Showing 51001 words to 54000 words out of 373688 words
Chapter 18 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
larai ta juya tabar gidan tana fadan karya inda tasan yana gidan lokacin da batai gigin shigowa ba lokacin.
Tana fita ne baba ya juya gurin mama yana cewa ke kuma in kina kama girman ki ki kama don wanan ba halin arziki bane gareki.
Mama dai sai faman haushi takeyi wai tana fada an mata gori ita da diyan ta a gidan.
Indai don auren tsofin da nakeyi ne inna take ganin kamar wani fin diyan ta nayi su zuba haka zan kare rayuwana a wahalce gidan Jatau.
Don duk yadda zatayi shige da fice sai tayi ko bama so sai na tafi gidan nan nai masu bauta su ma kamar yadda na saba yi a gidan garbati bakin ciki shi ya dade bai kashe Inna ba dani.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE.
IDAN KIN BIYA KI RIKE AMANA YAR UWA KADA KIBA WA WANDA BAI BIYA BA PLEASE DON AMANA NAUYI GARESA, ,
Shirin kwanciya sukayi tana saye cikin kayan barcin ta sun matukar karban jikin ta sai hullan da ta saka a kan ta don kariya.
Har wanan lokacin mijin ya fahinci tana cikin damu wanda bai wuce nasaba akan yaran ta ne da zaman su ke hannun kishiyan ta.
Tsaye yake saitin window dakin yana waya daga inda take kwance tana kallon shi.
Tun yana wayan a hankali har yakai ya fara daga muryan shi yana cewa.
Wai ke mahaukaciyar ina ce haihun ki nawa a gidana don a sani na ai kina haihuwa har ma yaushe ne kika haihu wai ?
Bata ji may ake cewa dashi ba don ba handfree wayan shi yake ba a lokacin ta fahinci indai zaiyi waya bai saka handfree ba da kishiyoyin tane yake waya wani lokacin.
Muryan shi taji yana fada a hasale yana fadin wai ke hindatu wata irin mace ce wacce a kullun sai ta fito da sabon sallon tashin hankali a rayuwan ta kada dai a zauna lafiya.
To ki sani na fada maki banda kudin zuwa Germany ganin wani likita kan neman ciki duk shekaran yar ki nawa da zaki tayar da hankalin ki kan wai neman ciki yar just three years take nema fa yanzu.
To ki sani duk abinda kikaga dama kiyi amma amma ni bada kudina ba cikin wanan shirmay naki.
Daga haka ya katse wayan tare da jan tsuki ya nufo gadon don ya kwanta shima.
Yana kwantawa yaji muryan salihan matar nashi mai son shi da kaunar shi tsakani da Allah na fadin.
Hindatu ce ko ?
Yace a hasale itace mana.
Anya kishin hundatu ko akwai imani a cikin sa heartbeat ?
Yace nima abinda nake tunane ke nan ko dai tana da matsalan kwakwalwane .
In ba haka ba yaya da ganin wata da ciki duk tabi hankalin ta ta tayar ga banza ?
Ta manta cewa Allah ne ke bayarwa ba mutum ke badawa ba da kan sa.
Tace to ai ba fada zakai mata ba tunda abinda take so ne sai ka lalashe ta a wuce gurin.
Yace oho na tsaya mata sanya ta ci gaba da min rashin hankali da ta saba ke nan ko ?
Tace ba haka bane hankalinta ne ya tashi bata cikin natsuwa ne yakawo hakan .
Yace matar da bata damu da damuwan kowa ba kan ta kawai ta sani ita a rayuwan ta.
Tace hakkuri dai zakayi ka rarasheta kada ta jefa kan ta cikin wani hali kuma na daban.
Yace na fada maki ki bar wanan yarinyar kawai samun daurin gindi tayi a gurin daddy shiya sa take min abinda taga dama.
A can kuma gida Nigeria inda Hindatu take zaune gaban mahaifiyan ta tana rusa kuka.
Mahaifiyan nata tace na fada maki kibi a hankali kin san halin mijin ku da murdaden hali baida saukin fahinta ko kadan.
Maza ki kirashi ki kara bashi hakkuri tun bai ce zai dauki wani mataki ba a kan ki.
Uwar tace maza kira min shi nai magana dashi don nasan yanzu yana can hasale duk inda yake.
Mama yanzu fa dare ne a can wata kilama sun kwata a lokacin nan ko.
Dama dai baki son zaman lafiya aike baki san maza sai da lalashi ba kina ganin komai dole daddy sa ya sa shi dole a kanki.
