Showing 135001 words to 138000 words out of 373688 words

Chapter 46 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

masu cewa, an fadawa Baban shi yana zuwa sayen taba harda dukan shi akayi kan hakan.
Kai mutane dai wallahi muna fukai ne yanzu har mahaifin ka,saida ya,samu wanan dan labarin kamar wani abin sheri can.
Nan suka,bada shawaran ya canza shago kawai inda baza,a sani ba yana zuwa.

****** ********* ******
Tun dawowan su ka fara karo da kwalayen da akai amfani dasu a dakin Maji na kayan da aka haka, duk da an kwashe anzubar da saura ga kuma shirgin kayan da aka fitar a inda suka barsu dazun.
Yaran su ne suke fada masu cewa yau basu nan an sha aiki a dakin Maji don an gyara mata dakin ta kamar na amarya.
Mama Asiya bata yarda ba saida ta shiga hardakin don ganewa idon ta abinda yaran ke fada masu.
Tun daga labulen falon tafara shock don bata ma taba ganin su ba da idon ta gidan kowa ba.
Kujerin da tai tozali dazune suka saka gaban ta wani irin faduwa, don tasan bana kasar nan bane da ganin su.
Juyawa tayi don babu kowa a falon bata tsaya ba sai dakin Umma wadda itama shigowan ta gidan ke nan a lokacin.
Yaya waiko kinga abinda idona yau yaganan min may kuma kika gani zaune takai tafara lissafawa Umma abinda tagani da idon ta.
Amma sai Umma bata dauki abin da muhinmanci ba ta zaci kawai idon Asiya ya rufe ne har take dada abinda akasa don ina zasu samu kudin irin abinda take fadin tagani a dakin Maijidda.
Maji da ta idar da adduoin ta da mika godiyan ta da neman tsari a gurin Allah tafito don yi masu sannu da zuwa.
Don kullun suka dawo dama sai tai masu sannu da dawowa bata gajiya duk da gwatsaleta da watarana sukeyi.
Har ta juya sai kuma ta tsaya tana cewa yaya baku nan fa abin arziki yau ya samay ni don dan ki ya sayo min kayan daki da kudin da ya samu.
Wani dan nawa Umma ta tambaya a gwatsale cikin basar wa maji tai murmushi tace dan ki sadauki mana.
Umm,uummm, dakin dai Maijidda tunda gashi uwarshi ya sani inda danane ai da ni zaiwa.
Tace idan kin huta sai kije ki gani ki samin albarka a ciki, ta juya ta fita zuaa gaida mama Asiya .
Itama ta fada mata yau abin arziki ya samay ta daga dan ta tazo tagani don Allah.
Nani kawai tace ba wani adfuan alheri akan wanda yayi din dama ita da tasamu din.
Hjy kubura dai dama sai yamma lis take shigowa gidan kullun koda kuwa sun tashi daga gurin aiki ne bata dawowa sai ta gama gantalin ta take shigowa gidan da yaran ta a gala baice da yunwa.
Maji tana shiga daki tafara cirewa kowa tsaraban shi kamar yadda suka tsara ita da diyan ta.
Matan gidan dai sun samu turamay yan ghana masu kyau da tsada turmi biyu, biyu sai yaran su maza bandir din shadda kowan su koda kuwa yaro karamine,
Yan matan kuma dogayen riguna da turamay suma aka basu, masu kyau sosai.
Nan gida ya kaure da surutu kowa da abinda yake fadi inda babu wanda yazo godiya cikin su sai yaran ne duk wanda akabawa zai zo yayi godiya da jin dadi masu bakin hali irin na uwayen sune basu shigo ba.
Hjy kubura da aka kai mata sakon cikin mamaki tace sadauki fa ya kawo muna wanan haka don harda kwallon da danta yaba da soko saida aka sayo mashi
Bata san da zancen gyaran dakin ba saida ta shiga taga ikon Allah dare daya Allah ya kai su gaba haka.
Tace may nake gani haka hjy maijidda kice min ci gaba yazo ke nan nan ta shiga sauran dakunan tana kallo tana kada kan ta cikin mamaki don bata taba zaton haka ba.
Falo ta dawo tana fadin kai Maijidda kin ko tambayi yaron nan akan kwallo ne ya samu wanan kudin haka?
An fa kashe kudi yakai miliyan biyu a nan ma kawai fa tanayi tana kara latsa kujerun don jin kwalitin su.
Tace ina dan nawa yake sarki yan kwallo ke nan ace mutum shigan farko ya dawo da haka.
Sai bayan ta mike take cewa ja iri yako tafi da dabun da nai mashi na tafiyan kuwa.
