Showing 87001 words to 90000 words out of 373688 words

Chapter 30 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

kawai su ma mikewa sukayi suka watse daga dakin mama Asiya tana ta bakar magana.
Maji tadawo daki zuciyar ta na mata kuna ta samu su Amira suna ta hiran su Bintu tana gefe zaune a makure bata tanka masu a hiran nasu.
Suna ganin ta sun fahinci ranta a bace yake anyi ba dadi ke nan a can falon baba.
Amira tai tsuki tana fadin wallahi yaya sadauki dai yana jawo muna matsala a gidan nan.
Bintu tace sai ko mu bishi da addu,a don adfua makamin mumine ne tunda ba haka Allah ya halicce shi ba ai.
Dago kai Maji tayi ta dan tsura wa Bintu ido sai kuma ta kawar duk yadda taso ta danne hawayen ta kada su zubo saida suka zubo mata.
Hankalin yaran gaba daya ya tashi sai cewa Amira take halan mi sukace maki maji.
Bintu tace haba Anty Amira maganan manyane fa sai su kawai dai mama tayi hakkuri tabarwa Allah al,amarin shi, ian Allah mai karban adduan bayin shine idan Allah ya tashi canza shi sai kowa yai mamaki a gidan nan.
Hmmm Bintu ke nan baki san ko waye yaya sadauki ba ko a gidan nan ki barshi kawai kuyi yar nisa danisa dashi shine sauki wallahi.
A,a anty Amira insha Allahu wata rana sai kunyi mamakin shi Allah dai yasa wanan halin na iya kurciyane kawai.
Ikon Allah ke kin iya magana kamar tasbin kaka kamar wata babba van wallahi.
To Antu ai ba abinda yafi karfin ubangiji nagani don shine maitin komai a lokacin kuma da yaso wanan fa jerabawa ne akan su mama da baba sai dai muce Allah ya basu ikon cinyewa kawai.
Shiru dakin yayi suna nazarin zancen Bintu yarinya karama da babban magana kamar wata babba can.
Jin sunyi shiru Bintu tace da zamu dage ko mu iya dakin ga mu dinga aiwatar da ibada akan shi kawai ba,wai mu tsaya muna magana kamar sauran mutane ba muna kuma yin sadaka akai insha Allahu ba,dadewa zamuga saukin al,amarin da yardan Allah.
Don ni wallahi na yarda da addua takobin mumine sosai don da na roki Allah saiki ga an karba min.
Dariya,suka saka mata kai Bintu wanan cika baki haka kamar wata,shirihiya can.
Hmmm anty ke nan nifa tun ina karama Baba na ya kowaya min yin addua kin san ban tashi a gaban mahaifiyata ba.
Da sauri maji wacce sai yanzuta sa masu baki a zancen su tun shigowan ta tana hawaye tace.
Fatima ina mahaifiyar ki take Bintu tace tana can wani kauye tana aure sun rabu da Baba ance tun ana goyo na da ya auri kishiyar mamana.
Shine da aka yayeni iyayyen ta suka dawo dani gurin mahaifina wai bazasuyi wahalan banza ba .
Tayar dake shine suke gani wahalan banza Bintu tace cikin yar murya haka suke gani sai kawai ga kwallah ya zubo mata,
Bata daina magana ba don kwallan sai cewa tayi, mama nasha wuya a gurin mama hausi sosai don har tsakar gida na kwana ni kadai tun ina yarinya na.
Da kuma na girma abin ba,a cewa komai don ba irin wahalan da bata gwada min.
Amma sai gashi duk yaran ta ba wanda ya kaini don mazan su da matan su duk sun lalace mata sai nice ma nadawo tana dan jin sanyi a gurina.
Ina ganin ganin da Baba yayi aikin wahala zai kashe shine suka hada baki da,gwagona wai nazo nai mata hutun sati biyu na koma.
Sai daga baya gwago take fada min cewa wai Baba na yace na zauna gurin ta kada na koma garin mu.
Takarasa maganan cikin kuka tace ina kewan gida da yan uwana sosai da farko amma yanzu don rikon da gwago take min yasa na manta da komai gashi yanzu zama daku yakara sa hankali na ya kwanta sosai bisa ga zamana a can kauye don abubuwan da ban sani ba,a,rayuwa yanzu na,san su sosai.
Tun ina shekara sha hudu na haddace alkur,ani maigirma yanzu tulawa nake sai dai akwai banbancin karatun mu na can da naku na,nan birni sosai.
