Showing 306001 words to 309000 words out of 373688 words
Chapter 103 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
Allah ya nufe da mai shaye shayen da baida ranan barin shi a rayuwan shi.
Yana sauraren maganan da nake fadi sai dai baiyi magana ba har lokacin karshe ji nayi barci ya dauke shi.
Har na mike na shiga bathroom nai wanka nafito nai nafila na zauna ina kara kai kukana ga Allah akan al,amarin nashi.
Nagaji na taso daga inda nake na kwanta daga gefen gadon nan nima barci ya dauke ni ban sani ba ina cikin tunane.
Da safe ko da na falka na samu yafita daga dakin bai kuma tadani ba don ganin da yayi ina barci a lokacin saboda yasan ban samu barci ba a daren jiya din.
Bayan na sallah na kimtsa jikina na shiga kitchen na hada abin karyawa na jera su atable na shige daki abina na kwanta.
Har ya gama abinda yake ba alama na a falon haka yasa shi leka dakin kwance nake rub da ciki kamar mai barci sai dai yasan ba barci nakeyi ba a lokacin.
Daga kofa yake ce min shi zai fita sai yadawo ban dago ba kuma banyi magana ba haka yasake labule yafice daga gidan.
Jin fitan shi yasani fitowa daga daki na gyara ko ina nagidan tsab na dora muna abincin rana again.
Bai shigo ba sai bayan la,asar naji shigowan shi ya shige dakin shi ina zaune ya shigo cikin shirin shi yana cewa ni zan tafi ga wanan ki rike a gannun ki sai badawo.
Da kyat na iya bude bakina nai mashi adawo lafiya yafita daga gidan ranan ban rakashi ba yadda na saba yi mai wanan abin ya kara bata mai rai.
Sai washe garine yaya Bashar suka zo gidan da maryam mun gaisa da su muna zaune tana min sheri wai na kore mata yaya a gari saboda halina.
Idona ya kawo kwalla nace cikin wata murya ta mai kararen zuciya haba anty don kawai baison a fada mashi gaskiya kawai.
Muryan bashar ne yake cewa Fatima kiyi hakkuri shi kan shi yasan bai kyauta maki ba kuma yaji nauyi da kunya da ya sani.
Hakan da kikai mai kin kyauta gara da kika rufe idon ki kikanuna mashi abinda yayi ba alheri bane.
Don idan mutum yana aikata barna a doron kasa bai samu wanda zai rufe ido ya fada mai gaskiya ba komai dacin shi sunan wanan mutum din tabbabe wallahi don baida ranan daina a rayuwan shi.
Amma kuma ke kuma kin tauye shi da yawa Fatima kin hana mashi hakkin shi bayan kin saba farauta mashi.
Kunyan maganan shi naji na saddada kaina akasa yace gaskiya kin hora min abokina wallahi.
Yace ko yar kwaliyan da kike mai da taro haba haba duk kin daina yi mashi su haba Fatima adai dan sasauta mashi mana.
Maryam tai tsagal tace akan may zatai mashi tunda shi baisan ciwon kan shi ba har yanzu ba gara ta kama kan ta ba.
Yace to gama dama ai yace shawaran ku daya da ita kece coordinater din ta.
Dariya mukayi nace babu ruwan anty kada yaga laifin ta a banza bataci batasha ba halin shi daine bai min ba yaya.
Yace to kiyi hakkuri Fatima tinda dashi Allah ya hada ki zama nifa ina ji ajikina insha Allahu zai daina nan gaba.
Tinda kinga yanzu yarage sosai inda dane ai abin ba dama wallahi don baku san irin halin da na shiga dashi bane a baya kafin ya aure ki.
Amma aikinyi sa,a ma yana shayin ki yana tsoron yayi ki gane ko ranan ina ganin akasi aka samu kawai.
Duk wanda yai mai asiri bai fasa ba mai shi yana kan yi har yanzu don dai suga ya lalace kawai a rayuwan shi.
Maryam tace ina fa suka fasa kwanaki da nafisa tai shaye shayen ta ai ta fadi amma aka mayar da abin haukan tane kawai yatashi take fadin hakan.
Bashar yace ai zan koma gur8n mutumin nan da muka taba zuwa don wallahi Alokacin ya daina kwatakwata dawowa abin yayi.
Kuma zan fada maki wani sirin shi idan yana son sha zagiga idon shi sun rine sunyi ja jajir dasu yana dafe kan shi yana dan murzawa to yana sin yasha ke nan.
