Showing 318001 words to 321000 words out of 373688 words
Chapter 107 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
an saka mai man shanu shi na danci kadan still ina jin tashin zuciya har lokacin.
Nan mama take tambayana yaya za,ayi da kayan da mukazo dashi nace a fitar wa Baba na da nasu sai su raba sauran amma sabulu da clean abawa makwabtan su.
Yadda nace haka mamana tai rabo na adalci don har na Baba na yafi yawa sai da nazo nagani nace a,a daidai za,a raba ita dashi.
Mutanen da aka kai ma tsaraba sukai tashigo yi muna sannu da zuwa naji dadin yadda mutane sukai ta nuna min karamci haka.
Ice dake gidan mama a karkashin shi muka mayar gurin zaman mu ni da iya sai dare muke shiga daki don rana haka na wuni kwance rijib ba lafiya.
Iya ta matsa wai na fadawa maigida banda lafiya asan abin yi nace mata haka nakeyi dama idan nai tafiya.
Sai mama ne da iya dake taya ta aiki suke ta faman kai kawo a tsakar gida kawuna yazo amsa kiran mamana da ta aika tana neman shi.
Nan suka kebe tai mashi bayanin komai kuma ta kawo kudin aikin ta damka mashi don shi a garin yake zaune dama gurin shi tazo har mijinta ya ganta ya aureta.
Sun gana da maigidan mama da kawu yace aiba matsala wanan taimako ne ai akai mashi da yamma kuwa sai ga masu aiki sun shigo gidan suka fara awon yadda za,a fitar da plan din ginan.
Dakuna guda biyu na mama ciki da falo dayan kuma single ne sai wasu biyu a gefe daya su ma sai na samari washe gari yan aiki suka fara aiki akan idona akafara komai ga katan aiki kawu har ya sawo an fara aiyuka ko.
Da dare daga ni sai mama na a daki Iyya na waje kwance wai zafi take ji.
Nace mama dama ina son mu samu lokaci in fada maki wani magani da aka anso muna naba yaya yasha wanda ina gani shine sanadin barin shan abin maye da yakeyi.
Nan dai nai mata bayani da kuma garin don ba nisa tace tagane mutumin ai dan uwan mahaifina ne tace insha Allahu zatayi kokari taje gurin shi.
Muna cikin hirane yaya sadauki ya kirani muka gaisa yana jin murya na yace Fatima na amsa may ke damun ki nace may kagani ne yace you sound like baki da lafiya na kakaro murmushi nace daga barci na tashi yanzu barci na somayi kata dani.
Ina ganin bai yarda ba sai naji yace humm kawai yace ina mama nace gata tare dani barin bata ku gaisa dama tana son maka godiya.
Yace No No godiyan may kuma don nayi wa mamana alheri haba kada ma ki bata idan hakane kice ina gaida ita nace to ya kashe wayan.
Koda ya kashe wayan hankalin shi bai kwanta ba yadda yaji muryana sai hankalin shi yai matukar tashi.
Amma kuma baida yadda zaiyi tunda nace mai lafiya nake da ance sokoto nake da ya zo gobe gobe taga yanayin da nake ciki.
Dole jiki ya matsa min ban samu tafiya ba ranan da muka ce zamu tafi sai da dare ya samu time ya bugo min waya yana tambayana mun sauka lafiya da kyat nake magana don da zazzabi na wuni.
Yake tambayana ko mun sauka lafiya yaya baba nace cikin karfin hali ban samu wucewa ba yau yaya.
Ya rage fara,anshi yana tambayan saboda may nai mai shiru yace baki da lafiya ko Fatima ?
Shine kika shige kauye kika zauna da ciwo yana cin ki ajiki haka.
Watau ke kin samu su mama kin manta da lafiyan ki ko ?
Na rasa abinda zance sai da ya kara tambayana may ke damun ki ne ma wai ?
Na rasa abinda zance mai sai can nace zazzabine amma naji sauki shine mama tace na bari sai gobe mu tafi idan na kara jin sauki.
Yace a zaune zaki ji sauki bakiga likita ba ko may nace nasha magani ai na samu sauki yace ina Iyya take ne wai nace tafita.
Yace gobe goben nan ki koma sokoto zan ma bashar magana yazo ya kaiki asibiti idan kun isa kafin na iso.
Gabana yai matukar faduwa gashi banje gurin babana ba kuma yasan munzo.
Na marairaice nace don Allah yaya kayi hakkuri naje gurin baba nai kwana daya jibi sai na karasa gida.
