya shine mutum na farko da yazo na daya a duk duniya arziki da tarin dukiya.
Gashi da ra,ayin son wasan kwallon kafa don matashi ne shima haka yasa ya kyasa taimakawa yan kwallo musanman matasa musulmai irin su sadauki.
Yana kuma da kamfani na kera gwala gwalai da diamond nashi na kanshi ga rijiyoyin mai da yake dasu kasa kasa na duniya.
Yana da kamfanin kera jiragen sama da na ruwa wanda yake mallakan shi na kansa.
Hannu Abu sufiyanu ya mika ya karbi Amir dake a hannu na ya dan yi mashi wasa tare da sumbatar yaron.
Cikin wasa yake cewa sadauki ya bashi Amir don yaron ya shiga ranshi.
Sadauki yake cewa ya bashi yace ya gode tare da kissing din yaron inda ya juya gurin na hannun daman shi yai mai magana.
Mutum ya amsa da insha Allah.
Nan yaja hannun sadauki wanda nake biye a bayan shi sun dan jima suna magana irin ta Siri a tsakanin su.
Wanda ashe alakace ta business suke kullawa a tsakanin su a lokacin, mutane da yawa sun San ba kebewar banza Abu sufiyanu yake da sadauki ba a lokacin.
Da hannu ya yafito na nufin na karaso inda suke a tsaye, yake ce min nai wa mutumin godiya.
Duk da ban San ko na may ye ba amma nai mashi godiya irin ta addinin musulunci wanda ya kara sawa mutumin jin dadi a ran shi.
Don shi mutum ne wanda yake son mutane masu yi mashi godiya da nuna farin cikin su gare shi.
Nan dai sukai ta gaisawa da mutanen arziki na duniya kala kala ina rike a hannun shi har taro ya fara watsewa.
Muka Fara ficewa daga sahun farko muka bar gurin don a lokacin a gajiye nake sosai ga Amir da nauyi ba kadan ba.
Muna a mota ya dan sasauta tie din wuyan shi yana juyowa inda nake zaune yana cewa my queen kin gaji ko don nasan baki saba irin wanna kwaram din namu ba ke.
Idanuwana na Dan lumshe nake cewa nauyin daukan wanan din dai ya isheni .
Yace Kai ni dake son na samu ma yafi haka girma idan son samu ne a gurina.
Nace kai Yaya idan Amir yafi haka kiba kuma ai sai dai na dinga barin shi a zaune guri daya don ina zan iya daukan wanda yafi wanna girma haka.
Yanzun ma a Yaya nake iya daukan shi balle ya kara yafi nan kuma ?
Ya dan juyo a mamaki yace Queen baban nawa zaki bari a zaune don tsaban mugunta kuma ?
Nace ai nima babana ne ko ko kamanta nima shi ya haife ni ne wai ?
Nace sune fa gata yanzu a duniya don sune sillar wanna rayuwan da nake a ciki yanzu.
Murmushi yayi don jin abinda na fada yasan ba karya na fadin ba haka zancen yake ko yaushe Ina matukar godewa mama da baba din.
Yace tare da kwantar da kanshi saman kafada ta nauyin ya karu min biyu wanda a lokacin ba nauyi naji ba sai wani sanyin dadi da naji a raina kawai.
Don farin cikina yanzu karuwa yake a kullun Ina mai godewa Allah na da biyayyan da yabani iko nai wa Maji ban butulce mata ba ga bukatan ta a gare ni na auren dan ta da duniya kewa kallon lalatace.
Matsalata daya yanzu shine ban gama tantace ko sadauki ya daina halin shi ba ko yanayi har yanzu.
Haka ne yakan rage min jin dadina a kullun na tuna da wanna rayuwan nashi na shaye shaye.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login