Showing 363001 words to 366000 words out of 373688 words

Chapter 122 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

yan iska su cika min gida shiyasa ita bata tafi ba.
Karshe kuma sai ga zancen auren Nafisa da Raiha da taji Allah ya hadasu da wasu manya sai dai ba yara bane su.
Nan kuma ta shiga zage zage kamar mahaukaciya wai ta yarda ni yar bakin cikine ta karshe sosai don ban son ta da arziki nafi bukatan komai sai a gani a gurina kawai.

****** ********* ******
Bukin anty Amira ya taso sosai ba kama hannun yaro don haka muke ta zirga zirga ba hutu don mu ke gudanar da komai akan bukin duk da gwatsale ni da takeyi tana nuna bata bukatan saka hannuna acikin al, amarinta sam.
Hakan bai sa na daina duk wani abinda nake da niyar yi ba don ba don itace nakeyi ba dama don Allah nakeyi da mijina da kuma mahaifan su.
Bata san ina da rana a gare ta ba sai da masu zuwa ganin dakin da za, a saka mata kaya sukaje suka dawo da labari mara dadi don ashe a family house za, a aje ta.
Kuma ga dakunan ba wasu dakuna bane maigirma a jere suke ita da uwargidan ta wace yar uwace ga mutumin da zata aura.
Da labarin yazo ba karamin tayar da hankalin ta tayi ba sosai nan ta tuburewa mutane akan Ibrahim ya cuce ta don cewa yayi gida zai kama mata haya don may yazu zaice a gidan su zai aje ta.
Sosai ta tayar da hankalinta akan bazatayi auren ba ta fasa hankalin mama yai matukar tashi gashi an gama komai akan shirin buki ga yan uwa na nesa har sun fara hallara a gurin bukin.
Kuka wiwi takeyi akan ita kan wallahi ta fasa sai dai akai wata ba ita ba don bazata wanan gidan da ake bada labarin shi ba babu tsari.
Mama kuma da yan uwa sun kafe kan lalai sai anyi auren nan sai dai ta mutu idan an kaita don bazata basu kunya ba.
Ganin matsalan yai yawa ga tashin hankali ga fuskan kowa idan ka duba ya sa na tashi daga inda nake zaune lokacin cikina yai girma sosai wata bakwai saura kwana goma nake.
Dakin da take na shiga na samay ta ta kifa kai ga filo ita kadai a cikin dakin tayi buji buji da ita kanta duk a hargitse dashi.
Zama nayi bakin gadon don bazan iya tsayi tsaye ba a yadda nake lokacin don karfi hali kawai nakeyi da kaina.
Duk da taji anshigo dakin bai sa ta dago daga yadda take a kwance ba cikin yanayin tashin hankali.
Cikin yar siriryar murya nace Anty Amira ki tashi muyi magana musan mafita akan wanan al, amarin don kuka ba shine mafita yanzu tunda kinga mama ta kafe akan sai anyi auren nan ba fashi.
Jin muryana yasa ta dago kai a cikin fushi tace Bintu for god sake ki barni naji da abinda ya damay ni please ke har wani taimako zaki iya yi min ?
Wani matsayi ke gare ki da har zaki dauka zaki iya taimaka min dashi a matsayinki ko don kawai kinga kina auren dan uwana kina juya shi yadda kike so to ni ba shi bane ko maji ki sani.
Murmushi nayi kawai nasan ban taba fari a gurin ta amma ni don Allah kawai nai niyar taimaka mata.
Nace a fili ba matsala anty ni don Allah nazo gurin ki don mu san mafita kawai idan kina da lokaci ki tashi muyi magana dake mu san abinyi tun ba, a kai maki kayan ki ba a wancan gidan yawan.
Wani kallo ta watso min kafin tace ina sauraren ki nace nagode naci gaba da fadin nasan bawai baki son Ibrahim bane a yadda nasan kun dade tare dashi kuna soyayya.
Kawai dai wanan matsalace ta gurin zama yasaki bacin rai irin haka sai nake gani idan yace zai canza maki gurin zama duk wanan matsalan zai iya wuce a tsakanin ku tunda soyayya ce ta hada ku ba kiyayya ba.
May kike fadi mutumin da ya kafe akan shi baida kudin da zai karasa ginan shi kuma baida wanda zai iya kama min hayan irin gidan da nake so a yanzu.
Nace insha Allahu anty idan don gurin zamane na rokeki Allah ki kwantar da hankalinki ayi wanan bukin cikin farinciki.
Yadda kowa yazo lafiya don farin ciki ya koma gida da farinciki a ranshi anty baku gaji yin kunya ba a rayuwan ku balle kuji kunya don Allah ni dai yanzu abinda nake so shine ki kwantar da hankalinki ki koma kamar babu abinda ya faru a baya don marasa da suyi kunya don yanzu kinga ido aka sakawa mama aga yaya zata kaya ana farin ciki zaki shiga gida mai kuntatawa.
Wani kallone takara watso min tare da cewa wanan shine dama maganan da zaki fada min din.