Kinga ashe na,dan san wani abu nima ga,addini ke nan don malamin mu yana gwada mu abubuwa siri sosai.
Allah sarki ashe mahaifiyar ki bata tare da mahaifinki gaskiya wasu mata akwai ha,inci a tare dasu sosai wallahi.
Shi yasa nake ta hakkuri tun farko da cin fuskan da ake min a gidan nan don yaran nan dake gabana don idan na fita na barsu cikin gidan nan wa kuke ganin zai rike min ku amma na cikin su, ina ciki ma yaya muka kare dasu balle na fita na barku.
Duk shiru sukayi suna nazarin maganan Maji don sun san gaskiya ta fadi ba mai iya rike su amma kamar yadda suke rike yaran su.
Kowan su tasan gaskiya Maji tafadi don ba mai iya rikon su amana suji dadi kamar yadda tace don haka sukaji tausayin uwar tasu ya kara shigan su sosai a gidan.

****** ********* ******
Salamu Alaikum wai ana sallama da Raiha sai mama dake duke a kitchen ta dago tana cewa kai waye da yamman nan ka ce bata nan.
Kai tsaya Raiha dake fitowa daga bandaki tace wa yaron je kace gani tafe kaji.
Raiha yanzu don baki da kunya zance zaki fita da rana haka kowa yana ganin ki kikau a kofan gida tsaye da namiji duk wanda ya wuce yai miki tir da halinki ko?
To mama kin san ko waye da,zaki kore min mai shi mama bari naje naga ko waye nadawo, kawai sai ta shiga daki ta shiga gyara fuskan ta tsab ta saka hijjab din ta sai waje.
Mama dake waje ta rike habar ta cikin mamaki sai cewa tayi ikon Allah yaran yanzu Allah ya kyauta kawai.
Raiha tana fita taga gidan su tunfitowan ta ya kura mata ido yana kare mata kallo nan yasan yarinyar tayi mashi ga komai kuma,zai more mata sosai idan yai sa,a ta yarda da bukatan shi gare ta.
Dan waige waige taks don bata ga mai neman taba a lokacin sai wani bakar mota mai tsada da ta hango, daga wajen gidan su, dan nesa kadan da gidan.
Hon din da mutumin dake cikin motar yayi yasa tagane shine mai neman ta a lokacin.
Raiha ta nufi gurin a cikin mamaki don ita duk iya sanin ta,bata da saurayin da keda koda karamar mota balle wanan dirkekiyar motan dake gaban ta.
Mutimin da tagani a motar bata taba ganin shi ba,a,rayuwan ta don haka sai tai tsanmanin ba gurin ta yazo ba.
Sai taji yace malama,Raiha ko ?
Eh nice
Bisimillah shigo daga ciki mana ko kina tsoro ne kuma.
Tai wani irin har da idanuwan ta ce tsoron may zanji kawai dai ban gane ka bane dai.
Bazaki gane ni ba,asalima baki sanni ba ni ne dai na,san ki ta hanyar gane gane na nahagonki kawai.
Shine na biyo ki har nagane gidan ku ne nan sai yau na yanke shawaran nazo gurin ki dafatan zaki fahince ni ai.
Wani kallo tai mai kamar bata yarda da,zancen shi ba sai tace mai a ina ka ganni ne ?
Sai da yai murmushi sannan yace a gurin birthday din Salim murmushi tayi don tasan anyi hakan .
To amma duk tsararun yan matan;dake gurin bai gansu bane sai ita zaizo gurin ta, sai kuma,wata zuciya tabata amsa dacewa kece kikai masa kawai a gurin.
IkonnAllah tace a fili tare da,fadin shine kabiyo ni har gida kuma ?
Yace eh mana ko nayi laifi ne tace bance ba yace to sunana Abdul amma ana kirana duwel ne don haka abokaina ke kirana dashi.
Hmm tau nagode da,har ka zabi kazo guri na,dafatan lafiya kazo har gidan mu a,kaina.
Murmushi guy din yadan yi tare da,cewa ai tunda kika ganni a gurin ki ke ma kin san alheri ne yakawoni gareni da,fatan zaki fahinci manufata a,gare ki batare da kin fassara min zance na ba.
Murmushi Raiha tamayar mashi tana cewa da fatan zan samay ka mai cika alkawari nima.
Nan suka tsaya suna dan kara fahintar da junan su kan shi tare da dan hira yana fada mata ko shi waye da inda yake aiki.
Ganin yamma tayi sosai tasan mahaifinta zai iya dawowa a lokacin yasa ta yi mashi sallama ta,shiga gida da fara,anta.
