Showing 270001 words to 273000 words out of 373688 words
Chapter 91 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
ko lanban shi ban dashi tace kin shigesu wallahi Bintu wai ke kina ganin yadda yaya yake kaman ba masu son shi ko?
Wallahi ki kama jiki Bintu, don na fada maki shine kawai bai damu da mata ba in ba don haka ba da sai kin raina kanki wallahi.
Ki dinga kiran shi kina mai sannu da sauran tare da tambayan lafiyan shi idan kuma zai dawo ki bashi mamaki hada mashi abincin da kika san yana so ki gyara gida da jikin ki tsab.
Kada ki tsaya wani jan aji can ki mai kyakyawan taro sai kiga yadda zaki juya abinki cikin ruwan sanyi wallahi.
Kai gaskiya nikan bazan iya ko daya ba mutumin da ke har hasashen wai ina son na kashe shi idan nai mai girki yace dole sai naci ya gani kada na kashe shi.
Dariya tayi tace ku takon kainan ku ai daban yake Bintu don baku bari agane har afahinci komai.
Muna ciki bamu san cewa har lokacin sallah magariba ya kawo jiki ba sai jin kiran sallah kawai mukayi a masallacin kofan gida.
Mun idar kuma tashiga kara min wasu haske sai mamaki nake wai ita a ina duk tasan wanan abin haka ne wai?
Takwas da yan mintina mijinta har ya iso daukan ta baiji kunyan idanuwan mu ba yake ta faman shige mata ajiki a gaban mu nikan sai faman kawar da kaina nake cikin jin kunyan abinda sukeyi.
Yaya bashar ne yace Fatima bari na baki layin mijin ki don ya sauka kasan waje ko tun da magariba ya bugo min waya.
Mukai sallama dasu sai lokacin da suka tafi na samu ganawa da musa nan mukai ta hira dashi har gurin karfe goma da wani abu na dare muka shige don Amira tun fitan su maryan da ta dan fito bata kara leko falon ba kuma har lokacin da muka shige muka kwanta.
****** ********* ******
Kwance yake saman gadon dakin da ya sauka waya yayi da wani abokin shi dan kasan saudiya da suka shaku dashi sosai.
Yana gama wayan ya fara juyawa a saman gadon gami da zubawa wayan dake hannun shi idanu .
Saboda wani mugun takaicin Fatima da yake ji a zuciyar shi yau kwanan uku ke nan baya gida amma wanan yar kauyen yarinyar mai fadin rai ta kasa daga waya takira shi.
Gashi yana son jin lafiyan su amma sai yake ganin kirata gare shi kamar kasawa ne hakan.
Itama da take mace mallakin shi zaman shi takeyi bata kirashi ba sai shine zai kirata akan may ma wai ?
Don yasan koda ya kiratan ba wani magana bane mai dadi zai samu a gareta banda bacin rai da zata saka mashi kawai.
Ya kifa kanshi a filo yana tuna maganan Maji dazun da suka gausa take tambayan shi kana ko waya da matar ka yaba amsa da eh maji muna gaisawa ai ina tambayan ta lafiyan ta?
To yanzun idan maji din ta bugawa Fatiman waya tace bai taba kiranta ba ko sau daya yaya zata dauke shi a makaryaci mayaudari mara rikon amana zuciyar shi ta bashi amsa da hakan.
Take yai matukar tausayawa kan shi do min kuwa yasan acikin garari rayuwan shi take zuciyar shi ta kara bashi shawara ka kira ta kawai don ka kirata shine wani abu.
A haka har barci ya dauke shi bai sani ba sai dare sosai ya falka tare da jin barci ya kauracewa idon shi alwala ya mike yayi ko zai samu relief a zuciyar shi idan yai sallah dare.
Hakan ne kuwa ya kasance dashi don sai yaji shi wani wasai dashi da rana ma bai sa wani abu a zuciyar shi ba.
Satin shi biyu cif da tafiya sai zaman doya da manja muke da anty Amira a gidan gashi ta hana min dan uwa shakat a gidan.
Da yai abu kadan yanzu zatayo cikin shi da masifa da zagi yadda ran ta yaso ita ko haka abokan ta zasu shigo suyi yadda ransu ke so agidan.
