Showing 63001 words to 66000 words out of 373688 words

Chapter 22 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

bata a gidana.
Nakuma bata zabi amatsayin ta wacce ta taimaka ma rayuwana tun ban san ko mai ba na hanyan neman kudi har yakai ta fara lurar dani yadda zan zamo mai dogaro da kaina har zuwa wanan lokacin.
A fusace hajiyan shi, take cewa kace ma da kudin ta ka zama haka a yau.
A gadarance yace kusan hakane gaskiya don kudin ta da nawa ne muka hada nasai form na sai sauran abubuwan da ya sace nayi kafin na samu na kai ga appointment dina.
A lokacin hajiya ke kin sani Abba bai yarda da zancen aikin da nake nema ba yafi da son na kama kasuwanci kawai.
Ashe don haka hajiya yau komay nai ma sa,adatu kaman ma ban mata komai bane daga cikin gudun mawan da tai min a rayuwana.
Don haka yau hajiya a gaban ki ina son kowacen su ta sani cewa Sa, ade da suke gani ba abin da zanyi wasa ko sakaci da ita bane arayuwa na.
Don haka wace zata iya zama dani da mata ta zauna don a tare kuka gan mu da ita auren mu va zai sa na watsar da mata na mai tausayina mai sona da kauna na wace ta san zafina da tausayawa rayuwana.
Hajiya ta cabe da cewa ai ka karasa kace wace ta haife ka ta san zafin cikin ka da goyon ka.
Aa hajiya bata kai can ba amma dai ina son su fahinci darajan ta a guri na yafi karfin yadda suke tsanmani a yanzu don naga suna son su wuce limite din su agidan nan.
Duk wace bata iya zama a gurin da na ajeta hanya a bude yake gareta zata iya komawa inda tafito don babu dole a gareta.
Matata dai ce ba zan taba wullakanta taba akan ko wacen su insha Allahu.
Kuma ina son ku sani hajiya da kuke kai karana kona matana a gare ta ga hajiya ga ku duk wace ta kara kai karan dayan mu gurin hajiya a gidan nan kan al,amarin da ya shafe ni ko Sa,ade.
Mace ta sani kuma ta rike a kanta zan bata mamaki kwarai ga irin matakin da zan dauka akan ko wacece a gidan.
Haka ya isa please ban san may kuke so dani ba kowacen ku nan tasan zamana da matana tun farko haka kuma kuka amince da zaku iya zama damu a hakan da muke ban auro ku don na wulakanta matana ba don ina son abina kowan ku kuma ta sab da hakan ta amice don haka yanzu kune kma kuke son bi ta hanyan mahaifiyana don ku cuta mata kuma cutawa mahaifiya don Alhakin yarinyar mutane ya haukan magaifiyana.
Saboda may zakuyi muna wana mugun sakkaiyan hakan kuna amfani da mahaifa na don ganin an cutatawa yar mutane saboda hakkurin ta.
Kada kuyi tsanmani ban san abubuwan dake gudana a gidan nan ba na bar kowa tana abinda ta ga dama a gidana.
Akwai watarana yaba tafe ranan da zan dauki mataki daidai da laifin kowan ku amma dai ina mai kara ja maku kune ga abu biyu zuwa uku.
Na farko shine mai son zaman lafiya ya bar hadani da matata da iyayye na fada.
Sai kuma ina gargadin ku da ku daina shiga harkan Sa,ade ku barta taji da lalurar da Allah ya jarrabe ta da shi.
Don haka zance shiya da kuke cewa ta zaba ta bar maku wanda bakwa so zaku iya komawa can dakunan ku da kuka fito don yau idan Sa, ade tace min bata bukatan zama da kowacen ku a cikin gidan nan ya ya tabbata hakan a gare ni.
Aiko na hajiyan shi ta amshe da cewa tau issahe akan wanan figagan matar naka mutu kwakwai rai kwakwai kake wanan magana.
May yarinyar nan tai maka hakane har idon ka da zuciyar ka ya rufe yau a gabana kake wanan magana.
Lalai Sa,adatu kin gwada min ki kai kin kai matakin daba naki ba a gidan nan tunda har yau Alhaji karami ya rufe idon shi a gabana yake wanan magana haka.
