Showing 279001 words to 282000 words out of 373688 words
Chapter 94 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
a hannun shi ashe takardan addmition ne na makaran tan da zai tafi.
Zama nayi a gefe daya ina satan kallon su duk da hankalina yana gurin tv dake aiki a lokacin.
Musa ya tatara kayan shi ya kwasa cikin jin dadi zuwa dakin shi tare da muna sai da safe nasan zai tafi yyakara baje kayan ne yasake kallon su a tsanake.
Shiru falon yayi ba wanda ke magana a cikin mu sai tv dake aiki shi kadai ana ta watsa turanci ganin ankirashi a wayan hankalin shi ya dauke yasa ni mikewa nabar falon.
Bathroom na shiga da niyan nakewa sai naga kawai nai wanka na ji dadin kwanciya kawai nafito na dan shafa mai laushi tare da saka yar rigar barci na dana feshe da turare, light pink mai dagwari biyu sai dai iya cinya ya tsaya min rigar.
Ina zaune saman gado naji ya turo kofan daki sai dai ya sauya kayan jikin shi saye yake da wani wando mai laushi iya gwaiwan shi kamar three quarter da rigan shi mai kama da dinkin banga na maza.
Sau daya na daga kai na na kalle shi na dukar da kai kasa inda nake zaune a dan stoll din mirror yazo ya zauna tare tare da kura min ido.
Muryan shi naji yana fadin tashi muje mu kwanta tunda ke baki san abinda ya dace mace taiwa mijin ta ba sai an fada maki.
Na dan bata fuska tare da turo bakina nace ni anan zan kwanta murmushi naji yayi tare da riko min hannuwa na ya mikar dani tsaye.
Look at me yace, sai na dan dago kaina kadan na kalle shi amma ban iya jure kallon shi ido da ido dole na dukar da kan nawa, kasa.
Yace daga yau ban son sai na kara biyu ki a dakin ki don ko zo guri na ke baki san right din ki ba ne a gare ni.
To bari kiji bazan biya kudin sadaki na ya tafi a banza ba ni ina gabas kina yanma kudi nabiya dole kuma a bani hakkina.
Jin abinda yace yasa ni watso mashi harara au harara na ma ki keyi ko ba biya nayi ba ne ?
Cak ya daukeni kamar ya dauki babyn roba sai dakin shi ya dire ni saman gadon shi yana cewa this where you support to belong every night.
Rankwafo wa yayi tare da raba hannaye shi yasani tsakiyan shi kokari yake sai mun hada ido dashi amma na kasa lumshe idanuwa na nayi.
Yayin da naji yafara canza min sallon wasan shi a hankali yafara bin sassan jikina da wani irin romacig.
Tun ina iya daurewa har na fara dan nishi, kadan kadan cikin neman agaji sosai yake gwada min wani irin mahaukacin kauna wanda ni kaina ban iya cewa ga inda nake a lokacin.
Mun dauki tsawon lokaci dashi sai da ya gaji dan kan shi ya sarara min tare da rugumay ni a jikin shi yana sauke numfashi a hankali.
Al,amarin yau da dan sauki bisa ga daren farkon mu dashi don banyi mugun jikita irin na wancan ranan ba.
Gaba dayan mu shiru mukayi kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi a lokacin.
Ni dai tunane nakeyi anya kuwa zan iya da yaya sadauki ashe mutum haka bai da tausayin mace ko kadan.
Ko dai dama haka yake ne wai yana mu,amula da wasu matan ne acan baya.
Da sauri nai istigifari don ance zato zunubi ne koda ya zama gaskiya don haka nai saurin janye wanan tunanen a raina.
Shiko tunane yakeyi wai dama ashe abinda Bashar ke ta fihintar dashi ke nan akan mace.
Tabas yanzu ya yarda da zancen bashar da yake cewa dan hakin daka raina shike tsone ma ido ashe ni,ima da baiwane tattare da wannan yar kara mar yarinyar da ya raina a idon shi.
Bai tsan mani a rayuwa zaa samu mace haka mai tarin ni,ima da baiwa ba irin na Fatima ba yarinyar da bai taba samun wani jindadin rayuwa ba irin wanda yake tsinta yanzu a jikin Fatima ba.
A hankali ya kai hannun shi saman kaina naji yana shafa a hankali ban san lokacin da na saukw wani irin ajiyan zuciya ba mai karfi.
Ji nayi yakira sunana a hankali yana fadin FATIMA na amsa a hankali da fadin naam .
