Showing 255001 words to 258000 words out of 373688 words

Chapter 86 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

Advertisement

irin wanan ddaga gare ka tun tuni.
Akan mama zan iya hakkuri da duk wani cin zarafin da zakai min matsawon hakan zai mata dadi a ran ta.
Don nasan darajan mama nasan kimar mata a rayuwana kuma ban manta da irin halarcin da tai min ba a baya.
Don haka kaga tunda wanan ne kadai hayan da take ganin zan iya saka mata da alherin da tai, min ashirye nake da na rugumi duk wani kaddaran da zan tunkara a gidan ka.
Fita min daga daki yar kauyen banza kawai mara tarbiya wace bata san komai ba sai rashin kunya.
Nace nagode na gyara hijjab dina na fito daga dakin, idona taff da hawaye, sai da na saita kaina na shiga cikin gida.
Dakin mu na koma na kwatan ina tunanen makomar wanan auren da ake shirin kullawa a tsakanin mu a haka.
Ni dake fanin da safe zamu tafi sai gamu sai sha biyu da rabi na rana muka bar sokoto zuwa kauyen mu.
Tare da rakiyan yan uwan mama da suka zo daga Niger state gurin buki sai kawaye na muyi yan layin mune kuma school din mu daya dasu tun secondary school muke tare dasu.
Mun samu gidan mu ya cika makil da yan uwa da abokan arziki, da suka zo gurin buki nai matukar mamaki yadda na samu an gyara gidan mu a lokaci guda haka.
Dakin da zamu zauna an saka katifa maya guda biyu a cikin shi, nan muka sauka bakin da muka zo dasu basu dade ba suka koma don akwai event din da za,ayi na matar Ahmad gidan su suna son zuwa.
Sai bayan mun hutane nake jin wai mamana tana gari ta zo amma tana gidan su.
Da yamma aka sakani lalai kamar yadda al,ada yake a garin mu nan aka shiga shagalin buki, sai abinci ake ta faman tukawa na farar shinkafa.
Muma munzo da kayan cima da abokaina zasuyi amfani dashi a garin don haka ba sha wani wahala ba sosai.
Sai da safe naje gaida mahaifina yake ce min Fatima Bintu kinzo kin samu alherin da mutanen arzikin nan sukai muna a gida nan ko?
Alhaji ya aiko daga can birni an gyara muna guri don baki masu zuwa daurin aure sai kuma jiya gashi da safe kafin ku iso anzo da abinci da katifo wai daga marikiyar taki ta aiko dashi.
Nace an gode Baba ya ce tau Fatima sai dai ban tsanmanin zamu kara samun lokaci irin haka dake ba.
Abinda nake son ki sani shine shi zaman aure dan hakkuri ne don yanzu so ya kare a tsakanin ku sai hakkuri.
Yi nayi bari na bari inji manya sai a zauna lafiya, kin dai san ance mijinki mutum mutane ne gashi kuma dan gidan yawa.
Don haka ki zauna da kowa da halin ki duk da nasan ki amma ki kara da hakkuri Fatima, shi hakkuri baya karewa fa musulmi.
Duk da a hasashe na ina fanin kaman wanan aure aure ne na hadin iyayye a tsakanin ku dashi halinki shiya ha har suka kwaidaitu da son zaman ki da dan su.
Don haka ki kara wani saman wanda suka sanki dashi sai kiga akarshe ke ce da riban hakkuri.
Take naji idona ya ciko da hawaye har na kasa control din su sai da suka zubo min nan dai baba yaita min nasiha akan hakkuri da zamantakewan aure da kuma sabon rayuwan da zan shiga ciki.
Mukai sallama dashi yana ta saka min albarka tare da fatan samun zuria dayyaba.
Yinin ranan haka nayi shi a kwace babu walwala tare da ni ga mutane sai masha,an da sukeyi kawai.
Da dare gwagona mai masa tazo tace nazo mu tafi gidan su mahaifiya na don ko can akwai yan uwa da suka zo buki.
Mun shiga gidan mutane sai jin dadin gani sukeyi suna ga amarya tazo gaida ku.
Nan muka shiga gaisawa da mutanen da na dade banga wasu ba sai ranan.
Sai wani lokaci na samu kebewa da mahaifiyana a wani daki dagani sai ita muka zauna a dakin.
Tace tau yarinyar ga gashi dai Allah yayi zaki aure yanzu don Allah idan kin je kiyi hakkuri da sabon rayuwan da zaki tsunta a sabon gidan ki.
