Showing 210001 words to 213000 words out of 373688 words
Chapter 71 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
yaro yayi laifi ki tsare ba ai mashi fada kinga abinda wanan fasikin dan naki ya jawo muna a gida.
Wai dana mane yau tunda yai laifi ko?
Au to ba danki bane dan waye a gurin nan , saunawa kina fadin ke kikai daukan cikin abinki don haka abar maki kayan ki.
Zaitai magana yace cikin daga hannu da daka tsawa ki min shiru don ban son jin kazamin kalamin ki yau a gurin nan.
Yace Imirah kai kuma abinda kai min a idon duniya banda abinda zance maka sai dai nace kaje duniya tana da fadi.
Don daga yau ina son ku sani na cire Imirah ga duk wani harkan kasuwancina.
Don ba a hada biyu a lokaci guda zina da neman arziki basu tafiya daidai.
Don haka tafi nima nema nayi Allah ya bani kaje ka nemi na kanka amma da kudi na ni Abubakar ba za,a dinga zina dashi ba.
Wanan kalamin na Alhaji ya tayarwa Umma da yaran ta hankali sosai don sun wani babban komawa baya ne ya samay su.
Yace daga yau duk wanda ya dauko min magana irin ta zubar da mutunci da kima a idon duniya wallahi ku sani na tsamay ko wanene daga cikin zuria ta.
Ni ba mazinaci bane kowa ya sani a garin nan don kaucewa zina yasa na aje iyayyen ku haka a gidan nan.
Duk wanda ya ganin a gurin mace to ka tabbatar aure ne yakaini ba yaudara ba.
Yanzu ina riba ga illanta wa mutane yarinya da kayi amma fa ka sani shi zina bashi ne karike ka aje hakan a ranka.
Haba Alhaji kada kai mashi baki mana mama Asiya ta fadi haka da sauri ta tare mashi numfashi.
Yace Asiya ki shiga hankalin ki duk kune barayin na,tsunta da baku iya kwabawa diyan ku kun bar yara sun zama ni alkakan kafa a gida na.
Sai yai shiru can yanisa yace Maijidda ke kuma kada ki ga kamar ban san komai ba da kikayi.
Nasani kuma nayi mamakin yadda kika boye, wanan mugu munafuki mazinaci akan mumunan laifin da ya aikata haka.
Dukar da kai mama tayi tare da dan nisawa Baba yace ina kwana ki akanki yaso sauke wanan iftila,in kan yar amanan da aka aje a gurin ki.
Idan da ita yaiwa hakan ashe boye shi zakiyi ke nan kici amanan iyayyen yarinyar da aka danka maki.
Gaskiya kin bani mamaki kuma kin bani kunya matuaka dana ji hakan a kan ki.
Sannan ke mai da mai hali ko ?
Kika saka danki a gaba sai da yazo ya fitar da,wanan fasikin dana so ai mashi daurin rai da rai ya karata can gidan yari inga yadda zai samu wata yar kuma ya lalata.
Cikin karfi hali maji tace Alhaji ni ba na boye shi bane don kada a hukun tashi kokuma wai ba mumunan laifi yayi ba.
Gani nayi a lokacin yadda mutane su kai dandazo suna neman shi zasu iya illanta shi.
Yace da tsawa shi da ya illanta yar wasu fa ?
Tace idan sun kashe shi ko sunyi mashi wani mugun abin a lokacin Alhaji sai abin yafi na farko muni.
Kai kuma ka hau sosai a lokacin ba shawara zaka ji ba don yadda ka hasala.
Wanan dalilin yasa nai hakan .
Amma da aka samu natsuwa ai an fahinci juna don kaddarace shima ai da yayi abin ya koma mashi ciki.
Sannan ita wanan yarinyar mutane sun sheda ta da haka take watsatsa ce ita dama.
Yace ai shi ya fita watsewa,
Maji tace na kira sadauki ne don yazo ya san yadda zaiyi akan al,amari don duk kan mu nan ai matsalar ta shafa don ba wanda bai shiga tashin hankali ba daga cikin mu.
Ke da danki ya shiga wani hali a gidan nan wa hankalin shi ya tashi ina a tsakar gida ake tsayawa ai maki gori dare da rana.
Wanan kuma ai ba komai bane don kowa ma uwace ai don dan sune suma.
Amma ni idan abinda nayi laifi ne don Allah ayi hakkuri a yafe min.
Sadauki ne yai magana yace Baba don, Allah ayi hakkuri tunda abin ya riga ya faru.
Kai dakata don Allah ai kaima zanzo gareka ne watau kai yanzu ga mai kudi ko ?