Ta mayar dani kamar wata kukun ta can tace Bintu zokiyi min kaza Bintu zoki dauke abu kaza haka nake takure da ita a gidan.
Lokacin komawan mu school yayi ranan da zan fara fita shiga nayi na mutunci irin ta matan auren da suka san kan su.
Ga socks da katon hijjab na saka a jikina fuskanane kawai mutum zai iya gani a lokacin.
Na samu anty zaune a falo na gaida ita nake fada mata zan shiga school ne.
Ko adawo lafiya ban samu ba har na fara tafiya na tuna da key din motan da ya bani na koma na dauko na kara fita.
Motar dake a rufe tasha wanki tun jiya yaya Bashar yasa aka wanke ta aka kuma cika ta da mai, fam.
Ina fita ashe sai Amira ta leka tana fadin yar iska ki taki sayyada ai a kafa don sai dai kije titi ki hai taxe .
Babu uban da zai kaiki da mota in kince kwadayi kuka iya ke da uwayen ki ai kunkai karshe gurin yaya sadauki.
Lekawan da zatayi ta hago har na zauna a mota ina service din ta wani irin ashar ra mulmulo daga bakin ta tana fadin kan uban can motar yaya sadauki fa.
Ashe akwai bura ubah a gidan nan kuwa ko ni ban shiga motan shi ba balle wanan bakar jakar kauyen ta ce shi zata shiga.
Nikan har maigadi ya bude min get nasa kai ina ganin fitowan ta cikin matsifa ban tsaya ta kanta ba nafice daga gidan.
A cikin masifa ta koma cikin gida tana masifa da zage zage wai sam bazata yarda ba da hakan.
Tayi kiran layin shi lokaci yana gurin wasa wayan shi yana kashe bai shiga ba.
Maji takira a cikin fada take fadin maji kinga abinda kika jawowa yaya ko kamar Bintu zatace ta shiga motan yaya ta fita da ita?
Amira kina da hankali kuwa mata da motar mijin ta har kike fadan wai ta shiga ke kije ki shiga ta mijin ki mana.
Kashe wayan tayi don har kukan takaici sai da tayi a lokacin gashi sai faman kiran wayan shi takeyi bai shiga a lokacin.
Ina isa makaranta idanuwan mutane yayo kaina caaa suna son ganin wake cikin wanan irin motan haka kamar yadda mutane ke saka ido ga abinda bai shafe su ba yanzu.
Sai da na gama na kulle ko ina na sako kafana dake cikin takalma mai hill wanda duk kwakwan mace da wuya ta samay shi a kasan nan.
Zan iya cewa a lokaci daya muka shigo da maryam don a lokacin itama ta fito har ta rufe motar ko.
Ina tsaye ina gyara tsayin hijjab dina da ya sauka har kasa naji tace madam you are welcome to new world.
Dariya nayi nace ,a,a anty kema shigowan ki ke nan dai yanzun ko ?
Tare muka jera da ita zuwa cikin makaratan sai kowa ya nufi department din shi.
Idanuwa akan mu don komai na jikin mu sai ya koma sabon yayi kasancewan mu amare sabbin fitowa.
Ban tsaya wani gaisawa da mutane ba don gujewa sabawa Allah don balain tsoro gareni.
Ban fito ba daga class sai da lokacin sallah yayi na tafi school mosque inda muke zuwa sallah.
Maryam ce ta kirani ga waya tana tambayan inda nake wai muci abinci.
Nake bata amsa da ina mosque tace nasan dama baki wuce can ai gani kofa idan kin idar kifito ina jiran ki.
Nafito na samay take cewa ga abinci can da tazo muna dashi don tasan idan tanice bazanci komai har mu koma gida.
Nace a ina zamu zauna ya ustaziya dariya nayi nace nice kuma ustaziyan yau kuma anty ?
Nace sai dai mu shiga motar ki don gaskiya bazan zauna a fili ba can muka nufa muna ci muna hira akan matsalan anty Amira.
Sai after six na iso gida a gajiye dani nasamu musa a takure yana jirana don fitana da ya gaji da zama ga takuran anty Amira ya koma gurin su maigadi ya zauna.
Dakuma yagaji ya dan fita mike kafa yabi titi har saida ya gaji ya juyo ya dawo gida yana kofan gida zaune na shigo gidan ya taso da fara,an shi a tare muka shiga gidan .
