Showing 138001 words to 141000 words out of 373688 words

Chapter 47 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

gaskiya hakan yana da kyau kuma ina ga,dai kila zakiyi sati biyu zuwa uku ke nan eh mama Bintu ta bata ansa da hakan wanda ta dai fadi ne don su rabu lafiya da maman nata sabuwa.
Amma yadda tajeji bata sa ran cewa zata dawo wanan gidan ba kuma da sunan zama duk da dai ba ai mata komai ba amma gidan ya fita ranta don tana gudun kada sanadin ta mama tai fada da dan ta daya shiryu yanzu.
Tsaraba sosai Maji ta hadawa Bintu na gidan mahaufinta da yan uwan ta daban wanda zata kaiwa mahaifiyarta daban.
Mota akai mata shata ita kadai Alhaji yabiya tare da bata kudi da zata rike don amfanin ta a can.
Kamar yadda akai alkawari da driver hakan yayi har kofan gida su Bintu ya kaita inda aka,ganta a bazata don ba wanda yasan da zuwan ta.
Irin kayan da,akaga a na,shigowa dashine yasa hankalin matar uban ta ya tashi, har ta kasa boyewa da zuwan Bintu din.
Nan dai kowa ya,wayance sai sannu da zuwa ake mata ana kallon yadda a lokaci daya ta canza kamanin ta gaba daya ta koma wata yar Birni da ita.
Kafin wani lokaci har zancen dawowanta ya zagaye dan kauyen nasu kowa na fadin Bintu ta dawo ta koma yar Birni da ita.
Saida dare ta samu ganawa da mahaifinta wanda ya dawo daga gona a lokacin ana gabanin magariba.
Nan suka kebe tana bashi labarin zaman ta a burni da kuma mutanen arzikin da gwagon ta,tabarta gurin su.
Takawo sakon da maji tabata na,tsaraba ta bashi yana ta murna da farin ciki.
Bintu ta sheda mai ta kare karatun ta har matar dake rikon ta tace zata ci gaba da karatun ta idan jerabawan ta ya fito.
Mahaifinta yai farin ciki da jin wanan albishir din da tai mashi sai dai kuma yasan abune mai wuya yadda ta girma haka yan uwan shi su barta taci gaba da karatu sai dai in Allah ya nufa zatayi din.
Washegari Bintu kamar yadda ta,saba zuwa daukan karatu a lokacin da take gida hakan ta shirya zuwa islamiyan su.
Sai dai ta samu yawanci yan matan da suke karatun tare sunyi aure a lokaci, dan kauye basu bari yarinya tagirma sosai suke mata aure.
Malamin nasu yai farin ciki daganin hazikan daliban shi ta dawo kuma bata watsar da karatun ta ba don taje birni.
Taso ta fara a inda ta,tsaya da karatu a gurin shi amma da,tafara biyawa sai yaji ta,wuce tsanmanin shi.
Don haka yace ta dauka a inda,take can birni haka yasa taci gaba don ta sauka bita take yanzu.
Ganin duk idon sauran dalibai yana kanta kuma suna sauraren yadda sabon sallon karatun ta yake fita.
Duk sai sha,awan ta ya kama su nan suke zuwa wai ta koya masu yadda take fitar da haruffa cikin kara harshe.
Nan fa samarin kauyen masu jin sun isa suka fara kawo kan su gareta da,sunan sun gani suna so.
Itako mama ta,bawa matar ubanta tunda ta kyala ido taga kayan maihaifiyan Bintu da maji ta bata ta sa a ranta su take so.
Bayan nata da,takawo mata da yaran ta duk sai da Maji ta ba kowan su tsaraban da zata basu in tazo.
Haka ta,bawa tasa Bintu da mahaifinta gaba da masifan kan lalai sai dai ta dauki turmin wajen ina da aka bata takai mata.
Har abin yaso yakawo sabani a tsakanin ta da mininta watau mahaifin Bintu.
Don haka Bintu ta tsiri tafiya garin da mahaifiyarta take bashiri don tabawa sai fada takeyi wai bayan tagama wahala da ita yanzun anga dadi yazo shine zatace tasan uwar ta.
Bintu dai murmushi tayi kawai tana hada kayanta tare da tunanen yadda zata zauna gida da wanan masifanna matar mahaifin ta kulun.
Ta hada duk dan abinda tasan tana so tana bukata a cikin kayan ta tafito tare da,yi masu sallama ta tafi abinta badon ta tashi zuwa ba.
Ganin ta kawai mahaifiyarta tayi a bazata don rabin ta da ita tun tana aji hudu na primary bata sake zuwa ba don maigidan ta baida dadi ko kadan.