Shine zakai amfani da wanan dama gurin tallafa ma alfasha idan haka ya kasance daga daya daga cikin kannen ku yaya zakuji ne wai ?
Abinda nake son ku gane ke nan idan a cikin diyan mu akaiwa wanan keta haddi haka aka gurbata rayuwan su ashe taimakawa mai fyaden zakuyi a sake shi ?
Shiru falon yayi ba,wanda yai magana kowa na tunanen zuci daga cikin su.
Sadauki ne still ya kara yin karfin halin yin magana yace Baba don Allah ayi hakuri tun da iyayyen yarinyar sun hakkura.
Ido mahaifin shi ya watsa mashi cikin takaici yace eh maganan ta mutu ma na tunda kai mai kudi ka basu kudi ba.
Amma ni a gurina wallahi case din nan bai mutu ba dayan biyu ne ko na kai shi kotu ko kuma ya yarda cewa da zaran yarinyar nan ta kara dan tasawa zai aureta.
Da sauri kowa ya ke kallon baba cikin dago kawunan su.
Imiranah da,sauri ya dago yace haba Baba wanan yarinyar yar kauye yar talla ko boko fa batayi ba.
Au baka san haka take ba ne har ka turata daki ka kwamashe ta har ka kai ga halaka ta ?
Shiru kowa yayi ba wanda yace uffan Baba yace sannan kuma kaine zaka dinga dauka duk wani nauyi nata daga yau har zuwa lokacin da za ta tare a gidan ka.
Kuma ku sani wallahi ko bayan raina duk wanda ya tayar da wanan magana ban yafe ma maishi ba.
Daga haka ya mike zai shige ciki sadauki yace amma Baba don Allah ka barshi yaci gaba da sana,an shi da yakeyi.
Baba yace wani ai nagama magana ta yaje ya nemi tashi shima, don nima nema nayi ba gado nayi ba.
Ya shige abinshi yabar su nan a zaune kowa yai jigun jigun tsakanin su, hjy Kubura ta mike tana fadi yau dai ga irin ta nan.
Yanzu kowa na da abin fadi ke nan a gidan nan tab da tsuliya bamu kadai bane masu abin fadi ashe?
Ke tsohuwar kilakiya dama nasan a farin ciki kike don haka ya faru kuma nasan duk kece mai wanan shirin.
Iyakar ki ke nan zagin wasu naji ni dadewa nayi banyi aure har mijin ki yazo ya,aure ni gani kuma gidan zama daram ba inda zan tafi wallahi.
Ba kince lokacin da na,shigo kin bani wata uku ba dashi yau gani wata uku ya shude har da riba gasu nan min.
Sai da ki shirya don kilakiya tana nan dakin ki zaune ko kinzaci bamu san komai bane wai ?
Ni ba irin hajiya maijidda bace da kike wa yadda ranki yaso wai don takaici har da taimaka maku.
Nan da Sadauki ke dan shaye shaye a baya may nene bakuyi mata ba a gidan nan.
Yau gashi ita da dan da kike mata gori kullun sun taimake ku ai da kun gane kuren ku wallahi da ankamashi fasikin banza kawai.
Nan fada ya kici may masu hjy kubura tai masu tas ta fita maji dai tana ganin su sarke tabar falon zuwa part din ta.
****** ********* ******
Ina zaune a falo ni kadai don ban tafi gurin kiran da Baba yai wa iyalin shi ba don nasan magana ce da yashafi sirin iyalin shi.
Sadauki ne ya fara shigowa falon su maryam na bayan shi, nan ya samu kujera ya zauna tare da furzo iska daga bakin shi.
Daga inda nake zaune cikin yar siririyar muryana nace sannu yaya.
Sai da ya nisa yace yauwa sannu Fatima ke ma.
Maryam tace Fatima dauko muna salad din mu, mu sha kinji.
Namike na nufi kitchen na dauko salad fruit din dana gyara mu a a cikin wani roba mai fadi da cups din da zan zuba muna aciki.
Shina fara zubawa fruit din idon shi suna a lumshe na aje mai a gaban shi nace yaya ga naka nan na juya zan wuce.
Kamar mai rada yace ki zo ki dauki kayanki inba zaki juri bani hannu da hannu ba kuma ki tsaya nasha naji ko may nene?
Wani din nayi kamar na wuce sai kuma nai wani tunane tare da dukawa na dauko cup din na mika mai,
Bai ce min kala ba ya karbi cup din daga hannu na, zan juya na wuce yace amma kinji abinda nace maki ko?
