Showing 252001 words to 255000 words out of 373688 words
Chapter 85 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
san dalilin shi abugi mutum kuma a hanashi kuka ke nan yace a ran shi.
Zama yayi tare da cewa bani breakfast dina Amirah ya fadi Amirah dake masu kallon mamaki bata fahinci komai ba a fadan tace.
Yayana may kuma kaiwa maji hakane wai?
Yace wallahi ban sani ba kaunata kawai dai maji na son min fada ne don taga ban shigo ba kwana biyu ni kuma aikine yai min yawa.
Amirah tashige kitchen ta hado mashi abin karyawa tafito koda tafito ta samu maji na fadin.
Kai akwai gatan da za,ai ma dayafi na daga kayi arziki ka samu yarinta gari yar arziki zata rufa maka asiri daga shi har Amirah kallon maji sukeyi don jin abinda ta fadi a lokacin tace eh ba rufa maka asiri zatayi ba may zatayi, kai may ya saura a jikin ban da ragowan maye sai ball.
Yace maji nine yarinyar nan zata rufawa asiri ko zan rufa mata dai kece kike ganina haka maji amma ai duniya ta san ba abin banza nake ba yanzu.
Wallahi maji inkina fadi haka a gaban ta dadi zataji ta raina ni don bata da kunya Allah.
To ubana sai ka rufe min baki tunda kakawo karfi yanzu ka wuce fadana yace ni bance maji cikin dariya duk yana kokari yaga ta sauko daga fushin ta.
Maji wai wata yarinya ta ki ka yiwa yayana sababi a kan tana haka?
Cikin bacin rai ta dago tace mata Fatima mana ko da me ya fita oho?
Itama Fatima in ba tauye tan danayi bata iya musa min ba mitakai dashi haka ba makari.
Maji mi yayana zaiyi da Bintu kuma yar kauye da ita ba asali ga mata yan asali da yawa a cikin gari.
Da may yahita da zakice haka, nice hwada min damay hita, ?
Shi har wani asali yakaso yabar kyau ne tun wurin wanka ai yanzu ya makara da wanan ko?
Da mamaki furcin mahaifiyan shi ya dago kai yana kallon ta sai abinci yake cusawa a cikin shi kaman dolle yake ci.
Amma gaskiya maji kaman mara galihu zakice wai da Bintu zaki hada shi Bintu may can don Allah dai Amirah ta fadi haka cikin yanayin bacin rai.
Walle Amira kihita min ga ido tun banci kaniyaki ba gidan ke ko kwatan Fatima kin kaine asali ne mi ake bukata ga asalin ba uwa da uba ba.
Hwada min wane ta rasa daga ciki?
Ko shi arzikin ga dakika gani Allah ya bashi kikawa katobara, haka.
Ita ke san inda Allah zai aje tane halan ?
Nikkara jin keyi wani magana mara dadi akan Fatima walle saina lahira yahiki jin dadi a gidan nan marasa ta ido kawai.
Amirah tahau ta cika ranta ya baci ta kalli dan uwanta hadade guy ye haka son kowa kin wanda ya rasa amma ace ga Bintu yar tallakawa zai kare.
Sai dai ba dama ta muda ko tak yadda uwarsu hau tasan yanzu nata na samun ta.
Bai jima zaune ba yamike yana fadin shi zai fita, maji bata tanka mashi ba don haushi.
Mun dawo gida a gajiye don an kusa fara kiran magariba a lokacin saboda huturu yayi.
Amirah ce a falo, zaune ina shigowa naga wani ir8n kallon banza da wulakancin da tai min.
Take nasha jinin jikina da zargin akwai wani abu bani ba har Maryam sai da ta tsargu .
Mun shiga saida mukai sallah muka fito maryam ta fara fitowa bata dade ba nafito nima falon.
Zama nayi tare da cewa anty Amira an fara film din end of love ne?
Kamar batajini ba ta kyaleni maryam tace min yanzu za,a fara time yayi ai.
Can taja tsaki tace dama kwadai ya kawo mutum ai don kwadayin tsiya abi an asarice muna uwa da tsafi sai yadda akayi muna da ita.
Komai tsafun mutum dai wallahi sai ya bar mu kuma sai ya bar gidan nan don yawan kwadai ma har diyan mutum ba,a bari ba.
Ke dawa ye kuma Anty inji maryam, ke tambayan ta cikin kallin fuskan ta.