Hajiya ya kamata ki sani yau idan haka ya kasance a gidajen auren yan uwan mu mata ba zaki ji dadi haka ba, muma ba zamuji dadi ba don may hajiya ba zaki daina wanan halin ba ko don kwanciyan hankalin diyan ki mata dake gidan mazajen su suna aure.
Au to lalai abin har yakai zakaiwa yan uwanka mata baki akan matar son ka duk ka haukace min yau don na taba ko.
Ai kafin kayi naka, naga wata fitsararar yarinyar da matar ka ta dauko ta aje a gidan don isa da mallaka ra fara nuna min fitsara don samun wuri.
Ta juya gurin antyna tana cewa ban son ganin wanan yarinyar a gidan nan ta gagawan barin gidan nan tun ban dauki mataki ba a kan ta ?
Hajiya wanan yarinyar yar uwar Saade ce nina bada bakin ta dauko ta nan don ta samu mai taimaka mata ga halin da take ciki tana bukatan taimako ?
Kafin suci gaba da magana sai ga maigidan ta ya kirata yana tambayan ta tana inane wai.?
Ta kasa bashi amsa don tasan ya hanata zuwa gidan dan nata saboda wanan halin da take zuwa tayi.
Kwata kwata bata kaunan zaman Sa,ade da danta don acewan ta kullun wai ta girmay wa mijin nata shi yasa take masu wayo.
Ta manta cewa itama tana da diya mata dake aure a wanu gidan har su uku bata tunanen cewa abinda take wa yar mutane zai iya faruwa akan diyan ta.
Mata bamu tunanen cewa mu uwaye ne masu diya duk abinda ka shuka shine kake girma a rayuwan ka.
Muryan mijin nata ne ke fada mata cewa tazo gida ga Aisha, yar su ta dawo gida da matsala.
Wanan maganan da taji ne yasa ta dafe kirjin ta tana cewa zata tafi amma zata dawo don bata karasa maganan da ya kawo ta ba.

****** ********* ******
******
Tun da farar safiya muryan Jatau ne ya tayar da mutanen gidan da balain da yazo masu.
Yake cewa mama tafito bazai yarda ba tasan yarta honko ne ta dauka takai mashi gidan shi don an raina shi.
Shi za, aiwa wullakanci ko may da za, a dauko honkon akawo maigida don an mai dashi tsoho.
Gaban mama ne yai mugun faduwa haka ta daure tafito zani na faduwa mata gashi har mutane sun fara taruwa don gulma.
Tace a ranta bari ta rufe ido tai mai na mahaukaci kawai a wuce gurin gaba daya.
Ta na lekowa take cewa kai Jatau kada ka dauka ko tsoron ka ake ji duk haukan da kakeyi kyaleka na keyi.
Mata kace kana so mata kuma na baka banga dalilin da zaka taso tsofai tsofai dakai ba kazo muna kana wanan magana abin kunya.
Tace ankai maka honko din sai ka turo min yata yau din nan na fasa auren bazata zauna ba a gidan ka.
Da Jatau yaga mama ta fishi iskanci da hauka dole ya kwantar da nashi haukan yace baki da hurimin daukan min mata, don mata zamana take yanzu.
Matar ka da kace honko ce ai daga yau ta gama zama dakai a gidan ka don dama kudin bazawara ka biya bana budurwa ba.
Yace a shekeke yo ina budurwan take anan kin kai min hinkon diyar ki aiko sai ga su Rukaiyya sun fito daga cikin gida.
Mama ta juya garesu tana cewa maza kuje kuzo min da Lawisa gidan nan yanzun nan.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,


IDAN KIN BIYA KI RIKE AMANA DON NAUYI GARESHI YAR UWA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA DON GIRMAN ALLAH, , , , , ,


Da taimako na muka kanmala aikin girkin rana da muka samu anty ta dora don muna cikin hira na mike don jin kaurin abinci danaji.
Kofan danaga ta nufa dazun dauko muna abun sha na nufa sai dai ina shiga kaina ya daure yadda naga kayan girkin zamani ya cika kitchen din ta ko ina.
Na rasa yaya zan duba abincin da naji yana nuna alaman ya dahu a lokacin.
Gurin gas din na nufa da tsoron tabawa fal a zuciya na don ban taba amfani dashi ba sai dai cikin karfin hali na bude tukunyan dake saman wuta.