Bai son yaga Bintu tazo wajen uwarta ya shiga fitina da mitan shi baison zuwanta tana zuwa tana hure mata kunne don ta koma gidan mahaufinta.
Ta,samu mahaifiyarta da tsohon ciki a jikin ta kuma yana bata wahala don haka tun zuwan ta bata huta ba.
Da maigidan ta ya dawo daga Kasuwan kauye ya samu Bintu tazo ya dan fara daure fuskan shi.
Saida yaga abin arzikin da tazo masu dashi don har shima ya samu shadda yadi goma.
Shine har ya dan sake fuskan shi, yazo har dakin su fuska a sake yana cewa ,a,a Bintu harda tsaraba muka samu haka mai yawa.
Har yana tambaya ko taci abinci da tazo nan dai ya karaci surutin shi ita dai Bintu kai kawai ta gyada mashi har ya fita.
Washe gari tun da safe Bintu ta tashi ta gyara ko ina na gidan nan gidan yakoma wani fes dashi.
Sai zuwa rana ta fahinci ko abinci basu dashi a gidan nan ta saka katon hijjab din ta har kasa ta fita can sai gata da kayan cefanen ta niki niki mai mashin ya kawota gida.
Bata tsaya ba ta girka masu abinci suka zauna ita da yan kannen ta suka ci suka koshi harda mahaifiyarta dake auren wahala.
Maigidan sai zuwa rana ya dawo yana yan kamay kamay shi wai tunda ya fita ko sisu bai samu ba sai dan fura da akabashi da nono yace a dama,mashi,
Matarshi ta mike da kyat ta shiga daki sai gata dauke da kwanon abinci yana mamakin ina tasamu kudi har tai masu girki.
Bayan ta aje yake tambayan ta don ya zaci taciwo mashi bashine don diyarta tazo ta girka masu abinci.
Matar tace mashi yaringa ce ta sayo ta girka muna nan ya wani washe baki yana bude kwanon yai tozali da shimkafa da miya harda nama a ciki.
Yashiga ci yana sakawa Bintu Albarka tare dakai lomar abinci a bakin shi.
Bintu da ke daki tausayin mahaifiyarta ya kamata don tasan wanan susun mijin nata bai aje komai ba sai bakin shaye shayen da yakeyi kawai.
Abu tun bata da,wayo yake haka har yanzu data girma ta zo ta samay shi a hakana.
Dalilin da yasa ke nan take matukar tausayawa Maji akan shaye shayen da dan ta yakeyi don tasa mugun abune mawuyacin abune mutum ya daina shi a rayuwan shi.
Da yamma sai gashi da dan kunshin a leda yana wargale baki yana fadin ina,diyata ne gashi ba,sayo mata dan abin mu na kauye taci don nasan can birni basu samun shi.
Bintu najin haka tafito daga dakin tana gyara daurin dan kwalinta ta nacewa gani Baba.
Ya mika mata ledan ta,karba batare da,tasan abinda ke cikin ledan ba yana fadin ki gyara kici abin marmari ne gare ku.
Ta dauko kwanon ta bude ledan zogalane da rogo dafafe da zafin shi ya sayo mata harda kulikulin da zata gyara shi ya hado mata.
Bintu ta zauna ta gyara tasamo wani kwanon silver na miya ta zuba mashi azaton ta,bazai karba ba sai gashi ya karba har ya riga su cinyewa ko.
Sai faman santi yake zubawa sosai taji dadin ganyen don ta dade bataci ganye ba haka mai yawa.
Kamar yadda tai masu girkin rana haka ta girka mazu na dare inda tai tuwon garin masara data sayo da miyar kuka yaji daddawa da kayan yaji sai kamshi ke tashi ciki.
Haka ta zauna gidan mahaufiyan ta don yafi mata dadin zama gidan mahaifinta da matar uban ta ke sakata gaba da fitina kyashi kishi da hassafa duk ta dagwara mata shi.
Satin ta biyu a kauyen bata fita ko ina kulun tana gida da yan kannen ta suna hira ko tana koya masu karatu.
Ranan dai mahaifiyarta ta matsa mata akan tafita taje gidan yan uwan ta,su gaisa.
Ba don Bintu taso ba ta shirya tare da yan kannen ta mata biyu suka fita zuwa gidajen dangin su.
Suna gap da zasu dawone suka hadu da,wani matashi daganin shi kasan bako ne a garin ko kuma dai yazo ne ba,a nan yake zama ba.
Saboda yanayin shigar shi jikin shi da suturun shi ya banbanta da na mutanen da yake tare dasu a gurin.
Tun da su Bintu suka tunkaro idon mutimin yake kanta duk da katon hijjab din dake jikinta bai hanashi kallon ta ba.