Sai naji ya rugumay kamar wani zai kwace mashi ni a lokacin yace.
Don Allah ina son kiyi hakkuri da halina kizama mai dauriya acikin duk wani al,amari na zaman takewan mu nidake.
Idan har kin min haka kin gama min komai bazan taba son na samu matsala ba daidai da rana daya da mahaifiya na koke don rayuwa a yanzu akwai akasi a cikin shi kala da kala.
Shiru nayi ina sauraren shi, yayin da idanuwana suka ciko da hawaye wanda ba zan iya fadin ga dalilin zubowan su ba a gare ni.
Kukane ya kubuce min jin yadda nake kuka yasa shi kara manna jikin shi sosai da nawa shi bai lalashe ni ba kuma bai iya furta komai ba .
A haka barci ya daukeni ban san manayi barci ba sai dai dana falko nagani a saman chest din shi kwance nayi filo dashi.
Gyara kwanciya na nayi dakyau abinda yasa shi dan motsawa ke nan ya kara jawoni zuwa jikin shi.
Da safe da kyat na mike na nufi dakina can na gasa,jikina sosai da,ruwa masu zafi haka yasa na dan samu saukin ciwon jikin da nake ji dana tashi.
Nai matukar mamaki kwarai da naga yaya yana sallah jam,i bai wuce shi duk asubahi sai naji fitan daga gidan zuwa masallacin uguwan sallah.
Ya dawo daga motsa jiki ya samay ni tsaye ina hada table din cin abinci a cikin kunyan abinda ya faru a tsakanin mu daren jiya yasani dukar da idanuwa nakd gaishe shi da kwana.
Ya kara so tare da dan rike ni daga bayan na yana cewa, ke baki gaji bane har kika tashi ki aiki haka mai yawa?
Kunyan shi nake ji ban yi magana ba sai dan murmusawan da nayi nace yanzu zakaci abinci ne?
Ba abinci nake son ci ba ke dai nake so yanzu ya bani amsa fuskan shi a daure tamau kamar ba wani magana yayi ba a lokacin.
Da sauri na kalli agogon ban gon dake falon sai na ji ya furzi iska yace zan makarar dake ke nan kike nufi ko?
Ya juya ya fara tafiya yana ffadin ok a dawo lafiya sai dai kafin ki dawo zan kai musa school din su sai kuyi sallama dashi.
Daga haka ya shige dakin shi ya barni gur8n tsaye koda na shirya nashiga yi mashi sallama na samu ya shiga wanka a lokacin.
Don haka na cire mai kaya daga cikin wardrobe din shi haka zai sa yagane na shigo dakin na juya nafita da sauri don na kusa makara ranan.
Bayan yafito kayan da ya samu na fitar ma saman gado don yasa yasa shi gane cewa na shigo dakin a lokacin sai daya gama shirin shi yafitone musa ke fada mashi nace na tafi don na makara yau.
Yana gamawa dama musa duk ya kagu su wuce don haka,basu bata lokaci ba suka fita zuwa school din da za,a kai shi na kwana.
****** ********* ******
Haka muka kasance da yaya kullun a tare muke kwana dashi yana yadda yaso dani tun ina jin nauyi da kunyan shi har na dan fara rage kunyashi da nakeyi sosai.
Yanzu yakai basai yace nazo dakin ba don kaina nake shiryawa naje don ma inhar banje ba shida kanshine zaizo ya dauke ni cak yatafi dani.
Ya gama binda yake ya koma gefe daya yana sauke numfashi a hankali tare da furzo iska daga bakin shi.
A raina nace wai dama maza basu da kunyane haka wai kamar ba shine mutumin da ke ta cika bakin shi ba abaya akan dole ne maji ta lakaka mashini.
Yanzun gashi shine harda wasu irin kalamai da ina ganin ba a hayacin shi yake fadar su ba idan mun kasance a dukule tare.
Idan kuma weekend ne zan iya cewa kusan a tare muke zama muyi shi agidan bai son fita nan da can yana nan ciki ya hanani shakat a gidan sai yayi yadda ranshi ke so zai sarara,min.
Watan shi daya cur a garin da dawowa bai fita zuwa koda Abuja bane yanan cikin gari.
Ranan ya shigo da yamma yake ce min na shirya zamu fita zuwa gida mu gaida su baba don baba bai jin dadi jikin shi ya tashi.
Na dan rude ina fadin subbahanallahi may kuma ya faru da,baba ni dai Allah yasa ba wani mugun abin aka aikata ba har ciwon shi ya tashi.