Dan guntun tsuki naja wanda ban san zai fito fili ba yace, ai da ma na barki ki tafi din yau kiga abinda zan ma shegen kunnen nan da baijin magana.
Babu shiri na dawo daga gefen shi na dan tsaya tsaye.
Yace ya haka kuma kamar wata soja can ko bodyguide, zama nayi daga kujeran gefen shi ina cewa Anty maryam ki zuba naku kada yai sanyi har nazo.
Bai ce min kala ba ya fara kurban salad din da cibin dake cikin cup din a hankali.
Ya kai cibi uku ya dago kadan yace me sunan wanan abin kuma ne wai ?
A hankali nace fruits salad ne.
Ya dan mayar da hankali ga sha can yace waya hada shi haka ?
Nace nice nayi shi dazun da safe.
Ya nuna cup din yace ina son kullun da safe da yamma idan ina gari ki dinga hada min shi.
Zan so na sha shi kafin nasha komai da safe haka da yamma kafin na kwanta.
Kaina na gyada mashi kawai.
Yace baki ji may nace bane ?
Da sauri nace tau yaya.
Maryam tace Bintu zo dauki naki mana kafin yai sanyi ki sha.
Na yunkura zan mike sai naji tasa kafan shi ya take min kafa, wani mugun zafi naji ban san lokacin da na sake wani dan kara ba da karfi.
Da sauri na daga kai na dubeshi sai naga shi sai shan salad din shi yake hankali a kwance.
Da sauri su Amira suka dago kai amma basu ga abinda nakewa ihu ba hakanan.
Gashi shi kuma yaki daga kafanshi daya danne min nawa dashi idan na dan motsa kafana wani irin mugun zafi nake ji sosai.
Kuma yaki koda kallon inda nake balle yasa alaman cirewa.
Take idanuwana suka fara kawo hawaye, mama ce tafito daga dakinta don jin karan da nayi tana tambayan maye haka kuma kikewa mutane ihu haka Fatim?
Ban ce komai ba sai dan kukan dana kara da sauri takai kallonta ga ketan da yake min.
Tace kai amma ko anyi babban banza anan wallahi yanzu mai tai maka kake mata wanan cin amanan haka sadauki ?
Kamar badashi mama take magana ba tace bazaka cire mata wanan kauren kafan naka ba da yasha buga ball.
Sai lokavcin su Amira suka gane wani keta yake min duk tsawon wanan lokacin su dai sunga kawai ina kuka ne.
Mama ta kara cewa wai bada kai nakeyi bane sadauki ?
Jin haka yasa shi daga kafan shi a kan nawa yana yamike tsaye yana fadin, ai na fada maki sai nai maganin rashin jiki a gidan nan.
Yan tsun kafan nawa a take sukai wani irin jawur dasu bansan lokacin dana duka ina murzasu ba a hankali sai hawaye nake zubarwa shaaaa.
Can na mike cikin dan dan gyasawa nafara tafiya zuwa daki ina kuka raina a bace ina fadi a raina wanan ai cin zallun ne don kafi karfi sai ka cuce ni haka kawai.
Muryan mama maji tana fadin haba kana son wallahi in maka abin da bakai tsanmami ba kan yarinyar nan.
Yanzu mai taimaka da kai mata wanan cin amanan haka, ko kaima dai ka canza ne wai ban sani ba don ban sanka da wanan halin ba haka.
Ya ce kai maji munafukan yarinyace fa har may nai mata ne wai da zata sakawa mutane kuks haka don shagwaba kawai.
Uwarka kai mata nace,
Da sauri ya dago kai yana kallon maji don ya dade baiga ranta ya baci haka ba har tai mashi wanan kalman da fada.
Sai gashi yau akan Fatima ta zagi uwan shi, maimakon yayi fushi sai murmushi yayi yace dama haka take son ji ai munafukan banza kawai.
Fita min daga shiya mara kan gado kawai kasaka yar mutane gaba da kyashi da hassada kawai.
Maji Fatima ce zanyi kyashi kuma ?
Sai ya wani dan bushe da dariya don abin ma dariya ya bashi shi har may zai kyashe akan Fatima kuma.
Yana dariya yafita daga dakin don shi kalaman kyashin ma dariya yake bashi sosai wallahi.
Yana fita su Amira suka kwashe da dariya suna cewa kai maji wai kyashi yayane kuma zaiyi kyashin Bintu kamar wata hamshakiya can.
Ta juya gare su tana fadin in ba kyashi ba mai ya kawo haka don Allah kuma ?