Sun kawo daidai inda suke Bintu tai masu ina wuni gaba daya suka amsa cikin washe baki, a hankali mutumin ya tambayi wanda suke tare wanan a garin nan take ne ?
Har zasu wuce sai dayan mutumin yace wa dayar kaunan Bintu a,a Dije bakuwa kukayine yarinyar ta tsaya tana cewa eh yayan mu dage Birni ne tazo.
Su dai suka wuce zuwa gidajen da Inna ta tsara masu sutafi sukai Bintu ta gaida su.
Agajiye suka dawo gida lokacin yanma tayi ko gashi batai sallah la,asar ba don haka ta shuri buta ta nufi gurin alwala don kada lokaci ya shige.
Inda ta idar da sallah tana zaune mahaifiyarta take tambayan ta kawo mata abincine tace sun koshi tasha fura a gidan kakanta.
Sai ga,yaro yana sallama yace wai ance ana sallama da bakuwar gidan nan.
Bintu dake daki a ran ta tace ai kaji matsalar wallahi shiyasa ban son fita ko ina wallahi.
Bata so fita ba amma mahaifiyarta ta takura mata akan sai tafita badon taso ba haka ta shirya tafita cikin katon hijjab din ta kamar kullun.
Wanan mutumin da tagani a cikin gari dazun shine tsaye a kofan gidan nasu ya jingina jikin shi da motar shi baka henixe,
Yana dan kada makulin motar dake hannun shi a hankali, yana ganin fitowan ta ya dan fadada murmushin shi.
Yana cewa barka da fitowa gimbiya sai kika gannin kwasan kofan gidan ku babu tsanmani kuma ko?
Murmushi tayi tana fadin ina wuni yace shaf kinga na manta bamu ko gaisa ba ko ya kuke ya garin kuma?
Ta amsa da Alhamdullahi,
Yace ko da yake nasan ke bakuwa ce a wanan garin don ban sanki ba a garin namu.
To nidai sunana Mohammed Kabir kuma ni haifafen wanan garin ne ina aiki a abuja ne ina da mata biyu da yara biyar.
Jin haka Bintu ta dago kai tadan saci kallon shi yace yes kwari kina mamaki ko nayi yaro da,tara iyali haka ko?
Gashi kuma nagani ina son karawa ta uku ke nan insha Allahu idan an yardan min.
Mahaifina shine hakimin wanan garin nine kuma dana uku a gidan mu don yan uwana da kowa nawa suna garin nan da zama nine kawai Allah yakaini wani nahiyar zama.
Ina aiki a Federal houses ne a can da fatan kin gamsu da bayani na.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

A LOKACIN MU KE,,,,,,,

Zau ne take a tsakar dakin da ta gyara da sunan ta wanda babu mai shiga daga ita sai kawayen ta dakan shigo gidan jefi jefi.
Kwalaben kayan shaye shayen ta ne ta zube su a kasan tana dan mixed din su a cikin wani drinks dake gaban ta.
Mahaifiyarta ce tashigo dakin unexpected taji muryan ta a bayan ta tana fadin,
Raihanatu ina kika shiga ne haka tun safe robon ki da gidan nan ne?
Daga sama taji muryan uwar nata a dakin shigowan uwar bai hanata yin abinda takeyi ba a lokacin.
Idon mahaifiyar kar akan kwalaben maganin da take juyewa daya bayan daya.
Wanan kuma may nene kike yi haka tambayan ta ya koma akan abinda taga Raiha din tanayi a zaune daga ita sai yar farar shimi dake jikin ta.
Raiha tace cikin rashin damuwa ko tsoro magani nake hadawa na dan sha kafin na kwanta.
Amma ai wanan maganin haka masu yawa kamar ba na ciwo bane?
Raiha ta juyo tana facing din uwar ta take cewa, ba wai na ciwo bane ko wani abu kawai dai don naji garau ne a raina.
Da mamaki mahaufiyarta ke kallon ta tace kiji garau da shan wanan uban kwalaben haka.
Raiha tai murmushi tana cewa kai haba mama wanan aiba komai bane kawai dai muna shan shi ne don ya karawa mutum lafiya da karfi.
Raiha, Raiha kodai shaye shayen da yan unguwa suke fadi a kan kinayi gaskiya ne.
Hmmm Umma kada ki dauki zancen hassadan su a gaskiya mana hassada ne kawai irin na mutune da zaran sunga kaci gaba.
Tana fadin haka ta dauki cup din da ta zuba drinks din a ciki ta kwankwade Umma na cewa ke, ke, ke
Yanzu Raiha wanan uban maganin zaki durawa cikin ki kina da hankali kuwa Raiha?
Haba Umma relax ba zai min komai ba don ba yau na fara shan shi ba ai.