Ance zo mu zauna zo mu saba ne sai dai mu mata da hakkuri aka san mu dan namu yafi na maza don mune a kasa garesu.
Kina dai ganin irin rayuwan da nake ciki ba sai na fada maki ba kin san hakkuri nake dashi don da ban hakkuri da tuni nabar gidan nan na,watsar da yaran nan.
Amma sai naga idan na fita na barsu dawa kuma zasu zauna har ya basu tarbiyan da nake son su samu saboda kinga shi wanan ba irin naki mahaifin bane.
Ina jin haka sai wani irin kuka mai karfi yazo min don tausayin mama na dani kaina.
Da kyat ta dan lalashe ni na sasauta cikin kuka nace mama ina ganin kusan rayuwa guda Allah ya jefo muna na aure.
Don kinga shima din mashayi ne ne kaman baban su musa sai dai dan banbancin su kadan ne don akwai wayewa a cikin nashi.
Mama bana son shi na tsane shi natsane shi a rayuwa na amma sai gashi magaifiyan shi ta nemi alfarma a guri na akan na rufa mata asiri na aure shi.
Mama may zanyi da mutumin da bayaji tsoron sabawa Allah bai dauki sabawa Allah a bakin komai ba.
Mama don mahaifiyan sadauki zanyi wanan auren don ba zan iya mussa mata fa bukatan taba a gare ni.
Mama ta katse ni tace amma kin bani kunya wallahi yarinyar ga ina iliminki da tarbiyan ki ya shiga da har kike ganin ba zaki iya taimakawa hajiya ba yau.
Tace da kikaga hjy ta zaboki a cikin dubu ta bukaci ki auri dan ta kina zaton don kyau kine ko arzikin ki ko wani abu can.
Tayi hakane don tana hasashe watakila tagare ki zata samu nasaran raba dan ta da waban halaiyar tashi.
Bafa don bata sonki ne tace ki auri dan ta ba suna da kudin da zasu aura mao duk macen da yake so a duniyan nan.
Amma kikaga ta nace akan sai dai ke din take so ki zauna dashi, nasan kuma tai hakane don tana ganin ke ce kila zaki iya kawo karshen wahalan nashi.
Shi fa hanyan sabon Allah shiga rai ke gare shi sosai, daga lokacin da akace wanan abin baida kyau haramun ne, sai kiji zuciyar mutum na tura shi aikata shi a ko wani lokaci.
Shiyasa akace an zagaye wuta da abin sha,awa wanda zuciya ke so, an kuma zagaye aljanna da abubuwan ki wanda zuciya bata so.
Don hakane duk wanda ya kama hanyar aljanna zai ta haduwa da abubuwan da zuciya bata so, haka kuma shi wanda ya kama hanyan wuta zai hadu da abubuwan da zuciya ke so.
Shiyasa akace daga cikin hakkurin da ake son mutum yayi shine harda biyayya ga Allah da manzon sa dama
magabatan mutum da kuma hakkurin gujewa sabon Allah.
Hana zuciya aika ta sabon da ya ginu a kanta farat daya abu ne mai wahala so sai sai mai hakkuri.
Idan kana da hakkuri zaka iya jure jawo hankalin mai yawan sabon Allah sannu a hankali ta yawan nasiha da lurar da mutum illar abinda take aikatawa.
Uwa uba kuma addu,a da nasiha ga mutum har Allah ya bada sa,a ya bari ko ya rage.
Yin fushi da mutum ko kaurace mashi baya hana mutum sabawa Allah sai dai ma ya kara kangarewa kawai.
Amma jan mutum zuwa jikin ka shike sa mutum ya rage watarana har ya tuba ya daina gaba daya.
Don haka ita hajiya taga cewa, kece kadai zaki iya taimaka mata gurin wanan yakin.
Don haka yaki babba a gaban ki yar ba don hajiya ta dora maki nauyi mai girman dauka gare ki.
Fushi zagi gori da kawar da kai ga abinda yake aikatawa yanzu ba naki bane yar baba.
Don haka wani kawar da kan ki gare shi ko ki kyamace shi ba naki bane yanzu.
Don idan kinyi haka tankar kin kara tura shi ga halaiyar da yakeyi ne na kyamata da uwarshi bata son ganin shi a ciki.
Hajiya ta wuce ki watsar mata da bukatan ta gare ki, sai dai ki kara runguma kawai da hannu bibiyu.
Zata ci gaba da magana gwagona ta leko tana cewa fito mana Bintu, dare fa ta soma kin san ba wuta garin.