Kuma ko a gidan yana da kayan maye har na shayin su da yake sa kina dafa mashi da hannunki amma ke baki sani ba.
Nazaro ido nace wallahi ko duk dare yaya sai na dafa mashi bakin shayi mara sugar da madara yasha.
Yace to sune yake sha yanzun dai kafin ya dawo insha Allahu zan koma kauyen nan naji may ke ciki akan al,amarin don idan akwai wanda zaki bashi yaci batare da yasani ba sai ki hada mai.
Nace nagode kwarai yaya yace kiyi hakkuri kinji ban son mama taji wanan zancen ko kadan don kada ciwon ta ya tashi.
Nace nima shine wallahi amma badon mama ba ranan wallahi dana gudu gidan nan yaya.
Yace no no don Allah kada kije ko ina kefa haske ne a gare shi Fatima.
Zamaki tare da Sadauki wani falala ne ga kowa ga masu gadinku suna fada min irin alherin da yake masu akan ki.
Idan kinyi haka mama bazata ji dadi ba masu hassada akan auren ku kuma zasuyi farin ciki sosai.
Maryam tace ai bata ma zuwa ko ina mutu ka raba ita da yaya sadauki sai dai yan bakin ciki su mutu.
Mun kai wani lokaci dasu suna bani shawaran yadda zan kara bullowa al,amarin.
Sukace zasu tafi don zasu shiga gaida Inna gidan ta a lokacin nai masu rakiya har waje suka tafi yaya bashar yace yace akawo maki kayan abinci sai gobe za,a shigo dasu don ina ganin zai dade a can ne.
Har ya shiga mota yake cewa kin ko kirashi kinji saukan shi na dukar da kaina ina dariya yace don Allah ki kirashi nace mashi to kawai .
Amma bazan kiraba nace a cikin zuciyata indan yadamu yakirani in kuma bai kira ba ajira har ranan da ya dawo din.
Jin za,a kawo min wasu kayan abinci na shiga kitchen na auna shinkafa da taliya don tun na garan mu sunanan ba ai komai dasu ba na kira malam Atiku na bashi kowan su leda guda guda da dubu uku uku na cefane akan Allah ya yaye mai wanan lurar tashi.
Suna ta godiya suka fice kowa yakai nashi gida don dama a bukace suke a lokacin don abin sai shukaran kawai.
Na idar da sallah la,asar naji anata kwada sallama daga kofa nafito ina karba sallah ma.
Na so sheda matar amma na manta ida na san ta a baya muka gaisa da ita cikin sakin fuska take ce min baki gane ni ba ko hajiya ?
Nace na dai so na gane ki tace Allah sarki yanzu maji tai min waya wai nazo na zauna dake don maigidan bayanan kuma tace ma zata bugo maki waya ai.
Nine Rabin dan musa uwar goyon sadauki a baya nace cikin sakin fuska Allah sarki wallahi mama ban gane ki ba saudaya na taba ganin ki ranan da kika zo gaida mama ina gida lokacin.
Na mike tare da amsan ledan bakon dake a hannun ta na shiga mata dashi dayan dakin da anty Amira ke sauka a cikin shi.
Nace mata ga daki nan inda zaki zauna mama tana washe baki tace ai da ko nan kika barni ma yayi min wallahi ko.
Nace kai haba dai nan a waje mama tace ina wajen yake nan na je na kawo mata abincin mai yawa taci sai da ta koshi tana godiya.
Mun dayi hira sai da magariba ya gabato muka shiga daki don yin alwala da sallah.
Da dare ma mun dan taba hira da ita take ta bani labarin irin zaman da akayi a baya a gidan su sadauki yadda maji tasha wuyan su Umma da mama a baya.
Sai zuwa goma mukaiwa juna sai da safe kowa yanufi dakin shi ya kwanta.
Washegari kafin duk ince nafito na samu ta gyara gidan tas ta goge ko ina tai wanke wanke nace bayan mun gaisa haba mama baki huta ba kuma wanan aikin haka tace min haba to may yakawo ni gurin ki ba don na taimaka maki ba na zauna kuma ina kallon ki haka uwar dakina.
Tun ranan itace mai gyara gida iyakata nai muna girki kawai wanda zamuci ko girkin ma tace bata iya ba da abinda mukeyi sai da icce amma in koya mata don watarana.
Shine dalin idan zanyi girki muke shiga kitchen da ita tana kallon yadda nake aiyuka na.