Innalillahi wainna alaihim rajiun, Umma take fadi yaunzu Raiha irin rayuwan da kika zabawa kanki ke nan?
Mace da ke kike shaye shaye haka ko acikin shaye shayen kuma sai naga naki yafi ma wanda nakeji karfi.
Hmmm kawai Raiha tace tare da kokarin mikewa tsaye take wani jiri ya dauke ta takoma ta zauna.
Umma ta kara saka salati tare da tafa hannun ta biyu tana fadin na shiga uku ni Lami yanzu Raiha ashe da gaske kina shaye shaye,
Sai kuka tajuya tabar dakin cikin tashin hankali ta samu mijin ta dake daki zaune yana shan shayin data hada mashi.
Ganin matar shi ta shigo tana kuka yasa shi saurin cewa, may yafaru Lami,?
Gefen shi ta samu ta zauna tana cewa malam ashe, zancen nan da muke ji gaskiya ne akan wanan yarinyar Raiha.
Zancen may ye gaskiya Lami?
Ya tambaya cikin son jin ba,asin zancen da tazo mashi dashi wanda bai fahinta ba.
Tace zancen shaye shayen da Tanimu yazo maka dashi tana yi bamu bincika ba muka haushi da fada.
Yau sai gashi Allah ya nuna min nagani da idanuwa na ta fashe da,wani irin kuka cikin tashin hankali.
Malam bai san lokacin da ya cire hular kan shi ba ya fara fifita dashi a hankali.
Yana fadin Inna lillahi wa,inna alaihim rajiun, yanzu ita Raihan abinda take yi ke nan har a gidan nan.
Ya mike cikin sauri ya nufi dakin Raiha inda ya samay ta har syrup ya fara aikin shi a kanta tana kwance daga ita sai dan shimin dake jikin ta tai dadaya da ita.
Yace ke Raiha, Raiha fa dake nake magana ko bakijina ne wai?
Raiha ta dago kai cikun mayen da ya dauki caji a jikin ta tace haba Baba please ka barni barci nake ji .
Inna lillahi yake maimaitawa don ganin abinda idon shi yagane mashi kan yarsu Raihanatu dake buge lis a cikin maye.
Haka suka kwana cikin tashin hankali a wanan daren don sun kasa runtsawa.
Malam sai fadi yake yanzu ashe kallon da mutanen shiya suke min ke nan ban sani ba suna min kallon mutumin da,ya,kasa tsare tarbiyan gidan shi.
Mutumin da baida kwabo ko tace ga iyalin shi suna,min kallon mahaifin yar maye a cikin shiya.
Lami tace nifa malam dama na dade ina,zargin wayewan yarinyar nan yai mata yawa wanan facali da take da kudi yadda,ranta ke so a ina take samun su haka.
Mijin yace bar wanan zancen Lami yanzu zancen shaye shayen nan zamuyi muji yaushe ne tafara shi har girma mata haka.
Washe gari Raiha bata tashi da wuri ba sai musalin karfe tara na safe tafito daga dakin ta don yuwan ne ya,tashe ta.
Dama shi kayan maye haka yake da zaran ya sake mutum sai ya ji cikn shi tankar babu ko hanji a cikin sa.
Sai neman abinda mutum zai zuba a cikin shi a haukace zai far ma duk abincin da ya samu yaci.
Brush tayi ta na kokarin shiga daki taji muryan mahaifinta yana kiran sunan ta alokacin.
Tai mamaki da taga har wanan lokacin baifita ba kamar yadda yasaba fita tun da farar safiya zuwa sana,an shi ta aski da yake wanzanci.
Nam Baba ta amsa mashi cikin nuna jin wani dar da kiran shi don bata san wai tayi laifi ba.
Tazo ta tsugun na gaban shi tana cewa gani Baba, wani irin kallo ya watsa mata amma ko ajikin ta.
Gani baba ta kara maimaita mashi cikin ko in kula da kallon da yake mata a lokacin.
Yanzu Raihanatu shaye shaye kikeyi a,rayuwan ki bamu sani ba ashe.
Kallon inda mahaufiyar take tayi cikin wani yanayi daya ba uwar tsoro sosai don bata san yarinyar takai haka ba ma sai yanzu ta hango a bubuwa da dama daga diyar tasu.
Baba bafa wani abu mai karfi sosai nake sha ba wanda kawai zai kara min karfi ne ta fada cikin nuna rashin jin tsoro a ranta.
Malam baisan lokacin da ya mike ba yafara kai mata duka amma Raiha ko gezau batayi ba.
Ganin haka yasa shi samun guri yazube sai wani zufa ya fara karyo mashi.
Raiha ta juya zuwa dakinta, babu ko damuwa da yanayin da taga


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login