Bai jira may zance ba ya katse layin bayan dan tsokin da yaja.
Mama dake zaune gefe na takale ni a tsorace tace so yake ki koma gida baki isa can ba ?
Na bata fuska tare da jan tsuki nace wai haka yake nufi ni kuma ba zan koma ba banje gurin baba tunda ba bari yake nazo ba.
Tace a,a yar baba kirashi ki roke shi idan ya yarda sai ki karasa gurin su idan kuma yace lalai sai ki koma gobe din sai ku shirya ku koma din.
Na dai daga wayan badon naso ba ga mama ta tsareni da ido na kirashi na zaci ba zai daga wayan ba dana kira.
Amma sai naga ya dauka yace yaya akayi kuma ?
A hankali na ce mai kayi hakkuri yaya don Allah naje gurin baba gobe nai kwana daya sai na dawo kada yace ko gudun shi na soma yi na rike uwata.
Yace as you wish ai jikin ki ne nace kadai yi hakkuri please gobe da safe zamu karasa can mu kwana da safe sai mu taso.
Yace na fada maki da kun kwana daya ki dawo gida kije asibiti aduba lafiyan ki nace insha Allahu jibi da safe zamu taso da yarda ubangiji.
Yace is ok Allah ya sauwaka nace nagode muka kashe wayan mama tace ai kinga haka yafi da ran shi ya baci yakawo ki cikin dadin rai kuma akoma ana haka baiyi ba gaskiya.
Nai mamaki irin tsaraban da mama ta hada muna mu tafi dashi wai kaji, man shanu fura da nono kwakwamayti kuka daddawa da kuli kuli da kwanzabbi mai yawa.
Mijin mama ma yabani mamaki rago yasa akayanka aka,soya shi sai da ya cika bucket din penti yace nashi tsaraban ke na da mazzakwaila mai yawa.
Tun da safe mukai masu sallama na wuto da kauna ta Sa,ade muka bar Asma,u tana kuka nai mata alkawari itama zan dawo in dauke ta ai tai makaranta haka yasa tai shiru.
Sai kauyen mu nan na samu baba bai gida da farko kamar mama tabawa bazata karbe mu ba amma tana ganin an fara jido kaya ana shigowa dashi tafara washe bakin ta tana cewa sai yau Hjy maryam tun fa shekaran jiya akace muna kina Rabah.
Nai dariya nace wallahi mama munje daniyar nai kwana biyu nazo nan nakarasa kwana uku sai ga ciwo ya rike ni acan.
Tace assha subahanallahi inji da sauki dai ko nace naji sauki mama.
Nan muka basu tsaranan su na aika,wa kakanina da nasu sukai ta godiya.
Da baba yadawo shima na bashi nashi sakon yai ta saka albarka kwanan mu daya tunda safe muka kama hanya sai sokoto.
Rijibb na iso garin na kwanta bamu jima dashigowa ba wayan yaya ya shigo yana cewa yaya kun taso ko nace gani dakina kwance yace ki shirya bashar yazo yanzu kuje asibiti.
Ba adade ba bashar yazo muka wuce asibiti ganin likita duk a lokacin na jigaye na wahala sosai.
****** ********* ******
A gurin da zanga likita ma sai dana dan kwanta kafin shiga ya kawo kaina banda kuzari sai yawan jin kasala dake damuna ko ruwa nasha sai na fitar dashi san nan naji shakat a raina.
Nan yakira wayana nace gamu asibiti muna jiran layi yazo kan mu ne.
Yace wai may ke damun ki ne Fatima haka ?
Na lumshe idanuwa na nace ban sanni ba yaya komai naci dai sai na amaye shi kuma banjin kuzari a jikina ina dai ganin maleria ne yai min yawa a jikina.
Yace bari a shiga gurin likita muji may ke damun ki haka kilama ruwan kauyen ku ne bai karbe ki ba kike wanan wahala haka ?
Mun shiga gurin likita yai min yan tambayoyi irin nasu ina bashi amsa can dai yajefo min tambaya yaushe rabona da period ne ?
Gabana ya fadi sai lokacin na tuna zancen wani period can nace gaskiya ina ganin kamar yakai kusan three month yanzu sai dai koda nake gida ai nakan yi irin haka din.
Test akai min cikine dani har wata uku da kwana takwas nan dai suka rubuta min magani tare da,son na samu hutu don nayi weak da yawa.
Kunyane ya rufe ni da akewa yaya bashar din bayani tun nan yaya bashar yake min congrats.