Tun karfe bakwai na fara shiryawa na saka wani atamfan super exclusive, mai ruwan yellow da zanen ganye kore zani da rigane sai gyalen da na yafa karo na farko a gidan aure na.
Takalma da handbag duk na fitar da zan saka sai wani irin mayen kamshi dake tashi ajikina na dade ina bata lokaci gurin gyara jikina kamar wacce zata gidan wani shugaban kasa.
Nasan idan na samu matsala ga shigana ba su Umma da mama ba har Amira sai na samu musguna daga gare ta.
Sai gashi ya shigo dakin yana wani kamshi dashi yai mugun haduwa don shadda ce gezenah a jikin dark blue sai wani maiko da yauki takeyi har hulla sai da ya saka yau nace dankari a raina wani abu ko sai mahaifa.
Yadda yake kallon shigana nima haka nake satan kallin nashi shigan don duk wanda ta fan mu komai bakin cikin mutum dole ya kyasa muna.
Karasowa yayi har inda nake zaune a gaban mirror ya kura min ido can naji ya numfasa yace wai ke ashe haka kike dama kike ta faman boye kanki cikin mugun hujjib kullun kamar wata munafuka can.
Nace ai dama sunana ke na a bakin ka kuma boyewan danakeyi ai ba kaina naiwa hakan ba don da baka samay ni ba kai.
Namike ina cewa dama nasani na dinga kwalliya irin na anty Nafisa tunda shina ga yafi burge mutane yanzu.
Yace dako na halakaki tun lokacin don ba zaki jawa maji zagi ba, nace ai naga shine ra,ayin ku ku.
Murmushi yayi tare da kamoni yana mikar dani tsaye yace ki tabbatar da kin rufe min wanan jikin naki da kyau don kinsa akwai kardawa a gidan .
Yayyen nawa ne kuma gardawa ashe kardawan yawa gare su bamu sani ba masu kalle surar kannen su .
Yagane maganata sai yai murmushi kawai yace ai ban kalle ba sai dai ina shirin kallo don gada wani ya bani labarin abinda ban sani ba nida abina.
Da sauri na dago kaina nace may kake nufi da hakan ya wani lumshe idon tare da furzo iska yace ma,ana har yau ban san komai ba akan matata da rana ganin dare kawai nake mata koshi ma a,wahalce ga cizo ga yakusa da zagi.
Murmushi nayi na dukar da kaina kawai don natuna first night din mu dashi yadda naitakiran shi azzalumi macuci mazina ci kawai.
Isan kin shirya sai ki tashi mu tafi kada ki bata muna lokaci don ina da abinyi ni idan mun dawo don ba wani dadewa zamuyi ba can.
Kallon mararaicewa naimashi nace tare da turo baki, ni wallahi kullun abu kullun abu ba tausayawa mutum.
Yace wani abu kuma cikin kasheni da idanuwan shi don son jin amsa na.
Banyi magana ba sai gyalena da ke tashin kamshi kawai dana yafa akaina nan na kara fitowa wata shar dani nai marukar kyau har ya kasa dauke idon shi akaina.
Yarinya ke kikace kina so dabakice kina so ba da ba,abaki ni ba, yasani gaba muna tafiya yana min waka a baya na.
Wata landdrove jeep nagani a waje dark blue sai shaki takeyi van san da ita,ba a gidan sai wanan lokaci ko ba afada nasan ansha miliyoyi a waban gurin .
Ita muka shiga shike driving kamar bai son tukin motan nace amma ya kamata mu dan sayi wani abinda zamu shigawa baba da su Umma dashi kada mu je masu hannu a sake.
Kamar baiji mai nake cewa ba yai banza dani a raina nace bahagon mutum kawai wanda ba,a gane kallan shi kaman ba shine yanzu yake min waka ba gashi mintina kadan ya wani sha toka ya murde fusaka tamau dashi.
Gaban wani katon shago ya tsayar da motar shi sai da ya kashe motan ya juyo yana ce min fito mu tafi.
Har mun fara tafiya yace gyara rufe jikin ki dak yau don kinga an fara binki da kallo kiyi shiga kamar wata budurwa can.
Gyara tsayin gyalena nayi da kyau tare da bin bayan shi munyi sayayya sosai a shagon har sai da nai mamaki leda kusan bakwai akayo muna muka nufo gida dasu.
Ina ganin get din gidan nai wani lumshe idanuwana don jin dadin ganina a gidan da nai rabin rayuwana a cikin shi cikin jin dadi.