Tana shiga takasa boye farin cikin ta take cewa mama yau saura kiris ki kore min sa,a ta kin kuwa ga mutumin da yazo gurina ne.
Uwar ta mayar da hankalinta akan yar ta tana sauraren bayan nin da takd mata akan bakon ta.
Har saida mahaifinta ya shigo gidan suka bar zancen don gudun kada yaji zancen su.
Tun daga wanan ranan suka hada alaka a tsakanin su ita da Abdul din guy din da ya tafi mata da imanin ta gurin son ta.
Ba uwarta ba har mahaifin ta saida ya,san da zaman Abdul din don masifan son da Raiha take mashi.
Wasa wasa Abdul ya fara dan test din Raiha da,wasu yan abubuwan da yake son sani ko tasan da su a sabon sallon so da matasan yanzu ke ciki yanzu.
Bai samu matsala ba don ya samay ta yarinya ce yar rock sosai ba wasa don haka harkoki suka fara tafiya a tsakanin su ba bata lokaci.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

A LOKACIN MU KE,,,


Waya take sai ko mama dake kusa da ita bata iya jin may take fadi a,wayan , saboda matukar tausa muryan ta da tayi ga wayan.
Sai yar dariyar da tayine yasa mama dake zaune saman kujera yar tsugunno dago kai tana mata kallon mahaukaciya.
Ta dan dauki lokaci tana wayan cikin jin dadin abinda ake fada mata ga,wayan wanda babu maijin ta balle a san abinda su ke fadi.
Mikewa,tayi zuwa cikin dakin su inda ta kwanta saman dan gadon katakon dake dakin mahaifiyar nata.
Nan ta shige cikin katon hijjab ta rufe kanta sai dai hannunta na akan gaban ta zuwa kirjin ta a hankali take dan shafa,su don kada a gane may take a lokacin.
Nan taci gaba da,wayan ta na tsawon lokaci mai tsawo sannan tai wani mike barci ya dauke ta.
Haka mahaifiyar ta ta shigo dakin daga gurin girkin da take yi ta samay ta kwance tana barci,
A fili ta furta kai amma,anyi malalaciyar yarinya gurin nan yanzu barci kikayi ashe ni ina jiranki ki min shara a,tsakar gida.
Nan dai uwar dole itace ta karasa aikin ta,da kan ta inda Raiha bata farka ba sai bayan sallah azahar ko shi sai da kyat uwar ta,tayar da ita don tai sallah.
Bayan ta gama cin abinci a lokacin har uwarta na zance dora girkin dare don yamma tayi sai ga Raihanatu tafito a cikin shiga na fita da katon hijjab din ta har kasa.
Sai dai kassh da mutum zaiga mai ta sa a kasan ta da yayi tir da Allah waddai da irin shigar ta haka.
A,a Raihatu ina kuma zaki a wanan lokacin bayan yamma ya riga da yayi ko?
Mama dan wani guri ne zan tafi ba,wai dadewa zanyi ba yanzun zan dawo mama.
Tana fita bata tsaya ba sai shagon sayen kayan mayen su wand kamar kullun gurin ya zama majalissan matasa yan maye kala kala.
Duk da jami,an tsaro suna kawo masu samay akoda yaushe suna zuwa kama mata a gurin masu dabian shaye shaye.
Can ta kutsa tashige daga ciki gudun kada wani yagan ta a gurin don gudun ganin idon sani.
Brosha na ganin ta a lokacin yana mikawa Umar kayan harkan shi Umar wanda yake tsaye da bakaken kaya fuskan shi a murtuke.
Burosha yana ganin ta ya fara washe bakin shi cikin farin ciki da ganin ta yana cewa
A,a yau mutumiyar an shigo ke nan kayan aiki sun kare ke nan dai ko don ba,a ganin ku sai rana,tai zafi.
Ya dauko canji zai mikawa Umar yake ce ko yau din ma,za,a barmata canjin ne dan wancan katon ma naga kai ka biya mata.
Wani kallo Umar ya watsa wa Raiha yace cikin dakiya don Allah ka,sallamay ni don kasan ban son ina dadewa a gurin nan naku,
Raiha cikin yatsune fuska tace aikowa ma,sauri yake don ba wanda yazo don ya tsaya .
Kamar Umar ya bata amsa har ya dan bude baki da zuman yai magana sai kuma yaja bakin shi yai shiru .
Borasha ya mika mai canjin shi yai gaba bai tsaya bin ta kan raiha ba balle ya kulata ma.