Sai dana fada maki kada ki kirashi yanzu kiyi hakkuri har su dawo don sai ya fahinci kan wanan matar tashi kike wanan haukan haka?
Mama ni kunyan kiran sa fa nake ji na fada maki kin kuma ji amsan daya bani har da ce min wai ni mahaukaciya ce.
Kira min shi kibani shi nace maki aini dole ya ta tsaya ta saurare ni ko.
Dole Hindatu ta kira layin mijin nasu har wayan ta katse ba a dauka ba .
Uwar ta rude iya rudewa don tana gudun mahaifin hindatun yaji yai masu tsiya.
Sake kira min shi inji uwar cikin kidimaywa taje magana fuskan ta kan yarta.
Dole hindatu takara kiran shi yana ji yaki dagawa sai Saade ne ta daga kiran tare da mika mai wayan ya kalla cikin hasala tare da kara mai a kunnen shi.
Mama ya dauka Hindatun tace tana mikawa uwar wayan
Muryan mahaifiyarta yaji a wayan yasa shi dan gyarawa cikin muryan ladabi yana cewa
Yusuf nice a layin,
Yace na gane mama kuna lafiya yaya mutanen gida tace duk muna lafiya.
Yusuf dama kan zancen da kukayi da yarinyar nan ne nake son maka magana .
Yace mama idan wanan zancen ne ni na gama magana na ba hannuna acikin wanan magana.
Har yaushe ta haihu da zata dauku tashin hankali tasakawa ranta haka ?
Uwar tace na sani Yusuf nasan da haka ai rigimane kawai irin na yarinyar nan don shi ciki ai rabo ne.
Don haka kayi hakkuri abar wanan zancen don bana son ko mahaifin ta ya san da wanan zancen haka.
Don Allah kayi hakkuri kasan halin kowa da irin nashi tunanen hakan yana damun tane yasa take wanan haukan haka.
Inji Saade ke bashi hakkuri bayan sun gama wayan da mahaifiyar hindatu din.
Yace ba komai bane ke jawo min haka sai wullakancin da sukaga daddy da hajiya suna min akan su amma yarinya zata gane kuren ta wallahi.
****** ********* ******
Mama ce daki da baba cikin tausan murya take cewa yanzu malam haka zaka bari wanan daman ya wuce mu a gidan nan.
Allah ya rufa maka asiri sai masu hannu da shunin gari ke zuwa neman yar nan don sa, an ta.
Amma ita da uwarta basu fahinci nasaran haka ba don basu da fahinta akai.
Wancan auren da tayi da suka samu dadin su da wasu kaci ko wanna ma idan yai dadi ai sune zasu ci abinsu muna kallo.
Dadin baki mai ratsa zuciya mama kewa baba kullun akan maganan tun bai yarda ba har takai ya amince da zancen ta ya shiga zuciyar shi ya zauna daram ya kafe zai ba Jatau ni.
Ko ina so ko ban so dole ne na amince da zabin shi tunda shine keda Alhakin zaba min miji ai.
Ranan da baba ya koma dakin Inna sai gashi ya fito mata da zancen wai maganan Rahama da Jatau fa yana nan don haka sai ku fara shiri akan aure nan bada dadewa ba za, ayi.
Take ran Inna ya baci idanuwan ta sun sauya launi cikin bacin rai take cewa .
Malam da ba dakai na haifi yarinyar nan ba sai nace kana hassada da ita ko kiyayya don irin kiyayyan da kake gwadawa yarinya yai matukar yawa a gidan nan.
Yanzu kai ko kunya baka ji garin nan aji zaka kara aurar da yarinyar nan ga wani tsoho don kudi don abin hannun su kukewa kwadai.
Yanzu Asiya ni kike kallin idona kice saboda kwadan abin hannu nake aurar da yarinyar nan.
Inna ta ma rasa may zata ce da shi saboda takaicin daya rufe ta a lokacin.
Cikin bacin rai take cewa ai ba karya na fadi ba don duk wanda ma yaji haka yasan abinda kukewa ke nan.
Yanzu wancan auren abinda ta samu wa ya amfana dashi ba kai ba ina gidan ne kawai kila zata tsira dashi.
Don haka wallahi wanan karon bazan yarda da cin zalun din yarinyar nan da ake muna ba.
Har nawa yarinyar nan take da za, a dinga mata haka ina ga yayyin ta nan zube a gida su ko zancen su ba ayi.