Muna fitowa wayan sadauki na shigo mashi yace wai may ake cikine kunga likitan.
Yace eh mungan shi gashi mun fito zan da tsaya na sai mata magani ne mu koma gida.
Yace may sukace yake damun ta yace may ko zasuce banda cutar daka zubawa yar mutane mugu kawai.
Gaban sadauki ya fadi shidai yasan baida wani cuta a tare dashi asalima shiba mane min mata bane balle.
Yace for god sake may ya samu fatima din Bashar wani cuta ke gare ni da zan zubawa Fatima shi ?
Yace kaiko keda cuta gatan kana kayan shi cikin wando kullun kana durawa yar mutane wahala.
Nan yake ta tsokanar shi har yagane ciki yake nufi ke gare ni yace don Allah da gaske kake yi ko shirmay ka bashar ?
Lokacin yake shigowa mota yake ce min karbi wayan maryam ki fada mai da kanki tunda ni ya mayar dani makaryaci yanzu.
Kuma ka shirya tukwaici na wallahi don wanan ba karamin albishir bane nai maka.
Yamiko min wayan yace ga fitinanen mijinki kiyi mashi bayani da kanki ko zai yarda murmushi kawai nayi mashi.
Na dauki wayan cikin sanyin murya nake cewa hello yaya.
Bai amsa ba sai cewa yayi wai wanan munafikin maganar gaskita yake fada min ko wasa yakeyi nace uhumm kawai tare da murmushi na mikawa yaya bashar wayan shi.
Nan sukaci gaba do zolayan kan su har muka isa gida yaiwa iya bayani kan ance ana son in samu hutu sosai don haka kada ta bari inyi aikin komai please.
Barci ne ya dauke ni mai nauyi ban falka ba sai misalin karfe takwas na dare koshi amai din ne ya tayar dani a lokacin.
Sai dana natsu na jawo wayana kirane ciki barkatai na mutane nashi yafi yawa amma.
Ban kirashi ba don yanzu ko hayani kwarai ban so sosai na shiga whastff nan naga yayi posting din suraitai barkatai na farin ciki.
Ban dade ba nafita na kwanta sai ga Iyya tashigo dakin take min yaya jiki nace mata naji sauki sosai.
Tai min tayin abinci nace tea nake so na ruwan liptop kawai ba madara ba sugar tace ikon Allah shi ta hado min na zuba zuma ciki dan kadan nasha shine har naji dan dadin bakina nai sallah na kara kwantawa.
Da safe kiran mama ne ya tayar dani daga barcin tace Fatima ashe kin dawo kuma ba lafiya nai dan muushi nace wallahi mama.
To yaya jikin da sauki yanzu ko nace naji sauki sosai mama tace shima yace insha Allahu yau zai dawo zuwa yamma don yana abuja babu jirgin safe yau.
Nace Allah yakawo shi lafita tace amin ki kula da kanki kinji Fatima Allah ya inganta banyi magana ba don kunya.
Falo na fito na samu Iyya da Saade azaune suka gaishe ni tare da min Allah ya sauwaka.
Can nace Iyya afito da tsaraban nan kiraba abawa mutane nasu tace to nace man shanu da nama akai wasu mama shi idan kin dibi naki tunda munan akwai nama su zai masu a.fani suna da yawa can nasa ta diban ma anty maryam nata da Inna mama bashar kwai nace akaiwa mummy ta soyawa yaran ta.
Yadda nace haka iya tayi kayan miyane kawai tabar muna don muna da bukatan su sosai.
Iyya ce da kanta takaiwa kowa nashi mama tai matukar jin dadin yadda nayi don Iyya ta labarta mata komai kwai danace akawo wa yaran mummy da kwakwamayti ya matukar burgeta har mummy din suka ce suma suna nan shigowa su gaidani.
Nan mama ta debarwa ko wani daki ta aika masu tana fadin ga tsaraban Fatima nan da ta dawo dashi suka karba suna gyatsire fuska kuma suka shiga ci.
****** ********* ******
Bayan sallah azahar mama da mummy suka shigo tun a kofa mummy take fadin ina yake tun bai fito ba na kwali kan na yana wahalar min da yarinyana haka ?
Kunya naji sosai na dan dukar da kaina,a kwance suka samay ni saman dogon kujera na mike da kyat muka gaisa dasu nan mummy take fadin tun da dare sadauki yakirani yake fada min ai ban san lokacin da nai ihu ba har Alhaji saida yafito.