Bin shi Raiha tayi da kallo tana fadin ji shi kamar wani mutumin kirki wai sauri yake bai son a gan shi.
Brosha yace to ke nan fa wanan zubulelen hijjab da kika,sa wa zai dauka ba islamiya zaki a haka ba .
Dallah gafara malam nagafa kafara saka min ido don tsokanarka ya fara yi min yawa fa.
Dan sa ido kawai ina ruwan ka da shigata wanan nayi ne kawai don batar da sau amma a ciki ai shigar manya ne nayi sai ta dan daga mashi hijjab din ta inda ya hago wani matsatsen rigar da ta,sa duk nonuwan ta sun dan bultso a gaba sai dan guntun buje na zuwa part dakd saye a kunkurun ta iya cinya kawai.
Kai brosha ya daga tare da fadin kai amma Raiha kin kai shu,uma irin wanan shigar haka sai ina?
Don dai nasan da,akwai inda kike nufi zuwa da wanan shigar haka da kika boye cikin wanan katon hijjab din naki.
Tai wani har da idanuwan ta tana cewa ashe ka gane ke nan mazan, yau casu gare mu har dare shiyasa na dauki kayan aikina don ya taimaka min a can,
Tirka sa ki ce yau akwai babban harka ke nan raiha don nasan mutanen mu zasu hadu a gurin,
Tace hakane amma ba,wai irin wa yan nan ba wanan gayu ne masu harka da kwalabe da manyan wa yan nan,
Nima hanya akai min don naje naba idona abinci ko zanyi cafka a can don kasan ala,amarin sai da kwaskwarima ciki wanan lokacin don gamu nan birjit ko ina kowa na rabon ido yasamu mai cafkan shi.
Gaskiyan ki Raiha nima nasan sai da haka al,amarin don abin ba,a cewa komai.
Aje lafiya a dawo lafiya a yo muna kamu babban giwa mu sha shagalin mu muma ga,aljihun shi.
Ta,wuce tana tafiya a cikin rangaji da layi irin nasu na mashaya da suka goge a fagen boyon kan su, don batar da kaman nin su ga mutane.

****** ********* ******
Guri ne mai kyau da,shuke, shuke ko ina bakajin komai sai sautin kidan dake tashi na turan ci na mawakan Afrika.
Tana fita daga cikin napep din da ya kawo ta ta samu dan nesa kadan ta cire hijjab din dake a jikin ta tare da dan kara gyara tufafin dake jikin ta.
A hankali take takon ta zuwa inda mutane sukai dan dazo akasarin maza da matan gurin zakace ko ba diyan gari bane.
Don irin shigar su da kuma aakin kan su sai mutum ya rantse cewa ai a wata kasar arna ya ke ba cikin garin sokoto ba ma gari shehu usman dan fodio.
Mutumin da yai gwagwalmaya akan addini a kasa da,watsa su har sauran kasashen duniya don amfanin al,umma.
Amma,yau sai gashi a,kasan shi garin shi duniya da lokaci yasa matasan kasar kwaso akidar yahudawa suna yadawa da cusa shi ga,sauran masu tasowa na baya.
Wanda ba,a sokoto ba kawai yanzu ko ina a kasashen hausaw a na samun wanan akido jin na koyan akidar wasu da,al,adun su.
Allah ka tausaya muna ka,shirya muna al,umman mu yaran mu kan,nen da ma,sauran yan uwa musulmai baki daya,
Da farkon shigan Raiha a guein ta dan sha jinin jikin ta don tana ganin abinda yafi karfin idanuwan ta.
Sai da ta hadu da,wasu kawayen ta biyu haka yadan sata sake jiki dama can sune suka gaiyato ta gurin.
Daga inda take a zaune tana bin mutanen gurin da,kallo a fakaice tana kallon irin shigar da mata da mazan gurin sukayi abin sai shukaran kawai.
Don nata shiga ai mai sauki ne bisa ga na wasu yan matan yadda suka saka dan mitsitsin abu a jikin su abin ba dadin gani
Raiha sai tarena kanta a guri don taga iyakar wayewa a gurin yan duniyan da suka fita iya duniyan ci sosai.
Taro yai tsit saboda fara gabatar da bukin da,aka,soma wanda suka ce sunyi shi ne don tunawa da kafa gungiyar su mai shekara biyar da,kafuwa yanzu.
Inda,wasun su sin mutu wasu kuma,sun dain harka suna wani kasar haka dai maigabatar wa yai ta bayane na,shirmay a guri a na ihu da,sowa irin na yan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login