Maji tace ai yace yaji dadin danbun sosai shi uake ci ma a can yasha ruwa kawai don bai saba da irin abincin su ba sosai ,a lai kan naga alama.ai.
Tafita tana tunanen hitan su da yan office din su dazu da safe da suke cewa ashe dan kwallon gidan ku yadawo tace cikin tabe baki yadawa yadda yatafi shiririce mana.
Wanan dan iska wani tsiya dama zai tsinanowa mutane a can ban da tambadan daya saba nasan ya tafi yana shaye shayen shi sun koro shi.
Sai dayan dake rubutu take cewa ,a,a nifa naji kanina na fadin shine ma yazo na farko don ya samo kudi sosai wallahi.
Ba gaskiya bane wallahi yadda yaje haka ya dawo tsiya tsiya dashi wallahi don ina ga baiko maganin sisi ma.
Don ya samu wani abu da naji ko gurin Alhaji ne ko inga suna facaka ko ba abinda ya tsinano.
Sai daya tace balle ma mashayi kafin fa suyi sai an bincike su agani idan kana shaye shaye basu yarda ka buga kwallo yanzu.
Balle ma bai samo komai ba suna dai ganin hakane tunda ya tafi har wani kasa yin wasa.
Sai gashi ta dawo gida ta samu zancen abokiyar aikin ta ashe gaskiya ne ke nan boyon kurwa yai masu dama.
Maji dai ta rakata da harara tana fadin muguwa aniyar ki tabiki dakin ki munafuka yar sheri, Allah ya shirye ki kawai.
Maji tace wa Amira gobe ina son a kwashe tsofin kayan nan akai wa mai masa gidan ta ita ma,ta canza.
Nan Bintu tafara murna tana godiya kafin hjy masa tazo tayi mai karfi da bakin ta.
Sai da yamma da Alhaji yadawo ya samu wanan labarin gurin mama Asiya da ta fara tsegunta mashi ciki tsigar gulma.
Yace masha Allahu kai amma ko naiwa maijidda murna haihuwa ta fara rana ke nan yau Allah ya amsa mata adduan ta .
Sai ga maji da nashi tsaraban shaddoji da su turare masu tsada ta zube mashi su a gefen kujeran da yake zaune.
Ya kalleta cikin murmushi yana fadin yanzu Asiya take fada min abin arzikin da ya samay ki ashe sadauki ya fara fitar da uwarshi.
Maji tai murmushi tace kai haba Alhaji kai kuma da kanka zakai min sheri kuma.
Suna cikin magana sai ga hjy Bintu dauke da tsaraban ta dana yaran ta tana ta faman washe baki tana fadin ga abin arzikin da mutanen ghana suka kawo muna.
Yace mata nima kinga ga nawa nan yanzu aka kawo min shi ko dubawa ban gama ba.
Mama Asiya mai girki tashigo ganin kayan hjy Kubura dana yaran ta yasa take kallo don taga sun fi yawa ga idon ta.
Nan take cewa hmm muma fa anbamu har yaran nan gaba dayan mu gidan.
Masha Allahu inji Alhajin ya fadi yana mai kai ruwa a bakin shi yace haka ake son samu idan ka samu kowa ma yasan kasamu cikin yan uwan ka.
Yana gama cin abinci ya nufi dakin Maji don yaga abinda ake ta faman zuzutawa,
Yako gani kuma yai murna da farin ciki sosai sai faman sawa dan shi albarka yakeyi.
Bayan fitan su Amira tace ikon Allah yau Baba ne da kan shi kewa yaya sadauki wanan adduan haka.
Amma da can an zuga shi a kan shi sai faman cin mutunci da tonon asiri yakewa mutane a tsakar gida.
Maji take ce mata wanan ai haka yake duk uwa mai haihuwa sai ta samu bacin ran mahaifi akan dan ta watarana.
Don duk abinda yayi mara kyau laifin uwa ne maikyaune na uba ni dai na godewa Allah daya takaita min wanan bakin cikin da wuri.
Maryam dake kunna tv take cewa amma ai basu daina kiran shi da sunan mashayi ko?
Don ko dazun naji Umma tana fadin wai tsaraban yan shaye shaye suka samu take fadawa yaya Imirana da ya shigo.
Ba sai ta dawo dashi ba tunda bata son kayan mashayi da aka bata maganan banza kawai.
Maji dai shiru tayi batace masu uffan ba har suka gaji sukai shiru.
Da safe ne sadauki yaba mahaifin shi check din kudi yace yana so ya fara noma dashi ko za,a samu anan ma din
Bayan Alhaji ya karbi kudin yaga yawan su yake cewa sadauki duk wanan kudin haka akan kwallone kawai ka samay su.