Na samu abincin har ya tsotse na sauke sai dai ban iya kashewa ba ganin kayan miyan da tai blandinga cikin blander na juya na dora a wutan sai kamshi ne ya ziyarci hancin su a falo lokacin kuma suka fahinci bani falon tun dazun da sauri anty ta mike zuwa kitchen din ta samay ni a tsaye.
Cikin mamaki take cewa dani Rama dama kin iya girki da gas ne ?
Kaina girgiza mata tare dacewa yau ma na fara ganin shu ai, tace min kiyi a hankali nan take min bayani kan komai na kitchen din muna aiki a tare da ita har muka karasa tana gwada min komai sannu a hankali har na fara fahinta har muka gama aikin na zubo ma mama dani , mukaci mukasha muka koshi.
Suna hira da mama nake fahintar akwai matsala a gidan nasu yadda naji tanawa mama bayanin komai dake faruwa.
Na bu gidan da mamaki gashi da girma da kyau babu ne kawai babu a gidan amma wai zasu bar gidan bada dadewa ba.
Ganin ina zaune a takure na kasa sake jikina yasa ta kallon inda nake tausayi nake bata matuka idan ta kalle ni yadda rayuwa yazo min ina yar karama da ni.
Anty ke cewa na taso ta gwada min dakin da zamu zauna a part din ta nan na kwashi kayan mu na kai dakin sai da na tsaya na gyara shi tas na shiga nai wanka tare da yin sallah.
Don a kauye na tashi amma ina da matukar tsabta sosai naki jinin ganin daki a ya mutse ko kadan.
Kafin wani lokaci nai ma gidan kwal don dama gyara yake so bai samu ba ita gashi tayi tafiya sauran matan gidan kuma ba zama sukeyi ba a gida koma sun zauna basu iya gyara ko kadan don son jiki.
Tun wanan ranan da na zo anty tasan ta rage matsala ta wanan fannin sai misalin biyar saura yaran gidan suka dawo daga makaranta su hudu na gani uku mata daya namiji.
Na sheda yaran anty daga cikin su, don na sansu kwanaki da taje dasu ina gidan garbati.
Biyun yan matan ne ban san su ba sai ranan na fara ganin su don haka nake kyautata zaton diyan maigidan ta ne su din, don akwai dan kama na jini tsakanin su da diyan anty din.
Nan suka kewaye ta suna mata hiran makaranta sai can anty tace bakuga Grandma tazo ba da Anty Rahama.
Gaba dayan su yaran suka juyo inda muke muna masu kallon sha,awa da namijin ne ya juya yana kokarin cire school bag din shi dake goye a bayan shi cikin rashin damuwa da abinda uwar tace mai.
Duk da yara ne an koya masu gaisuwa sai yaran da ba nata bane suke muna wani irin kallon mamaki.
Nasir baka gaida Anty Rama ba fa ya dan juye fuska a daure yace ina wuni ?
Muka amsa mai a tare da mama lokaci daya sai dayan yarinyar ta dan kwanta gefen hannun kujerar da anty ke sama tace mummy are they going to stay with us ?
Gaba daya yaran suka juyo suna son jin amsan da uwar tasu zata bayar a kaina maman tace dasu i think so, cikin jin dadi suka saka ihu lokaci daya suka samu waje suka zauna suna surutu.
Kamar yadda nake wa kannena a gida idan sun dawo school zan sa su tube uniform din jikin su na kwasa na wanke na basu abinci kafin su wuce islamiya.
Tsab na mike daga inda nake na ce da Amira oya Amira zo na cire maku uniform kuci abinci.
Duk sukayo kaina suna rige rigen zuwa gare ni cikin jin dadi a tsakanin su, anty tai murmushi daga inda suke zaune da mama suna kallon mu tace dani ku shiga daga ciki dayan dakin kayan su yanan an kowa ta nuna maki nata aini kin ceceni yau wallahi.
Komai na gama masu har abinci a sama sukace zasuci don haka can na hau dashi sukaci muka gyara gurin kamar basu bata ba.
Cikin kwana biyun da nayi a gidan na dan fahinci abubuwan rayuwa na gidan yadda take gudanar dashi a tsarin ta.
Kaman tashi da wuri da safe a girka abincin yan makaranta ai masu wanka a shirya su a hada masu abincin zuwa makaranta sai rakiya har bakin motan da zai kai su school.
Haka yasa ta samu sauki sosai a dan zuwan da mukayi da nayi motsi kadan zata fara cewa wai Rama na nagode nagode kinji idan naji ta fadi hakan.