Haka yasa nai sallama da mahaifiya na tana ta jero min addua irin da yadace duk uwa taiwa yar ta da zata dakin auren ta.

****** ********* ******
Waagegari tun da safe wata mota ta iso da kujeru da rumfuna suka shiga hakawa sai kuma fa mota da abinci ruwan sha na gora da leda sun iso.
Inna ta bawa ranan ta arare ta yafe itace kirjin buki arziki ya sauka mata a gida sai yadda tayi zuwa tara da rabi sai dirin motoci ke tsayawa a kofan dan gidan mu.
Haba take guri ya kaure da yan ma,abba sai kirari sukeyi fa Alhaji wani ga Alhaji wani yazo.
Zuwa can wani mai murya ke sanar da jama,a ta lasifikan shi Allah yayi lokaci yayi yau an daura auren Umar faruq da Fatima Bintu akan sadaki naira dubu hamsin.
Sai wata matar babana ta rangada wani irin guda tana fadin yau Fatima Binta kin gwada muna kin haihu a zariyan Ibrahim da maimunatu don kin jawo muna arzikin da bamu taba sanin akwaishi na garin nan.
Allah yasawa auren ku albarka yakawo muna zuri,a dayyaba masu albarka arayuwa.
Bayan dan lokaci muka ji mata na fadin ance ku gyara ga angonne nan zasu shigo gaida ku cikin gida.
Ina can boye kuryan dakin Inna tabawa naji matan tsakar gida na fadi wanan na tsakiyan dogon ai shine angon lalai Bintu kan kin yi sa,an miji wallahi da ganin shi ba karamin mutum bane.
A raina nace baku san komai ku kumbu a rufe ganin kyaun dan maciji kuke mashi haka dahi nanan cikin shi.
Ba wani bata lokaci matan da aka zo dasu suka fara cewa wai a fito da kaya zamu tafi take na saka wani sabon kuka mai tsuma zuciya.
Bashar ne ya dauko ni a motar shi sai kaunan mahaifiyata wata malaman arabiya ce ita sai gwagona dana zo birni a wurin ta, kawa yena su biyu haka muka shigo mota daya dasu.
Tun da muka fara hanya ina a dunkule sai kuka nake rusawa a hankali gwagona tana min fada wai zan jawa kaina ciwon kai a banza kamar wace za aika gidan mugun abu.
A raina nace kyace haka mana tunda kin ja min mugun rayuwa a sanadinki duk na fada cikin wanan rayuwan haka ai.
Bashar yace gwago kyale Fatima tai kuka yau don zata fada sabon rayuwa kuka ta zama dole gare ta.
Magana ce yai mata a cikin magana wanda duk cikin motan nasan sai ita kadai ce zata fahinci hakan kawai.
Gida ya cika yacika ya batse kamar may yan uwa da abokan arziki nisa da kusa birni da kauyen an hadu.
Muna na isa aka fara futowa zuwa taron mu yan uwan mama da yan uwan mahaifin su yan uwan umma da mama nasu suma ya ishe su ranan.
Ga Nafisa tayi halinta suyi party tayi tatil haka tashigo gida tana ta watsewan ta gidan Amarya yaya Ahmad kuma suma suyi nasu bushewan sai tir da Allah waddai akeyi masu ta ko ina.
Part din maji ne ba wani abin asha da akaji don bukin yaran ta neat akeyin shi cikin mutunci da sanin ya kamata.
Ina rike da hannun kaunan mahaufiyata da yan uwan ubana don atare muka iso da sauran yan kawo ni daga garin mu,
Wanan kauna mamana ta dan duko tace saka kafan ki na dama ki ja basmalah kafa ashirin da daya tare da karanta, (fihizuma, wa huwa ala kulli shai in kadirr,,,, kafa ukku)
Nan mukaja muka tsaya kaman muna wani abu na karanta tace kin gama nace eh tace ubangiji Allah yasa ki shiga da kafar dama Fatima.
Mama tana jin mun shigo ta taso da kanta tazo ta tare mu ta rungumoni jikin ta tana maraba da diyata sannun ku da zuwa.
Dakin mu na shige da kawaye na na samu su maryam dakin ya cika da kawaywn ta.
Suna ganina ta saka ihu tare da shekowa ta tareni da murnan ta nan muka zube na hira ni dai ban da kuzarin bata amsa sosai a lokacin.
Zan iya cewa ni dai tunda aka fara shagalin bukin mu ban saka Amirah a idona ba har naje na dawo din ban gan ta ba ga gida ya cika ya make da mutane.