Yace to tunda kin isa da ita duk matakin da zaki dauka kan wanan zance sai ki dauka mu gani tunda kin isa ke .
Wasa wasa magana har takai ga daga murya tsakanin su sai ga mama da ta dade tana sauraren su ta saka baki daga waje tana fadin
Malam kada ka biye mata kasan va hankali ke ga Asiya ba don son abinda yarta ke so ya rufe mata ido bata hangen abinda kaje ya dawo.
Cikin fushi baba yace mata ki kyale ni da ita Lauratu wallahi Asiya kin yi karya dake da yarki ku mai dani mutumin banza a gari.
Duk iskancin da budewan idon ku da kuke ganin kuna dashi yanzu baku kai ni ba don haka ku ci gaba da min rashin da, a ke da yar ki ku gani a gidan nan.
Indan kunce haka kuka dauko sai kun kwammace rashin zaman ku gidan nan dani.
Kallon shi Inna tayi shekeke tace dashi ai kasan kaine keda rayuwan mu a hannun ka .
Indai kan wanan zancen ne sai dai ajimu don nai magana akan hakkin ya ta ai ba haramun bane ko ?
Kuke samun riban auren da takeyi shi yasa kuke son kara tursasa mata sai tayi wanan din taje ta ciwo maku kasuwa gidan.
Duk masifan baba yana ganin ta haukace mai sai jikin shi yai sanyi yasan duk yadda akayi akwai abinda ta digora dashi take hakan don ba halinta bane haka.
Aikin banza inji mama tace may ye bamu sani ba wani dare ne kuma jemage bai gani ba.
Auren da sai anyi kifi kowa zakewa da jin dadi shine har za, a tsaya ana muna tijara akan shi.
Malam ka kwantar da hankalin ka kana nan zakaga yadda take rawan kafa da jiki ita a dole yarta ta samu gurin zama.
Idan ni ban yi rawan kafa ba ai ke sai kiyi tunda ke ma kina da yaya dakin ki sai ki bashi daya daga ciki a wuce gurin.
Tana fadin haka ta koma ta kwanta abinta tare da watsawa baba harara tana fadin don an mayar dakai haka bari a turo ka kai min cin mutunci ko.
Tun ranan da akai fadan nan ina wuta mama da baba su jefa mu ni da Innata.
Duk wani kule kulle da makirci shi mama take kullawa akan zancen sai cin kudin Jatau takeyi tana bushashan ta a cikin gida ita da diyan ta kawai.
Duk wani hanya da baba zai fahinta mama ta toshe shi har yakai ta fara dan fita zuwa gurin malaman ta wai a kulle muna baki duk mu ukun sai abinda tace kawai za, ayi.
Haka Inna take cikin tashin hankali kan zancen don ta fahinci idan bata yi da gaske ba babu makawa sai anyi wanan auren gamin gan bizan dani da Jatau.
Kullun tana hanyan gidan mama Altine kan magana daya duk tafita hayacin ta.
Gashi mama taci kudin shi yakai dubu ashirin da biyar tana karba wai tana bani tana kuma kamun kafa da sauran.
Bata san cewa komai nashi a lissafe yake mai ba don ba mutun ci ne dashi ba akan dukiyan shi ko kusa bai taka kafan Alhaji Garbati ba gurin tara abin hannun shi ba.
Amma mutane don baya ci sai suke gani yafi garbatin ma tara dukiya a garin.
Wata rana ina fitowa zan shiga gidan mama sai ganin shi nayi a kofan gidan mu don kusan a nan yake wuni.
Yana gani na ya fara washe baki ya na dan soshe soshe kamar mara gaskiya.
Ya dan tafo duduke kusa dani yana cewa a, a mutumiyar barka da fitowa ashe yau nazo a sa, a zan gan ki ashe ?
Wani kallo nai mai nace yauwa sannu baba .
Yayi dariya hakoran shi da wanda babu da rinanun sauran dake cikin bakin shi suka baiyyana a fili.
Cikin dariya yake cewa ai ni yanzu ba babane gurin ki zaki dai iya kira na da ango ango mai shirin shan mai ko ?
Nace tau ikon Allah baba aure ne zakayi halan ?
Kallon mamaki yai min yace kamar yaya kike tambayana haka kamar baki san da zancen ba kuma.
Na dan fadada fara, a na nace ban ko sani ba baba a ina kasamu matar ke nan ?
Yace ikon Allah gaki tsaye a gabana kike min wanan tambaya kuma ai ni yanzu nan da kika ganni jira kawai nake a shafa a tsakanin mu don har dukiyan aure na biya ko jiya.