Ya dan dukar da kan shi a kasa yace Baba a nan na samay su don ma ban yarda bane da,har wasu club sun so su sayeni amma,nace masu a,a subarni cikin club dina kawai har gaba.
Ikon Allah ashe Alhaji Sani gaskiya yake fada min cewa idan nai hakkuri Allah yasa maka hannu watarana sai na dara akan kwallon ka.
Murmushi kawai sadauki yayi ba cewa mahaifin nashi komai ba yana fita hjy kubura tana shigowa suka gaisa dashi ya fita.
Alhaji ke ce mata kingani ikon Allah kudi sadauki ya kawo min wai na fara noma dashi.
Maimakon yaji tayi murna yadda ya zata sai ji yayi tace Alhji adai binciki a gani wanan harkan amma abin yai yawa wallahi.
Ya juyo cikin mamaki yana kallonta yake cewa ban gane hausan ki ba fa kubura.
Tace ni gani nayi kamar wanan kudin sunyi yawa ace duk a saboda kwallo aka samo su haka gaskiya abincika dai aji.
Yace to kina ganin kamar da akwai wata a kasa ke nan ko ya tambaye ta don son jin may zatace.
Tace gaskiya kasan halin dan yau fa kada ya yaudare ku da,wasan kwallo ya fada wani harka na tir da Allah waddai.
Cikin mamakin jin abinda ta fadi yace assha kubura ban zaci jin wanan magana daga bakin kiba wallahi.
Sai lokacin ta tuna tayi barambarama fa don mahaifi mahaifine ai,da sauri ta gyara zancen tana cewa a,a ba wani abu nake nufi ba kasan halin dan yau ne shi yasa na ce a dai bincika kawai ba wani abu ba.
Nan dai taita kamay kamay ta tafita shi dai yana jin ta kawai baice mata komai.
Kwana biyu sai gashi zance na yawo a gari da unguwa wai ya samu kudi ba,a san inda yasamo ba sai facali yake iyayyen shi suna jin dadi.
Wasu suce wai ba kwallo aka dauke shi ba zuwa akayi dasu suka fita da kwaya kasan waje shine aka fake da kwallo kafa.
Maji dai da zancen yazo kunnen ta da farko ta so tayar da hankalin ta don sai da ta tsure sadauki a dakin ta take tambayan shi gaskiyan zancen abinda taji.
Murmushi shi na rabin fuska kawai yayi mata yace haba Maji idan wani ya fadi an yarda aike bai kamata ki yarda da wanan zancen ba don kin fi kowa sanin halina.
Ban son raini da wullakanci shiya sa na roki Allah yai min mafita na dogara da kaina.
Nan dai hankalin ta ya kwanta tace koma,waye yai muna wanan sherin mun barshi da Allah shikw nan.
Takara ja mashi kunne akan ya futar da ita da yan uwan shi daga kunyan duniya don mutane yanzu ake kiwo ba dabbobi ba.
Bata hakkura ba ranan da take da girki ma saida ta samu maigidan su da wanan zancen.
Yace au kema ashe zancen yazo kunnen ki amma ya kamata ace kin san halin abinda kika haifa.
Ni ban ji ko dar ba akan maganan nasan kawai hassada ne irin ta mutanen yanzu kawai.
Amma ai watarana gaskiya zatai halin ta don shi kwallo ba,sanar boye bace duniya tana sanin mutum a lokaci guda.
Ki dai yi mashi fada yai tanadi kada yaga kudi suna shigo mashi haka dayawa lokaci guda yace zai bullo da shashanci cikin rayuwan shi.
Haka yasa tattara zancen ta watsar tabar masu hassada akan danta suna zuba mashi taki.

****** ********* ******
Sadauki yana zaune a cikin falon Maji duk kannen shi sun tafi makaranta sai ita dake final exam din ta yanzu.
Wayan shi yake dakila ta hanyar yin game da ita,Bintu tafito daga cikin dakin kwanan su bata san da yana falon zaune ba a lokacin.
Tana saye da da dogon riga na atamfa a jikin ta, style din dinkin da akaiwa rigar yai matukar mata kyau a jikin ta.
Tunda ta sanyo kai falon ta gashin a zaune sai taji gaban ta ya fadi don a rayuwan ta ta tsani ta gan shi a falon zaune don yawan takuran da takeyi.
Jin motsin da yayi a zaton shi ko Maji ce tafito daga cikin dakin yasa shi daga kai ya kalleta.
Bintu ce ya gani tana kokarin komawa cikin dakin da tafito din,cikin sauri.