Nace niko banga Anty Amirah ba fa tace wa tana can gidan yayan mu da wasu baki ma, ana dai ince maki tana gidan ki can ta tare yau tun safe suke can da kawayen ta wai suna wa bakin shi abinci.
Kin san ita yar ba ruwan mu ne daga cikin mu adole a bayan yaya take bata san zatai kunya ba idan yaya ya shiga hannun wanan matashiyar matar tashi da nake gani.
Nace kai anty zaki fara ko tace wallahi Bintu bakiga yadda kika koma ba yau gaba daya kamar wata yar kasan etopia can.
Kin san sune yakar kyayo acikin jin sin na yan adam.
Karfe daya da rabi a kaje daurin auren yaya Ahmad wai na yaya Imirana tun bakawai na safe aka daura don su haka akeyi gidan matar shi.
Biyu da rabi aka daura auren su Anty maryam da Anty Nasmatu diyar mama, ita ba ruwan ta da sha,anin kowa a gidan mu irin masu akidar ra,ayin rikau ne ita.
Muna nan akace wai za,ai dinner da karfe bakwai zuwa takwas na dare.
Haka yasa ana idar da sallah magariba mummy tace kowan mu ta fito dama muna cikin shiri tun yamma kowa ta kimtsa tafiya gidan ta.
Nice farkon kaiwa don tare aka fita dani da maryam anty Nasmatu yan uwan uwar ta suka kaita ita ma.
Jin an dakatar da mota yadan sani bude fuskana kadan gidan da nagani sai da gabana ya fadi don zakace ba cikin garin sokoto kake ba a gidan.
Hankalina yai balain tashi ina yaya ya samu kudin da yai wanan gida haka ba dai a ball kawai.
Ina jin Inna tabawa na fadin dankari ba fashi wanan gidan haka shine dai gidan Bintu ko kuwa?
Ina makalle ga hannun kaunan mamana wacce dama ina ganin don haka yasa tazo daga bangaren mamana.
Tace idan zaki saka kafan ki akasa ki karanto fatiha kafa uku, ko wani da bissimillah.
Sai ki karanta Basmalah irin na dazun kafa ashirin da daya ki karanta falaki da nas ki hada da ikilas uku uku Allah ya sawa aure albarka ya kare muna ke daga duk wani abin ki na cikin aure.
Ina idarwa ta kama hannu na tare da rada min ki dinga karanta Hasbunallahu wani imal wakeel har mu shiga ba adadi.
Muna tafe masu guda sunayi masu suraitai nayi niko ina saman bakina har abinda batace ba idan yazo min janakeyi na neman tsarin daki.
Nan aka shiga bin gidan da kallo mun samu yan uwan mama acan sune suka tari amarya.
Muna nan dai akace afito akai maryam nata gidan ba nisa sosai don unguwa daya muke.
Wata kawar anty Amira mai makeup ce tashigo dakin bayan an watse tace amarya nazo nai maki makeup na fita dinner ne.
A hankali na kware rufin da ke kaina sai naga tare da su Amira suke da kawayen ta naji mai makeup din tana fadin masha Allahu friend wanan ce kike kira da yar kauye haba waban aiko a fashion sai haka mana.
May kuma ake bukata ga mace ga kyau ga wayewa duk a gurin nan tsoki tayi tafita daga dakin tace ma sauran su fita su bar mu.
Ta busu tarufo dakin tace na taso na saka kayan da suka shigo dashi a jikina kallin kayan nayi da mamaki nace wanan kayan zan saka tace eh shine angi ya sayo na dinner.
Ba yadda na iya dole na saka kayan hakana a jikina ba don naso ba sai da zan saka nagane akwai wani daga ciki mai tare jikin mutum.
Tana min kwalliya tana min gulma wai may yasa Amira take ta faman kusheni ne haka ita bata taba zatin haka zata ganni ba.
Don Allah kada na damu da duk abinda Amira da yan uwan ta zasuyi min hassadane kawai take gani yana damun Amira.
Nace haba anty kin taba ganin mutum yai hassada da dan uwan shi nima fa kaunan tane halinta dai ne baku sani ba amma haka take ita.
Tana min magan ganu akan rayuaan mazan yanzu abinda zakayi wanda zaka kama miji da sauri a hannun ka ni dai umhumm kawai nake ce mata har muka gama komai da ita.
Ba matar ba ni kaina nasan na hadu haduwar da ban taba sani ina da shi ba irin haka sai yau.
Sai tara da rabi akazo daukan mu zuwa gurin dinner wata irin haddan motace aka bude min baya in shiga.
Duhu bai


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login