Nace amma bakasan wace ka biya dukiyan akan ta ba ko don bani bace kake zance akai.
Ya sake kallona cikin mamaki yace ai ko ke din ce nan da sati biyu insha Allahu zaki tare a gida .
Dadai kin dan tsaya mun fahinci juna naji dan naki tsare tsaren don kin san shi marigayi garbati ya riga ya shagwabaki so sai.
Ban tsaya sake sauraren shi ba kada ya kara jefani wani sabon damuwa na shige gida abina na barshi nan yana kwala min kira kamar wani tsohon maye.
Na samu inna ta a waje ganin yanayin da na shigo gidan ciki yasa ta barin abinda takeyi tabini daki.
Ta samay ni zaune nayi tagumi sai hawaye nake zubarwa a idona babu sautin kuka.
Hankali a tashe take tambayana ke kuma da kika fita yanzu cikin dadin rai may ya dawo dake gidan haka ne kuma ?
Na dago idanuwa dake zubar da hawaye ina cewa Inna kinji mutanen nan ashe wai har sadakina baba ya karba hannun Jatau.
Cikin mamaki Inna tace yaushe akai hakan bamu da labarin komai akai nan dai ina kuka nake fada mata yadda mukayi da Jatau din dana fita.
Inna ta zuba min ido cike da tausayina domin tasan irin zafin da nake ji a lokacin take cewa.
Yarinya ki kwantar da hankalin ki insha Allahu ba a wanan auren idan kinga anyi shi sai dai bana raye.
Bari yanzu naje naga mamakin mai kuli musan abin yi tun kan mu makara akai.
Koda hakan na nufin rabuwa na da mahaufin ki ne sai dai mu rabu amma ba mai maki dole akai indai ina raye .
Na gaji da wanan mulkin mallakan da ake muna a gidan nan ya Isa hakana wallahi zasu gane basu da wayo wanan zubin.
Gidan mama ta fada muka shiga kusan tare a lokaci daya yadda mama ta gan mu tasan ba lafiya ba.
Nan Inna ta shiga zaiyano mata duk halin da ake ciki itama dai fada ta shiga yi da tsinuwan mama lauratu tana cewa.
Wanan karon saidai abinta ya koma mata amma Allah bai basu ikon yin hakan a kanki.
Mafita daya ne idan zaku iya da dare muje gidan maigari mu samay shi mu fada mai abinda ke faruwa don asaka ma abin waigi tun wuri.
Inna tace may zai hana ni zuwa indai zaki kaimu mai kuli ai mu mafita muke nema tako wani hanya indai hakan zai samu.
Kamar yadda suka shirya dare nayi Inna tace zata shiga gidan su ta gaida wanta da baida lafiya.
Lokacin ni dama ban dawo gida ba ina gidan mama Altine don anan zan kwana
Akai sa, a baba bai hana ba don dama yana son zasuyi magana da mama kan zancen auren gashi kuma kafa ya samu.
Inna na zuwa muka wuce zuwa gidan maigari mun samay shi yana cin abinci muka gaisa dashi da iyalin shi cikin mutum ci.
Sai da ya idar muka isa gurin shi nan mama Altine ta koro mai duk halin da ake ciki dani.
Ya kurkure baki tare da watsar da ruwan gefen shi yana cewa kai amma malam Audi baiyi ba wallahi.
Don ma dai Allah ya hada shi da yar aziki ne ya samu tai mai biyayan akan na farko yanzun kuma shine yake son lakaka mata wani.
Kada ku damu dama mun samu wanan dokan daga birni cewa babu auren dole ga yarinya ko yaro yanzu wanda kuma ya karya doka tara mai tsanani a kan shi.
Don haka kutafi gida gobe da safe insha Allahu zan nemay shi muyi magana dashi.
Mukai sallama dashi muka barshi yana fada yana cewa wasu mutane basu san ciwon kan su ba wallahi ko.
Ina jatau ina yarinyar nan ina zai kaita duk yadda zan fahintar da mahaifin ta illan abinda hakan zai haifar zanyi idan ya kiya kuma nai karan shi.
Hakan matan shi suka ci gaba da bashi labari akan zaman da Inba take a gidan dafin karfin ta da mama take a gidan tana mata mulki kama karya.
Tun da farar Safiya ake kwasa sallama a kofan gidan mu baba ya fita ganin ko waye ?
Sai yaron mai unguwa yagani nan yake fada mai ana neman shi a fada hankalin shi yai