Ke dalla kyaleni da takaicin daka damuna yanzu don kwadai sai a asirce muna uwa tasa dan ta ya tillatawa kan shi wata gaja can mara asali.
Kai amma anty Amirah na raina maki wallahi, wanga magana kuma ina ya fito maki haka da girman ki.
Shi yaya din yace maki lakaka mashi ita akayi kan dole ko wa ya fada maki ?
Maryam kifita idona wallahi kafin na bata maki rai a gidan nan don naga ke kina ganin kin girma wawiya kawai da batasan ciwon kan ta ba.
Kasa hakkuri nayi nace Anty Amirah kamar yadda kike gani an lakakawa yaya sadauki ni haka nima aka lakaka min shi.
Don ni yaya sadauki baiko cikin irin namijin da so na aura a,rayuwa na, don kwata kwata baya burgeni.
Shi kuma asali da kike nufin bandashi uwane banda ko uba, bski fini uwa ba baki fini uba ba.
Tsafi kuma ni bamu san shi ba a gidan mu a gidan ku nazo naga a na tsafi.
Aiko tayo kaina wai zata mare ni maryam ta shiga tsakanin mu tace wallahi baki bugun ta don amsan maganan ki tabaki.
Jin hayaniya yasa mama fitowa ta samay mu tana tambayan basin may yafaru kuma mayye haka wai ?
Nan maryam ke dada mata abinda ya faru tsakanin mu da amsan da na bata.
Tace Fatima shiyasa nake son ki don baki shayin kowa gurin fadin gaskiya.
Wawiya kawai sakariya kinga har tabar ganin girma ki ta baki amsa ba yau ba nake ganin take taken ki kan Fatima gidan nan.
Uba kika fita ko uwa ki fada min nace ?
Gurin ubanki ko uwarki tazo maula kin taba jin Fatima ta roki wani abu a gidan nan duk zaman ta damu.
Ku arziki yake rudi har ya rufe maki ido kika manta da Allah, da tazo gidan nan gurina may nake dashi.
Shiru Amirah tayi karshe bata tsaya falon ba ta tashi fuuuu ta shige ciki can ta kira sadauki ta fada mai abinda ke faruwa a gidan yadda maji tai mata.
****** ********* ******
Ranan bamu zuwa school misalin sha biyu da rabi na rana maryam na baya tana wanki mama tana dakin ta tana barci.
Sai ganin mutum nayi tsaye a kaina ban san shigowan shi falon ba sai da na gan shi tsaye a kaina.
Ya nayi yana dan waige waige kamar mara gaskiya yace cikin daure fuskan shi ke jinan.
Na dago na kalle shi saudaya na dukar da kaina yace wallahi duk kika sake kika yarda har maganan maji ya zama gaskiya a kan mu sai na halakaki garin nan.
Mara mutunci kawai banza dake ina mai shawartan ki da kiyi maza maza ki sanarwa maji baki son wanan hadin kema.
Jiki dan Allah ko na rasa mace a duniya may zanyi da kucakar mace mara fasali irin ki.
Duk da zagin ya bata min rai sai nai murmushi a fili nace amma kaima kana da bakin fada mata ko don naga kaman yan maye basu da ta ido kaga kaine daidai ka fada mata idan kayo mayen ka.
Ni kasan lafiyata kalau don haka ina da kunya da daraja ba zan iya kallon idon mama na fada mata ido da ido don ban da kuya ba wai ban son dan ta gudan jinin ta.
Amma kaika nasan zaka iya tunda bata idone dakai ba inkai haka ka taimaki rayuwana da ga auren kaddara aure alkakai da zan tsinci kaina acikin shi gidan mashay,,,,,
Kau ya kwashe ni da mari daidai maryam na shigowa falon daga waje, bata tsaya ba tai ciki gurin maji.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
IDAN KIN KARANTA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NE SHEDA HAKA MUNA BINKU BASHI,,,,
Tun da safe na na shirya komai nawa ina jiran ace nafito ne kawai, a lokacin don ko karyawa ban yi ranan.
Ina nan zaune a takure maryam ta shigo dakin tana cewa a,a matar yaya ba dai har kin shirya ba kamar mai gudun mu kuma ?
Hararan ta nayi idanuwa na sun dan ciko da hawaye a lokacin cikin murya mai kama da ta shagwaba nace haba dai anty maryam.
Nice kuma matan yaya don Allah dai ki bari mana please wallahi kina kara tayar min da hankali Allah.