Mama tace kai in ma ba abin kurciya ba yaya mutum zaiyi ciki har wata uku ba,a sani ba tun fa tafiyan su ke nan ta dawo da cikin nan amma haukan shi bai bari ya sani ba.
Taron dai kurciyane hajiya inbashi ba ai ko ita zata gane tana da ciki a jikin ta ma kawai dai duk kan su kurciya yana cin su ne.
Mummy tace mazajen ki na gaishe ki sunce sunga tsaraba sun gode sunace suna murna wai yayan su ya samu baby Banan da haukan ta wai nazo da ita ta dauki baby.
Murmushi nayi nace lah mummy shine baku zo min da ita ba tace ban iya kiriniyan ta barta can suzo idan yayan su yadawo yakai su yawo ai yasaba da kwaram din su shi.
Mama tace a,a Sa,adatu din ke nan ai ni dani kuka ba ita ta debe min kewan ku wallahi gata kamar ku daya wallahi nace mama ai munfi kama ko da Asmau sosai idan kingata kaman mu yayi yawa tana can mun barta tana kuka wai ita ma sai tazo mukai mata wayo nace zanzo na dauke ta daga baya yanzun ba wuri.
Amma ko Fatima baki kyauta ba kikabar min Asmaun nawa kaunata ce ina ji da ita duk cikin kanne na wallahi.
Bari ya dawo ai zan sashi ya tura azo min da ita tunda ku baku son zama da ita nan.
Naji dadin jin haka kuma haka nake so don ina son yaran su fito suyi karatu itama mama ta dan huta yawan iyali.
Idan kuma ta zauna gurin mama zata sha dadi sosai a gurin ta don mama uwace bata fada ba.
Basu wani dade ba sukai muna sallama suka tafi akabarni da Iyya da Sa,ade a gida musa ya fita abin shi.
Sai da dare ya shigo garin ina,falo kwance na dunkule yashigo gidan Sa,ade naji tana mashi sannu da zuwa don tare muke zaune Iyya tana kitchen.
Yashigo idanuwan shi na akaina har ya karo inda nake kwance ina kokarin mikewa zaune daga kwancen da nake.
Yace No don Alla kwanta abinki yazo ya zauna bakin kujeran da nake kwance haka yasa Sa,ade mikewa ta nufi kitchen gurin iya tana fada mata dawowan shi.
Ya dan kai hannu shi a saman wuyana yana tabawa a hankali yaji ba zafi sosai yace how the you feel now ?
Nace a hankali da sauki ya daga hannuwana ya rike a cikin nashi gama yace I dont know what to say but nagode Fatima na gode kwarai da wanan babban kyauta da kikai min.
Na lumshe idanuwa na a hankali tare da kwantar da kaina ga jikin shi nace yaya I miss you.
Yai dan murmushi ya shafi fuskana yace kina hakan da fa fushi nake dake da kikaje kika zauna da ciwo a kauye kamar wacce bata san zafin kanta ba.
Amma yanzu kin wanke kanki ko gare ni komai ya,wuce ko yake cewa yanzun may kike ji kuma ne wai ?
Nace ba komai yaya bandai jin karfin jikina ne kawai sosai kamar farko yace ina zakiji dadin jikin ki kina haka Allah dai ya rabaku lafiya kawai.
Wanka ya,shiga yafito ya dawo falo inda muke don ni na kasa tashi ma,a lokacin sabada jiri dana ke ji.
Da dare ma dai haka muka kwana dole washe gari aka sa min ruwa don amai yai min yawa sosai.
Wani irin ciki ne wanan kuma bai bani wahala ba da farko sai yanzu gashi yana son kawo min cikas ga karatuna.
Haka nake daurewa na je lectures na dawo gida a,wahalce yau ciwo gobe lafiya.
****** ********* ******
Wasa wasa baba sani ya saka sadauki a gaba da zancen Rahama duk da mama tace bata yarda ba ita.
Ido da ido sukayi da baba Sani take fada mashi indai ita ta haifi sadauki wallahi ba,a auren nan sai dai in bayan ranta za,ayi shi.
Tace yanzu kasan suna da zumunci kamanta lokacin da kaiwa mutane cin mutunci kace dan shaye shaye ne shi baka aura mashi yar ka naje cikin dangina na nema mashi.
To na nema mashi din kuma yanzun sai hassada da kyashi ya biyo baya nace ba ayin auren idan kuma ka isa sai ayi mu gani.
Yace ke wallahi hauwa baki isa ki raba muna zumuncin ba sai dai ki mutu amma sai anyi wanan auren muddin ina