Muna fita gab da zamu shiga gidan sai naji ya riko min hannu na kallon hashi nayi ba tare da ya kalle ni ba yace eh haka nake son maman ki ta ganmu don tasan na rike mata amana.
A haka muka shiga gidan mun fara cin karo da yaya Abdul yace tun daga nesa a,a,a Allah yayi hadi a gurin nan sai kace kuka hallici kan ku haka.
Murmushi ya sauke kawai tare da kara rike min hannu da kya yaya Abdul yace kaga zabe gaskiya kan nan ba irin wa yancan da suka zabo mata ba kamar suna barci.
Muna shiga cikin gida Rukaiyya diyar mama Asiya tana waje tsaye tana waya tana ganin mu ta wani watso muna idanuwan ta gaba daya a kan mu.
Dakin maji yace a fara shiga da kayan bayan ya cire wasu leda guda uku daga cikin ledojin da,muka shigo dasu yace min a hankali kiba wa su Umma kowa guda guda nace angode.
Dakin Umma muka faea zuwa tana zaune da yaran ta sai jin sallaman mu tayi har mun kawo kofan shiga ko duk sai ta daburce da ganin mu.
Zama yayi kan kushi na zauna kasan carpet daidai kafan shi muna gaida ita .
Cikin hali irin nata na shan kamshi take amsa muna kallo daya tai muna wani mugun hassada da bakin ciki ya darsu a zuciyar ta tace kina nan kina ta hakkuri da halin mijin naki ko don ba fasawa zaiyi ba na sani.
Murmushi kawai mukai mata don duk mun fahinci nufita amma muka kyale ta
Bamu dade ba muka mike na karasa gaban ta ina cewa mama ga wanan ba yawa dan tsara bane ta amsa a wullakance tana tabe baki tana fadin angode.
Na juya har na fara rafiya sai najuyo ina cewa yaya sagir fa idon ta nagani tana kallin kasan zanina da harara tabini ta tabe baki tace yafita dazun nan.
Dakin mama Asiya kuwa muna shiga dama Rukaiyya ta riga data fadawa mamata zuwan mu ko da ta gan mu.
Idon kyam a kaina yadda mukayi dakin mama haka mukayi a dakin ta bamu dade ba mukafito namika mata ledan tace to har da wani tsaraba can to angode.
A daiyi ta hakkuri don kin san abinda kika aura dama don haka sai a daure da hakan .
Muna barin gurin sai dakin mummy sai dai a rufe dakin yake yaran ta dai ne kawai a ciki alaman tana dakin baba a lokacin.
Yaran suka yo kanmu suna muna sannu da zuwa cikin rugumay mu Imirah yace yaya nace mummy takai mu gidan ka tace wai zamu damay ka kana hutawa .
Muma yaya kazo ka kaimu mu huta tare da kai kaji, ya shakan shi yace zanzo na dauke ku.
Yaran sukaji dadi suna ta murna yayan su yace zaizo ya dauke su zuwa gidan shi namika masu ledan tsaraban su wanda daban yake saboda akwai alawan yara acikin shi.
Sai dakin mama muka nufa kuma suna falo zaune da Amira muka shiga da sallama ina rike a hannun shi kamar wata yar yarinya can dani.
Sannu ku da zuwa mama tai muna Amira tana dago ido kallo daya tai muna naga tai sauri kawar da kan ta gefe daya tana cewa sannu da zuwa yaya.
Nace anty ina wuni ta ansa a wulakance da lafia kawai ta juya kan ta ya kalle ta yai murmushi yace sister ke nan yaya gidan gaban mama na tafi na durkusa a gaban ta nace mama ina wuni ?
Cikin jin dadi da ganin mu haka tace ashe kuna tafe ne yanzun tashi ki zauna Fatima kinji Allah yai maku albarka ai yanzu yaro yashigo da leda yake cewa kune kuka shigo.
Sadauki yace maji yaya na barku dazun haka yasa nagane cewa yashigo da rana ashe nice dai yakawo nagaida Baba da jiki ashe.
Mama tace mai lafiya muke yace to yaya jikin na baba tace a,a Alhamdullahi ai ya samu sauki sosai har ya tashi yayi sallah ko dazun.
Ta juyo gareni tana cewa Fatima kuna lafiya ko cikin jin kunya nake cewa lafiya kalau muke mama.
Tace ashe musa an tafi makaran ta saiga babana yazo dashi ya sallamay ni ranan .
Cikin