Dariya ta kwashe dashi tace au to yanzu kuma may ya rage maryam ai kin zama matan yaya ko shafawa kawai ya rage insha Allahu.
Abinci mama ta aiko min ni da maryam din wai mu karya da taimakon ta na samu har na dan kurba ruwan shayi a cikina.
Ina nan ina zaman jira ina saye cikin wasu lace brown color sai duwatsun da akai mai ado dashi don nafi son dinkin riga da zani a rayuwana.
Tun lokacin da naji wa,azin mace ta rasu an rasa zani a cikin kayan ta da za,a yafa mata zuwa makabarta nake jin tsoron dinka skirt sosai, ina dinkawa amma ba ko yaushe ba.
Mama ta shigo dakin guri na muna zaune saman gado da maryam take ce min Fatima har kin shirya ne?
Maryam tace ai tuni da anbi ta nata ma ai da yanzu mai kaita ya dawo ko tundazu.
Murmushi mama tayi tace ai yau insha Allahu kuna zuwa ba fashi sai dai ban son ki kwashi kaya da yawa tunda kwana biyu kawai zakiyi a can.
Nace cikin yar muryana kala hudu kawai na dauka mama tace yayi kyau haka sai ki hada duk wani abinda kike so anjima su hajiya lami zasu kai sauran kayan ki can gidan ina son naga kafin buki ya kankama na gama da komai naku ko.
Mama koran mu ma ake kenan inji maryam tace ai muna tare balle ku da zaku zauna kusan uguwa daya da junan ku ai ba a rabu ba.
Da sauri na kalli maryam tace nima haka naji ana fadi wai nesan gidan baikai gida goma ba a tsakani.
Tace mama amma dai Bintu idan an dawo sai andawo da ita ta nan kafi a wuce ko?
Tace sosai ma kuwa tare da masu zuwa daurin aure fa zasu dawo kuma kinga su nasu can da safe ne goma na safe za,a daura naku kuma sai da rana karfe biyu na rana.
Don haka tana nan gida za, a daura naku ai insha Allahu, ko akwai wani magana kuma ?
Maryam tace a,a shike nan ai dama ina ce ko shike nan daga yau dai mun rabu ke nan.
Kun rabu mana tunda kowa zata kama dakin ta ku barni da wanan mara hankali muyi ta fama da ita.
Mama tace bari na fita kinji Fatima na aika akira min sadauki naji yaya zancen tafiyan naku kada ai rana ba,a tafi ba kuma.
Yana daki kwance yaji wayan mama ya shigo mashi ya dauka a kasale yana fadin salamu Alaikum.
Ta amsa mashi yadda ya dace tace baka shigo ka karya ba mana tin dazun ga wanan yarinyar Fatima kuma zancen tafiyan ta fa may ka shirya akai?
Yace maji bazan iya shigowa gidan nan ba yanzu don mata sunyi yawa wallahi, dariya yaba mama tace to ai duk uwayen kane a dakin zallan mu kawai.
Yace No maji gaskiya ba zan iya shigowa ba saboda yawa ba zan sake ba anan.
Tace ko abada akawo maka dakin ka ne yace shike nan maji hakan yayi.
Sai da aka shirya komai na karyawan mama tace nazo na kaiwa sadauki breakfast din shi yana dakin shi.
Wani irin faduwan gabane ya kamani amma dai haka na dake na fita da kayan a hannuna.
Ina fita na samu Abdul dan wurin mama Asiya zai fita na bashi nace don Allah ya kaiwa yaya sadauki.
Yace kai amma dai ke Bintun nan ke da mijin ki kuma kice baki iya kai mashi abin karyawa da kanki.
Na dan marairaice nace yi hakkuri yaya Abdul bashi kadai bane a dakin shiyasa nake jin kunya.
Yana min sheri ya karbi kayan ya shige mai dashi ina ganin ya shiga na juya cikin gida da sauri na.
Abdul na shiga ya samay shi a kwace ya fara gauda shi tare da aje mai kayan abincin yace kai amma dai Bintu shine tace min wai tana jin kunya bakai kadai bane a dakin bazata iya shigowa ba don Allah na taimaka na kawo ma ashe wayo tai min ke nan.
Murmushi yayan nashi yayi yace kyale yar kauye bata son shigowa ne tai maka haka .
Yace ai zamu hadu da ita ne sai na rama nima har yakai kofa zai fita yajuya yana cewa yauwa yaya UF dama ina son ka bamu kudi zanyi party da kuma ball na mu yan unguwa akan auren ka.