Yau satin shi daya da tafiya baikirani ba ban kirashi ba muna zaune a falo da Iya take ce min wai ke yar nan ni banji kuna waya da maigidan ba mana.
Sai da na kakaro murmushi a fuskana don tambayan nata yazo min a bazata lokacin .
Narasa may zance mata sai nace cikin murmushi lah iya ai shi sai tsakandare yake bugo waya kin san lokacin mu ba daya bane dasu can namuna rana sukuma suna dare ne.
Tace Allah sarki ni kan dai ince yaran yanzu baku wasa da waya da mazajen ku shiyasa na tambaya ai.
Takara cewa ba dai dan nawa yana lafiya ba dai ko nace lafiya yake yana ma yawan tambayan ki na ce mai kalau ki ke.
Tun da na fadawa Iya Rabi haka shikenan bata sake tambayana komai a kan shi ba kuma.
Abu kamar wasa yau satin sadauki biyu rabon shi da gida amma ba waya daga gare shi da farko abin bai damuna amma daga baya sai abin ya fara ci min rai kuma.
Mun shiga daki kenan munyi sallama da iya Rabi sai naji wayana yana ringing da sauri na isa furin don na dauka murja ce wata course mate dina da muka dan shaku da ita.
Nobar kasar waje ne daga US na dauka da sallama a bakina naji ya amsa sallaman nawa cikin wani murya.
Sai kuma mukai shiru gaba dayan mu can yake cewa Fatima yanzun kan na sheda dole akai maki a kaina don yadda kika nuna baki damu ba dani.
Nace dole dai akai muna da juna aikama kasan kabar mai gadi gidan ka baka damu dani ba.
Hmm naji yace yace wanan kuma mafanan ki na rasa ke wata irin yarinyace haka mai taurin kai dake.
Kina nufin idan munzuba ni dake waye zai sha wuya a cikin mu ne wai kefa mace ce ba kowa ba.
Nace oh don ina mace shine akace ban san right dina ba ko komay ?
Idan kina ganin halin da kika dauko yi min zai sa na daina abinda kike ganin zan daina sai ki matsayi ai gafili ga mai doki.
Nace ban ma son ka bari don ni ai nafison kabari don Allah da iyayyen ka da zurian ka masu zuwa.
Yace oh ashe kin sani kik matsawa wa kanki nace ni ban matsawa kaina da komai ba sai dai kawai ina tsoron mu,amulane da wanda baida tsoron Allah kawai.
Yace na gode nima haka nabashi amsa sai naji ya furzo iska yake cewa ance Rabin dan musa na gurin ki ko ?
Nace oh iyaba tananan yanzun ma ta kwanta don muna tare yace ok ina son ki kula da ita sosai don tana da mutunci sosai nace insha Allahu zanyi yadda kace.
Bashar ta kawo maki kayan abinci nace eh amma kasa akwai su dama kuma ka karo wasu shiya sa na diba wanda muke dashi na ba su maigadin ka su ma yace ok haka yana da kyau idan kuna da wani matsala dai bashar yana nan sai ki fada mai ko ma may ye.
Nace bamu da matsalan komai don iya tana da kirki matuka kuma tana debe min kewa sosai a zaman kadaici.
Murmushi naji yadan yi yace akwaita da,son hira ai sai kingaji kintashi inda Rabi ce.
Na katse shi da cewa ina fatan kana wa kanka adalci acan ka daina wanan shan mugun abin mai bata maka tunanen ka akan komai.
Tsaki naji yaja yace yacd ai da kika damu da hakan da sai ki shigo jirgi ki gani don gulma ko ?
Yace kin ga malama idan kikace zaki saka min ido haka arayuwa na wahala zakisha wallahi.
Raina ya baci da kalamin shi nace dama ai zaman wahalan aka kawo ni yi don raina yai ta baci a banza tunda ba fasawa zakayi ba kai.
Amma kin san ko ni waye kika yarda aka daura ni dake haka na ko don kin ga ban maki yadda na kulla ba shine har kike jin dadin samun gurin ke ki cutata min ko ?
Naga idan ban kashe watan ba haka zamuyi sa insa dashi akan zancen yasani kashe wayan dip na ji dul jikina ya mutu a lokaci guda.
Mikewa nayi na ahiga wanka na dauro alwala raina duk abace ina ta faman tune watau shi wanan dai bazai daina halin nashi ba ke nan yake nufi tinda da anyi zancen fitina yazo ke nan dashi.
Washe gari da safe yaya bashar ya samay mu da iya mun gaisa da yake iya mace mai fahinta sai taba guri dashi.