Babu kowa a falon nan muka zauna muna dan hira dashi nace bari na dan shiga na dafa mashi abinci.
Dakina nashiga na kwabe na koma kitchen nafara dafa abinci mai saukin dafuwa don a gajiye nake a lokacin.
Ban san zuwan ta ba sai muryan ta danaji a bayana tana fadi ke mara kunya yanzu ashe harke kina ganin kin isa shine kika fita da motan yayana.
May kike nufi da hakan dakikayi don duniya tasan dake ko kuwa kinyi ne dan gadaran kan ki ?
Nace anty banda amsan baki ni amma kina iya tambayan dan uwan naki ai kiji daga bakin shi don shikeda amsan tambayan ki.
Wani tsuki taja ta jyya tana fadin zaki gane kuren ki wallahi na aikat hakan da kikayi.
Nace wai may ke damuwan anty Amira ne haka duk ta wani bi ta canza rayuwan ta lokaci guda.
Yaya sagir ne ya shigo gaida mu karan shi na biyu ke nan bayan tafiyan dan uwanshi yana zuwa duba mu a gidan.
Shima yaya Abdul yazo amma saudaya ya zo gidan ya dubamu yana min sheri wai yaga na canza may ye sirin ne dayake shi mutum ne mai son barkwanci da mutane duk inda ya ke sai anyi dariya.
Nafito muka gaisa yana tambaya na ba dai matsalan komai ko nace ba komai yaya lafiya kalau muke.
Bai wani dade ba mukai sallama ya tafi don irin sadauki ne shi miskiline bai magana sai wanda yaso yi dashi.
****** ********* ******
Duk muna falo a zaune musa da yashigo abinci yake ci yana kallo, sai wayana yai kara na duba nomba bata kasar nan bace ta kasar waje ne.
Nai matukar mamaki da tambayan kaina waye kuma ya kirani haka ne wai?
Har kiran ya katse ban daga ba naci gaba da abinda nakeyi tana zaune sai faman dakilan wayan ta takeyi.
Wayan ya kara kara sai naga ta kalleni cikin zargi yanzu tsoron ta nake ji don ta canza gaba daya.
Haka yasani daga wayan don gudun zargi kada ta kulla min sheri gashi yau nafita zuwa school.
Mai shi baiyi magana ba nake ta fadan Assalamu Alaikum amma shiru ba ai magana ba nace please don't called this nomba agai iam marriage woman.
Murmushi naji anyi yace wata irin matar aure ce da bata san hakkin mijin ta ba sai kuri fadi da baki.
Sai a lokacin nagane cewa shine online ashe cikin yar murya nai murmushi don kafe ni da idon da tayi tana son tasan dawa nake wayan.
Nace shine zaka kira mutum kaki magana ni wallahi har ka ban tsoro ma naga nomban kasar waje ban san mai ita ba kuma.
Mikewa nayi tsaye don barin gurin kada taji fitinan mu don nasan shi zamuyi tunda ya fara fadin haka ina fadin.
Yaya ina wuni?
Tabini da harara tana fadin munafuka kawai wakike boyewa maganan ku indai yayanane baki taba fari a gareshi.
Ina shiga daki yana fadin dan baki da kirki da tarbiya shine koki kira kiji yaya na isa balle yaya nake ke wai wata irin yar kauyen yarinya ce haka ?
Nace da iska zan kiraka ko da guguwan nomba zan bugo maka ?
Yace dan rashin kirkin ki bazaki iya tambayan ko Amira ta baki nombana ba ki gaidani.
Nace banga zan iya wanan ba don ba damuwa kayi da asan lafiyan juna ba ai ?
Yanzun kuma da ka damu aika kira kaga na samu lamban idan zan iya sai nakira.
Ke baki da kunya wallahi idan kika fada min maganan banza ko a waya ne wallahi gobe zan shigo garin nan naci maki mutunci son raina.
Nace kai dade idan kaso ma ka taso yau din nan ka iso anjima ba sai gobe ba dip naji ya kashe wayan tashi.
Tun ranan bai kara kirana ba nima dai haka ban kara kiran nashi ba har lokacin.
Maryam ce ta ishe ni da korafi inda ta matsa min akan sai nakirashi a gaban ta kokuma wallahi mu bata da ita.