Yace kai Abdul party may kuma kawai da ka share da zancen wani party can ni kaga ba wani shirin da naiwa wanan auren.
Kai yaya auren da muke son aji labarin shi a gari zakace haka auren ka ne fa na farko yaya muka gaskiya zamu cashe sosai ne wallahi.
Sadauki ya mike zaune tare da jawo kulan abinci a gaban shi yace ka bari karfe biyar sai na ganka ba shi ke nan ba.
Yana cin abinci yana tunanen rainin wayyo irin nawa common abinci da zan kawo mai wai bazan iya ba sai na bayar akawo mai.
Kuma yasan da wani manufa maji tace ni na kawo mai abincin da kaina.
Yai tsuki tare da fadi a fili yar kauyen banza kawai wai a haka zan zauna da ita kuma.
Kiran wayan maji yayi tace maji yaron da kika ba abinci ya kawo min bai kawo min ruwun sha ba fa.
Tace yaro kuma ba Fatima nace ta kawo maka ba yace ni Abdul ne ya kawo min abinci yanzu.
Murmushi mama tayi tace kai Fatima wanan kunyane wai ko tsoro har yanzu ?
Kaga abinda nake fada maka gashi ka saka tsoron ka a ranta tun yanzu yaushe zata sake dakai kana mata mugun ta haka.
Tana gama waya ta nufi dakin mu ina kwance na kifa cikina a saman filo naji tana fadin Fatima yayan ku yace baki kai mai ruwan sha ba fa.
Kara faduwan gaba naji na dai ansa a fili da to mama ina mikewa zaune kamar da gaske.
Har tajuya tace ki tabbatar kece kika kai mai ruwan da kanki don in akwai maganan da zakuyi kafin ki tafi kan bukin ki sani.
Kunya ya kamani na sanin da mama tayi bani ce nakai mai abinci ba kamar yadda ta umurce ni.
Dogon hijjab dina na saka tare da daukan ruwa a jug na nufi dakin sai faduwa gabana ke yi a lokacin don nasan cewa zan samo wani sabon bacin rai ke nan kuma again.
Dan sallama na tsaya daga kofan dakin inayi cikin yar muryana yagane nice sarai sai yaki karbawa.
Na kara dan daga murya da sallaman naji yace please kada ki cika min kunne da wanan muryan naki kamar na munafukai don Allah.
Jin haka na sa kai cikin dakin yana kwace rigigin gine daga shi sai dan wando three quarter a jikin shi da yar singileti.
Na kai ruwan inda naga kayan abincin farko suke na aje tare da juyawa zan fita daga daki.
Naji yace manya kawai watau sai da kika nace sai kin aure ni ko don bakin jaraban ki da nacin tsiya.
To ki saurara sai ki shirya zama da U F don baki san koni wane ba da baki yarda da wanan bakin hadin auren ba.
Murmushi nayi nace niko nasan ko waye mijina fiye da kowa don ni san akwai aiki ja a gabana na sharan amai da fitsri irin ta mashaya.
What ya yunkuro kafin na karasa fita ya cafko hijjab dina ta baya sai naji gaban ya shake ni sosai, na sa kara da dan karfi ya karasa riko min kai tare da rufe min baki yana fadin .
Ashe ke yar karamar yar iska ce tukun may zaisa ki gudu tunda kin isa nine mai amai da fitsari ko?
Nace baka taba min bane karya nai maka idan ka manta aini ban manta da hakan ba, kaga nafi kowa sanin halinka ke nan.
Yanzu abinda yarage min na goge na kwashe idan kuma nayi arziki baka hada min da kashi ba ai na gode Allah.
Wani irin shaka da karfin shi yakai min sai da idanuwana suka fifito waje kwala kwala kaman zan somay.
Yana fadin zaki ci uban ki kuwa inkince ke yar iska ce don zaki dan dani wahalan ki a gidan.
Yace good haka ma nake so gara ki shiga shegiya na gasa maki kwakwa ga hannun ki, kagin na wullakantaki na mayar dake karamar bazawara gidan nan.
Nace shine dama sauki na in har kai min haka da sauri ka ceci rayuwana don, zaman kaddara dama kawai zanyi da kai.
Yakai wa kaina bugu da karfi sai da na gwauro da bango idona ya kawo hawaye nace dama duk matar mashayi wanan ne sakamakon ta ai duka da zagi da cin zarafi banyi mamakin haka ba don na shiryi taron