Wallahi abin haushi da takaici yabani Allah kuwa haka kawai katon banza ka dannewa yarinyar mutane kafa da karfin Allah don cin amana.
Ina daga ciki naji muryan ta tana kirana da karfi na amsa da na,am nafito still dan gyasawa nakeyi har lokacin.
Tabi kafan nawa da kallo har na iso gareta tace wai may kikai mashi ne yai maki haka ?
Ina kuka ina mata bayanin yadda mukayi dashi tace bar macucin banza kawai ai zai dawo ya samay ni ne.
Something is fishing, something is fishing wooo, something is fishing somewhere,
Harara na maka mata Amira ma kallon mamaki ke kuma may ye haka dan Allah bari mana kinga ta sha,wuya tana kuka.
****** ********* ******
Wasa wasa sai ga kafa ya rure min ya dan hau ya kumbura da kyat nake iya taka shi sosai.
Take ya,saukar min da zazzabi da sanyi a lokaci guda haka ya jawo kwanciyan dole ban shirya ba.
Shiko yana fita ya shiga motan shi sai gurin da yake ginan shi yanzu har kayan gidan komai anzuba mashi a gida zakace ko an tare a cikin gidan ne.
Nan Bashar yazo ya samay shi don su fara lissafi, saboda zasu yo odan kaya kwanan nan.
Bashar na shigowa yabi ko ina da kallo a gidan ya dan nisa yace,kai gaskiya fa MAN ya kamata kai aure hakanan domin barin gida haka hatsari ne ko banza kuma a ragewa Maji consurming .
Sadauki yai dariya yace, ai sai naga kaima katon tazuru ne bani kadai ke cinye abin uwata ba.
Bashar ga zauna cikin yanayin nishadi da kuzari yana cewa Allah ba,wasa nakeyi ba ni da ka ganni nan na kusa zama family man insha Allahu.
Kai dalla jacan da zancen banzan ka kullun da bai karewa mutane saurare.
Yace ai ko zakace nace don kwanan zan baka mamaki ne sosai Allah kuwa.
Sadauki ya kwantar da kanshi a jikin kujera yace gashi ko kaji tsoho yace wai ya bamu wata uku ba.
Bashar ya mika hannun shi ga kafadan Sadauki yace na fada maka kayar da wanan daukan kan naka kawai bori ya hau idan baka iya fadawa Maji ni sai na fada mata.
Da sauri Sadauki ya dago kai ya dan kalleshi yace ka fada mata may kuma?
Cikin kashe ido Bashar yace zancen yarta mana Fatima tunda naga kai wanan shegen fadin ran naka bai bari ka fadi abinda ke cikin ranka.
Kai dai wallahi wani irin dabbane dan akuya kawai don banda kuya na rasa wace zan aura sai Fatima.
Illa ne auren Fatima din don dai kana so wallahi girman kaine kawai irin naka ke cutan ka.
Wai kasan Allah?
Bashar yace niko nasan Allah sosai wallahi ko.
Ce to ni wallahi daidai da rana daya ban taba jin digon son yarinyar nan a raina ba Allah ko.
May ma zan so ga jikin wanan maikama da takarda ne wai ?
Yanzun ma saida muka kwasa da Maji akan ta kaga na gudo nan don naga maji tahau sosai har uwana ta zaga yau akan yar kauyen nan nata.
Yace mai kawai Fatima din kuma kai ?
Nan yake bashi labarin abinda yafaru yakare da cewa kasan shagwababbane kuma muna fuka shine harda kuka da ihu don uwarta taji ta zageni.
U see aina fada maka wallahi son ta kakeyi amma kana wa mutane wani noke noke haka?
Yace ban fa son iskanci idan kuma na daina kulata ace ga batu ga zance kuma.
Wai yaya kuke son mutum yayine wai ?
Don Allah ni let's do what we here for.
Sun dauki lokaci a gidan suna lissafi yadda ya kamata tare da tsara abinda ya dace suyi a karshe.
Sai sadauki yace amma gaskiya wanan riban da muka samu ina son mu kasa shi uku bashar yace inajinka.
Yace ka kwashi kashi daya kashi daya mubawa iyayen mu dayan kuma mu samu wani abin tallafawa tallakawa dashi.
Wanan ma babban shawara ne amma nawa da kace gaskiya yayi yawa ni kadai.
Sadauki No kada muyi haka dakai please kaga kace zaka yi aure soon, to dole ne kuma kaima kafara dan wani abin dogaro da kanka hakana.
For me kaga ni banda matsala ina dai samu gwargwado gaskiya ga harkan ball din don haka bawai sai kabi ta nawa ba.
Ina fatan