Nace eh anty don Allah tunda kuna son juna da Ibrahim kiyi hakkuri ki daure ayi wanan abin cikin rufin asiri insha Allahu bazaki zauna a wanan gidan ba.
Tsuki taja tare da marya da kanta a saman filo tace na zaci wani shawaran arziki kikazo min dashi har na bata lokacina a kanki haka.
Na dade a zaune ba tare da tajuyo gare ni ba ga wayan ta dake ta verviration taki dagawa.
Wanda nasan ba kowane ke kiranta ba a lokacin sai angwan ta wanda yake a cikin tashin hankalin kan cewan da tayi bazatayi auren ba ta fasa.
Nagaji da zama ina batun tashi anty maryam ta shigo dakin kallon mamaki tai min ganina da tayi a zaune ga maidakin ma kamar bata san ina zaune a gurin ba.
Tace ke kuma may kikeyi anan ina can ina neman ki mama tace wai wanan kayan kitchen din da aka fitar a mayar dasu a kwali tunda babu inda za, a saka su a gidan.
Tajuyo cikin zafin rai daga inda take a kwance idanuwan ta sunyi ja jajir dasu don kukan da tasha sosai.
Tace sai naga iban da akewa shirin auren da har ake maganan rage wasu kayan daki can akai badai ni ba.
Nikan da kyat na mike tsaye muka fita maryam tana mata dariyar mumuke muka fice.
A gajiye na bar gidan don dare yayi a lokacin yaya Sagir ne ya kaimu gida da kan shi don ban driving saboda matsalan cikin dake jikina.
Sai da nai wanka nafito falo na samu Iyya tana gyaran abin da zamu karya dashi tana kwaba abin da zatai muna sanasir dashi.
Ina zama ana kirana ga waya yaya sadauki ne wanda bai ma kasan yai tafiya a lokacin.
Mun gaisa yake tambayana ko mun dawo gida ko muna can gidan su mama har lokacin .
Nace mun dawo tun dazun har munyi wanka gani a falo ma zaune zan sha magani na kwanta.
Yace maji ta kirani tana fada min iskancin da wanan mara hankalin kewa mutane tun jiya wai ta fasa auren ko ?
Nace yaya bafa fasawa tayi ba kune dai baku fahince ta ba bawai bata son Ibrahim bane a, a gidan da za, a kaita ne bai bata ba don a cikin family house din su ne inda uwargidan shi take zaune.
Kaga kasan halin anty Amira da tsandan mutane bata son yawan hayani ita tafi son ta zauna koda yaushe silent bata son yawan hayaniya.
Ya karba kafin naci gaba da fadin don taita mugun hali ko?
Nace haba yaya ya kamata a taimakawa anty please bai kamata abar rayuwan ta a haka ba don Allah.
Yace ok yanzi so kike nima na biyewa haukan ta nace a fasa auren taita zaman gida ko?
Nace ba nufina ke nan ba yaya abinda nike nufi shine ka taimaka da baiwan da Allah yai ma na falala ka sama mata inda zata zauna don wanan auren nata yai karko kamar na kowa please ?
Ban fahince ki ba Fatima kima nifin nine zan bada gurin da Amira zata zauna da mijin ta ko may ?
Nace ai ba mijin ka zakaiwa ba yar uwar haihuwan ka zaka taimaka kamar yadda Allah ya taimake ka kaima ka sama mata gurin zama yadda take so.
Don yin haka kawai shine shedan dan uwata ya samu kuma mai taimako ne ga jinin shi don kaga ba Amira ba kawai wallahi har mama hankalinta a tashe yake akan wanan magana daurewa kawai mama keyi don ta bata karfin gwiwa amma ran mama baiyi dadi ba ace a wanan gidan za, a kai Amira gaskiya.
Yanzun dai na fahince ki yace nine zan aurar da ita kuma na bata gurin da zata zauna kamar na matsu da ita a gida ko ?
Nace wallahi yaya ba haka nake nufi ba ni nufi na shine kawai ka taimakawa rayuwan su tunda Allah ya hore ma abinda zaka iya yin haka din.
Idan kai haka ba karamin lada zaka samu ba har a gurin Allah don shine shedar zumunci yanzun fa kaine uwar mu kaine uban mu gaba dayan mu har kai.
Amira ba ko Nafisa ce da irin wanan matsala din zaka iya taimaka mata idan kaso saboda Allah.
Ji nayi ya katse layin tare da jan guntun tsoki haka yasa banji dadi ba a raina nasan bai yarda da shawaran da nake gani shine a matsayin mafita ba ni.
Bayan mun gama waya nasha magani na mun dan taba hira da Iyya akan zencen tana fadin ahi yasa ba, a son mutum ya faye bakin hali wallahi don karshen shi baya kyau.
Yanzu ga irin ta nan ai tace ita tafi kowa bata ganin kowa da daraja kamar ba mamace ta haife ta ba tafita daban a cikin yan uwa.
Nace Iyya kin san kowa da kalar halin shi ita nata rayuwan ke nan haka Allah yayi ta daban.
Ai ba za, a biye mata ba idan ana son auren yai karko sai a taimaka mata anyiwa banza ma balle ita.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,


IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA IDAN KINYI HAKA MUN BARKI GA ALLAH.


Alheri sosai ya tanadarwa su Mama da Umma da mummy har motar shiga sai da ya canza masu tare da gyara masu dakunan su tsab.
Wanan ya zamo karo na farko da sukaji dadi a ransu abinda taya sadauki yake masu na alheri wanda hassada baya bari suga irin alherin da yake masu abaya.
Yanzun ko abu yakai babu gare su duk yadda mutum yai masu alheri komai kankantan shi suna godiya sosai.
Don yanzu wanda suke samu gurin shi watau baba shima ta kanshi yake yi baida komai duk diyan su sun wawashe mai shago baida wani abin hannun shi kuma inba gonan da sadauki ya saya mai ba farkon fitan shi wasan kwallo da yafara zuwa.
A takure suke komai da suka fi karfi a baya yana basu sha, awa yanzu shi yasa suke ganin wanan kyautan na baya yazo masu kamar kyauta na farko da ya taba masu.
Har daki mama Asiya ta samu mama tana mata godiya wanda mama ma a lokacin bata san da wanan alherin ba inba yanzu da mama Asiya tashigo mata da zancen ba.
Mama tace ikon Allah wallahi yaya banda labarin wanan zancen yanzun ma nake jin shi a gurin ki.
Godiya dai ta karayiwa maji tare da fatan alheri tana ta saka albarka wanda maji ke gani yau kamar a mafalki.
Mama Asiya ce sakawa dan ta albarka haka akan alherin da yai mata don jin dadin zuciyar ta.
Mama Asiya tana fita har tsakar gida tana godiya Nafisa ta gamu da ita dakin su tashiga gurin mahaifiyarta tana cewa kina nan zaune halan may ya faru naga mama tana ta godiya a waje tafito dakin maji.
Umma tace nasan taje godiya ne godiya akan may kuma Umma ?
Tace yanzu Sagir ya samay mu da kyautan alherin da yayan ku dan kwallo ya aiko muna dashi mu uku motace ya sake muna da kujerun daki da gadaje sai kudi wai mu saka mai a mota da kayan abinci.
Nafisa tace tirkasa amma ko Allah ya saka mai da alheri wallahi to umma shine kike zaune ke baki zuwa kiy godiya?
Koda yake yadda naji kina magana kamar har yanzu kin saura hassadan abinda yafi karfin ki fada.
Dadai kin sakawa ranki ruwan sayi kibi kici arziki dayafi maki wanan hassadan da kukeyi shekara da shekaru yaki kare.
Ga yar uwar munafuncinki ta sulala taje tayi godiya tabarki nan kina hassada ga banza.
Kallon takaici taiwa yar tata da suke dauka a matsayin mara hankali ga maganan ta da dabiun ta amma kuma gaskiya ai Nafisa ta fada mata don tasan mama Asiya yanzu tana zare jikin ta tana hurda da al, amarin maji da yayanta.
Nafisa kan dakin ta tashige takwanta abinta yanzun ta daina sha sai dai bata bar harkan bazan ta ba da ta saba.
Sagir ya shigo ya samu umma zaune tayi tagumi ganin shi ya dan sata sake jikin ta tana mashi tayin abinci.
Yace Umma na fada maki yanzu a gidan yaya sadauki muke karyawa ni da Abdul komai dare sai Fatima ta kira mu muzo muci abincin mu yana aje haka ma dasafe.
Umma taji wani iri a ranta ba dadi tasan cewa ko ba komai anyi hadin zumunta a gurin kafin takai karshen tunanen ta taji muryan shi yana cewa.
Wai ko Umma kin san wani abu fatima fa tai muna kanfen gurin yaya ga sabon gurin aikin da za, a bude a abuja nasu.
Shi da kanshi yaya sadauki din ke fada muna cewa wai yar uwar mu ta nuna son kai ta matsa ita sai dai muma a nema muna babban gurbi a can mu kama aiki dasu ko kuma wanda ke nan sokoto.
Umma wallahi yadda suke gwada muna halarci irin haka ni abin ma har kunya yake bani yadda a baya mukai ta gwada masu kiyayya a filin Allah .
Amma sai gashi yanzu da ya samu mune na farko samun alherin shi harda mota fa yace zai saya muna wallahi.
Bamu kadai ba har dasu yaya Imiran naji ana magana a kansu suma za, a basu appointment a gurin.
Tace kai amma ko da ya kyauta muna wallahi don zaman banzan nan na Imiran ya fara ista wallahi.
Umma yanzun dai jekiyi naki godiyan kafin wani lokaci kuma kin san irin wanan alherin na bazata shi ake kira da kyautan dan aljanna.
Kyantan da zaizowa bawa a lokacin da bawa yake a bukace da wani abu a rayuwan shi dubi fa wa yan nan kujerun yadda suka koma kamar tsunma ni har kunyan nake jin azo agansu a dakin nan haka wallahi.
Bai bar dakin ba sai da yaga Umma ta mike yaga ta nufi dakin maji hankalin shi ya kwanta.
Don bai zai yuyuba ana masu alheri irin haka amma ace su har yanzu basu daina hassadan su ba da sukeyi.