Sai dai nayi murmushi nace kai haba anty wanan har wani aiki ne mai yawa ?
Nikan a guri na ai wanan ba wani aiki bane don banga abin wahala ba a cikin sa amma ita sai take ganin babu taimakon da yakai wannan tunda gashi tana samun hutu da yin barci da safe wadattace yadda ake bukata a gareta.
A kwana biyun da mukayi kawai shakuwa ne sosai ya shiga tsakanin yaran matan gidan dani sai Nasir ne har yanzu bai sake jikin shi dani.
Sosai nake mayar da hankali ga taimakon rayuwan anty a gidan ko ina na gidan sai walkiya yakeyi don yana samun gyara.
Idan yara sun tafi zan gyara falo har kitchen na dora abincin rana sai na koma part din anty na hada mata ruwan wanka na dan zauna da ita muna hira har ta mike ta shiga tai wanka sai nai saurin gyara mata dakin kafinta fito daga wanka na koma kitchen gurin girkin rana, kafin wani lokaci na gabatar masu da abincin rana ko.
Kafin mu cika sati daya komai na kan gidan nasan yadda akeyin shi zan kuma yi mata shi tsab haka yasa suke samun hutu daga anty har mama sun dan canza a wanan lokacin.
Duk wani abinda nasan bata so ko zai bata mata rai da yaran ta basu so, zan gujewa wanan abin .
Na zomo mai kafa kafa a kan komai na gidan bana shiga shirgin dabai shafeni ba don ko yaushe ina busy ne.
Ganin yadda yanayi na yake bana jin kiwar ko kyashin aiki komai idan ina yi, yawan shi bai damuna don ni a gare ni yar kauye tashin kauye har ina aikin yake anan bisa ga namu na kauye mai wahala sosai.
Sai dai ita anty ko yaushe cikin yi min fada take wai na dinga hutawa sai dai nayi murmushi kawai idan ta fadi hakan mama kan ce ai gareta wanan ba aiki bane.
Tana matukar bani kulawa ta bangaren ta sosai don tana nuna min kamar cikin mu daya da ita idan tana nuna min so.
Yau ma zaune take falo ta mike kafa saman dan stol din katakon dake gefen kujera wanda ta jawo zuwa gaban ta, dauke da waya take hannun ta tanayi tsawon minti goma da fara wayan ta kamar ba kudi ake akashewa ba.
Sai tv ke ta aiki shi kadai a falon don mama da suke zaune tare gyangyadi take yi lokacin a zaune ba kallo ba, ai dole mama tayi gyangyadi, taji sanyin AC na ratsa mata jini yanayi ya sauya sai barci duk inda ta zauna.
Ferfeson kodan kaza zalla tace nai masu yaji kayan yaji don hadin kauye nai masu take kamshi ya gauraye ko ina na gidan .
Na zuba mata shi mai yawa tare da dorawa ga ture da goran ruwa sai dai ba mai sanyi ba nazo gaban ta inda take waya na aje mata kayan abincin naji tunda safe tana cewa tana son cin bread da shi ferfesuf irin dai kwazaban mace mai ciki abinda, bai yuyuwa tace shi take so.
Sai ganin na hado mata shi komai kamar yadda take muradin son cin shi kusan kwana biyu ke nan da take marmarincin hakan.
Ta manta waya takeyi sai cewa tayi kai masha Allah Ramana Allah yai maki albarka duniya da lahira ya kare ki daga sherin masheran ta.
Yanzu abinda nafi kusan wata ina son nayi na zauna naci kamar may shine daga kinji na fada kika hada min yadda nake so.
Murmushi nayi ina gyara aje mata kayan abincin da kyau take cewa anya Ramana idan mutanen gidan nan suka dawo zasu gane ni kuwa wanan irin kulawa dana samu a yan kwanakin nan haka.
Sai da taji dan murya cikin waya yasa ta tuna waya take tun farko abincin dana shigo mata dashi ya katse ta.
Daga cikin waya ake tambayan ta wacece take zukawa albarka haka ne wai ?
Tace bari kai dai heartbeat sister na da suka zo da mama ne ta hada komai na gidan nan ta hutar dani daga barci sai ci sai wanka sai ko kallo.
Yace good da kyau amma ko na gode mata wallahi tayi min maganin ki tace wallahi kamar ka sani, kafin duk na gama


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login