Yace cikin daure fuska ke zo nan kina abu kamar muna fuka dake, cak taja ta tsaya tare da juyowa inda yake zaune.
Yace ina Maji take ne ban ji motsinta ba ya tambaya cikin ci gaba da latsan wayar shi .
Tana dakin Baba tana gyarawa amma yanzun zata dawo,,,
Hannu ya daga mata yana fadin ban tambayeki ba bani abinci na naci yace cikin gadara da daure fuskan shi.
Haka ta karasa fitowa ta gaban shi ta wuce ba don taso ba inda yabi bayan ta da dan tsuki yana fadi a ranshi jita dan Allah kamar zata kare, mace haka ba kiba ko kadan.
Tafito da abincin cikin sabon kulan shi da ake saka mai abinci ta aje a gaban shi ta juya zata dauko ruwa ya kara binta da kallon haushi.
Yadan kara jan guntun tsuki wanda yai daidai da shigowan Maji falon, tace, a,a Baba na kai dawa kuma ke wanan tsuki haka kai kadai?
Yace kai tsaye ni da wanan yar kauyen mana tafito taganni shine kuma wai zata gudu anya maji yarinyar nan kuwa tana da gaskiya ya fadi tare da,dago kan shi yana kallon Maji.
Wani kallon da yaga tana mashi yasa shi shan jinin jikin shi ta,wuce zuwa ciki ta aje kayan dake hannunta.
Jima kadan tafito ta zauna tana fuskantar shi tace gaskiya banjin dadin irin yadda kakewa yarinyar nan,
Ko banza taci albarkaci na nida na ajeta a gurina bawai bata da gata bane a,a itama tana da gatan ta rayuwane kawai yasa ka ganta anan din.
Amma yarinya tana tsaye tana iya kokarinta a kan mu kai kuma,sai binta da hattara kakeyi da wani zataji na rashin iyayyenta kusa da ita ko kuwa da halinka zataji.
Ban son karatun yarinyar nan ya tsaya ne shiyasa kaga ana ajeta a gurina don itama watarana iyayyenta suyi alfahari da ita.
Ashe ba dadin ku bane yau ace a sanafin mu ta zama wani abu a duniya, ban rokeka komai don na tallafa mata ba.
Amma kasa yar mutane gaba haka da tsangwama tare da hattara ba yau ba ina lura balain tsoron ka fatima takeyi wallahi.
Wani kunci ne yaji ya rufe shi a ranshi ya mike ba tare da ya gama cin abincin da yake ci ba ya bar falon cikin fushi.
Maju da tabishi da kallo ta,tsuki tace sha sha kawai mara hankali mutane suna bakin cikin zaman ta anan kaikuma kace zaka tsiro min da naka kalar tsiyar a kanta.
Tsayin sati daya sadauki yana fushi a kan maganan gashi ya hana Bintu sakat a sashin nasu don da ya shigo ya kama hararan ta ke nan da kuma tsuki.
Allah Allah Bintu keyi ta gama exam tabi gwagonta kauyen su don dama zaman dole take a gidan.
Hankalinta yana gurin iyayyen ta da yan uwan ta don tunda tazo bataje gida ba,bata kuma ga kowa ba cikin su sai gwago dakan dan zo ta kwana biyu ta koma.
Allah ya taimaketa kafin su gama exam aka kirasu Abuja inda ya kwashi komatsen shi yanufi gurin kiran da akai masu.
Hakan ya,dan ba Bintu daman sake jikin ta har maji ta fahince ta tafi sake jikin ta idan baya nan ke nan.
Amma tana gama exam ta fito da zancen son zuwa gida don tagano yan uwanta.
Hankalin Maji yai matukar tashi a lokacin inda take tambayan ta cikin lalashi ko an mata wani abine take son zuwa gida.
Bintu tace cikin sanyi murya da,sauri a,a mama ba ai min komai ba ina dai son zuwa,nagan su ne tunda nazo banje gida ba shiyasa nake son zuwa nagano babana da yan uwana.
Maji ta sauke ajiyan zuciya tare da,tambayan idan kin tafi yaushe zaki dawo Fatima?
Don nasan ko kwana,nawa zakiyi acan saboda na tura a dauko ki in lokaci yayi.
Bintu tana,wasa da yan tsunta,da,harde su guri guda tana cewa mama sai na tafi tukun don ban san hukuncin da mahaifina zai yanke a kaina ba yanzu tunda na gama karatu na ko.
A,a Fatima idan hakane ki bari mu tafi tare sai mu kwana daya mu dawo, tare.
Da sauri Bintu ta dago kai tana fadin mama har gurin mahaifiyata nake son zuwa don mun dade bamu ga juna,ba da ita.
Eh to


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login