Wasu kulin magani ya ciro daga aljihun shi ya kashe murya yana min bayani yadda zan yi da maganin idan yadawo sosai nai mashi godiya da fatan Allah yasa mu dace gare shi yace amin ya kara jadda mi na tabbatar da na zuba mashi fa yaci sosai nace insha Allahu nai murna kwarai sai nake gani kamar har maganin yaci ko a lokacin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA NA,BARKI GA ALLAH,ALLAH SHI ZAI KARBA MIN HAKKINA A GARE KI ,,,,,
Saura yan kwanaki a fara azumin watan ramadan ko ina,kasa shen musulmai sai shirye shiryen taron wanan wata mai alfarma da albarka dake tafe a,wanan lokacin aketayi manya da yara da,tsofi duk farin ciki suke da wanan wata mai albarka .
Zan iya cewa rashi dawowan sadauki a cikin lokacin da nake gani kamar har za a kama a azumi bai dawo ba garin a lokacin.
Babu wani abin da na rasa,a gidan daga na ci da,sha da sauran abubuwa amma kuma sai na kasa gane may ke yawan haddasa min bacin rai haka na rasa ganewa.
Gidan baba sai abin arziki yake samu daga diya da sarakain shi da,abokan arziki na gari.
Ba kunya mama take habaici wa baba wai gashi dan na shi bai kawo ba amma fa wa yanda ba,a so sun kawo don sune ,ba,a so da alheri gashi Allah ya hore masu sin kawo mashi ya karba yana washe baki .
Kai tun abin yana damuna har yakai yanzu na daina damuwa da rashin dawowan shi wanda wata biyu.ke nan rabon shi da gida.
Sai yaya bashar mijin maryam abokin shi shine kawai ke dawainiya da mu tako wani fanni duk da,ban taba cewa muna bukatan wani abuba a gidan na rayuwa.
Maryan yanzu cikin ta yakai wata biyar ke nan a jikin ta don har ya turo sosai mutum zai iya gane haka atare da ita duk cikin mu ita kadaice Allah yabawa haihuwa.
Da kafa takan tako daga gidan ta zuwa gidan mu don motsa jikin ta idan zata koma tare muke fita har Iya mu taka mata mu rakata gidan ta don bamu da nisa sosai.
Da dare muna cikin falo zaune ni da Iyan Rabi muna hira waja jen karfe tara na dare a lokacin .
Sai jin sallama mukayi kamar daga sama muka ganshi har ya shigo tsakiyan falon a lokacin.
Sadauki ne ya shigo muna gidan da sallaman shi ya murje yayi wani kyau yayi haske kamar wani dan kwara dashi.
Cikin fara,an shi da walwala ya shigo muna a lokacin daga ni har Iya sai sannu da zuwa muke mashi a lokacin.
Ganin da nayi fuskan shi a sake yake, yasani nima taron shi a cikin farin ciki kamar babu komai a tsakanin mu can baya.
Zama yayi saman kujera tare da fadin wassh Allah Iya tace sannu na wurina da kokari andawo yaya hanya yaya aiki da sauran jaman can.
Na,dawo daga,kai jakar kayan shi daki na nufo shi tare da dan dukawa na rugumoshi ban damu da wai iya tana gurin ba shima dai rungumoni yayi zuwa jikin shi.
Iya dai kunya taji ta juya zuwa kitchen abinta tana murmushin yadda taga mun burge ta sosai a yanayin mu.
Zauna da ni yayi saman cinyan shi yana sauke numfashi tare da kai hannun shi a saman wuyana a hankali yana dan shafawa cikin lumshe idanuwan shi.
Daga inda Iyatake a tsaye take cewa uwar dakina nace ko sabon girki zamu dorawa yaron nawa ne ?
Itace tadawo muna da hankalin mu muka tuna a inda muke zaune a lokacin.
Da,sauri yace a,a kubar shi kawai zan sa,akawo abinda zanci yanzunan kafin nai wanka.
Mikewa nayi daga cinyan shi nake cewa Iya zo zauna ki huta abinki ai dan naki bai faye danuwa da abinci ba idan bashi yaso ci ba kuma bama komai ne yake ci ba shi dole yanzun sallon abincin mu ya canza ai .
Maimakon tazo ta zauna sai ta shiga dakin ta yana tambayana yaya muke yazaman mu da Rabin dan musa nace bata da wani matsala wallahi ita ai mutum ce mai dadin zama ga tsabta ga aiki