****** ********* ******
Allah mai iko a yanzu ankai duk inda sadauki ya sa kafan shi yana tare da manyan body guard masu tsaron lafiyan shi dana iyalan shi wanda goverment da kansu suka bashi su don tsaron lafiyan shi.
Saboda gashi karamin matashi amma yana daya daga cikin manya masu shigo da manyan ababen amfani daga kasashen duniya.
Haka yasa ya zamo abin kula sosai a gurin manya na kasa da suke fada aji.
Saboda ya zamo daya daga cikin yan kasa masu kishin kasan su don sun cigaban matasa.
Gashi akan kamfanin da suke son kafawa har guda biyu na mai dana manyan jiragen ruwa da zasu dinga shigo da kaya daga waje.
Ga manyan injima na haska wutan lantarki da za, a shigo dasu kasa don amfanin kamfanonin da za, a gina nan n
Nageria.
Ban fita sosai zuwa yanzu don cikina da yai matukar girma don ko a wanan ma likitoci sun kara bani bedrest sai dai ba kaman wancan na baya ba danayi na Amir din.
Ina kwance saman dogon kujera a falo na dan mike kafafuna na da sukai min nauyi.
Yashigo gidan a gajiye dashi su Sagir suna take mai baya shi da Abdul dauke da dan briefcase din takardun shi da laptop dinshi a cikin case din.
Ya zauna yana cewa kai nagaji da yawa wallahi nazaci a nan idan na dawo ko zan huta amma gashi duk ba wani hutu da mutum ya samu tare dashi.
Na dan lumshe idona tare da kokarin mikewa zaune don na karbi case din zuwa dakin shi.
Yace da sauri No No kwanta abinki ki huta barshi idan zan shiga zan shiga dashi ai.
Bayan ya karasa kaiwa zaune ne yake cewa duk rashin samun hutu ya saka har kirjina yana min ciwo wallahi.
Da sauri na dago ina kallon shi nace amma gaskiya tunda ka fara jin haka ya kamata ka samu hutu ka zauna a gida koda na kwana biyu da zaifi ma.
Yace na kwana daya dai Fatima kwana biyu yai min yawa ga mu da tulin aiki mai yawa a gaban mu.
Idan ba naga angama gina muna komai ba hankalina bazai taba kwanciya


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login