Ba yadda na iya dole na dauko wayana daga cikin hand bag dina na kira wayan na shi a lokacin kuma shi yana zaune tare da Linda.
Sai ganin kirana yashigo a wayan shi da sauri ya dago kanshi tare da cewa hello,
Nace wa,,alaikum sallam.
Ina wuni yaya ya amsa da lafiya a takaice sai nai shiru maryam dake gefe na ta kafeni da ido don jin may zan kara fadi kuma.
Jin nai shiru yace min kuna lafiya dai ko?
Lafiya muke na bashi amsa a lokacin naji muryan mace tana tambaya cikin harshen tiranci da wa yake waya ?
Naji yace mata sister din shi ce .
Lafiya dai ko naga kin kirani yau?
Nace ai kaji matsalar sai ba lafiya zan kiraka dama ni sai anjima kawai.
Dakata sai na tsaya ina sauraren shi yace nasan wani ni yasa ki kirani dole ko?
Nace eh.
Anty maryam ce gata a zaune tace sai nakiraka ko mu bata da ita shiyasa na kiraka.
Ok
Maryam dake gefe na tace shit ta karbe wayan daga hannuna tace hello yaya ta damay ni fa da zancen ka shine nace takiraka mana taji lafiyan ka.
Murmushi yayi yace maryam kin san fa yar kauye ce bata san darajan miji ba balle ta san kiran shi taji lafiyan shi.
Daga inda nake a zaune nace, gara zama da kauyanci da hurda muranen banza ai muryan mace naji tana magana dakai yanzu.
Dariya magana ta tabashi don ya fahinci nasan kishi ke nan nima don har na kasa boyewa na fadi a fili.
Yace maryam fada mata Linda ce my wife to be nake tare da ita ba irinta yar kauye da batasan komai sai kauyanci da rashin kunyan su na yaran kauye.
Haushi naji nace komai kauyanci mu dai mun san darajan kan mu da mutuncin iyayywn mu dip maryam ta kashe wayan tana fadin.
Kinji halinki ko Bintu ke wanan bakin naki wai bai mutuwane nace cikin fada wallahi muddin bai daina kirana yar kauye ba bazamu taba shiri dashi ba kinji na fada maki.
Tace kai Bintu ada kema kice mashi kowa ma kauye ne asalin shi don mu kauyen mu fa har yanzu babu ko titin mota ba wuta ba ruwa.
Nace nagode anty aiko zai rana kanshi don daya fada zance mai munfi mutane kauyen tureta ai.
Ranan daga school maryam tace min mu tsaya salloon din dake kusa da school din mu gyara kan mu baki ba don da wuri muka tashi.
Wanke min akai akayi tare da zuba min kayan kamshin da tazo dasu masu kyau sai nace a dan gyara min kafana da yatsun hannu na haka akaimin gyara nafito wata yar birni dani.
Sai da zamu rabu take ce ban sa zamu hadu ba sai zuwa next week amma ina son ranan Friday don Allah kiyi girki mai dadi ki gyara gida da kanki sosai yadda yaya zai gane cewa yanzun ke ba bakauya bace don ina sa ran Friday din nan zai shigo garin suyi waya da yayana yace yana Abuja.
Muka rabu ina shigowa gida Amirah ta kasa boye haushin gyaran da nayi a zuciyar ta tace sai dai kikare haka Bintu miji kan sai dai kamahi shi.
Murmushi nayi a raina nace kai kodan na kure anty Amira dole nabi shawaran maryam.
Friday na yi kamar yadda tace sai bina da kallon mamaki Amirah keyi.
Kasa hakkuri tayi tace wa da ni yau wani kuma sheri kike son yi a gidan nan ne haka ko bakin yan kauyen ku zasu zo ne wai?
Nace anty ashe kin gane bakin kauyan mune zasu zo yau gidan kuma anan zasu kwana tare da mu.
Na gama komai na koma daki ganin biyar saura nan na bata lokacina gurin gyara jikina zakace wani gasan gwajin kyau zan tafi a lokaci don har musa kanina saida na bashi sabbin kayan da na,sayo mai ya saka yai aski irin ta matasa.
Falo muka dawo muka zauna ganin haka yasa Amira fitowa daga daki nasan ta hake ne taiwa bakina wulakanci a lokacin.
Bamu dade da zama falon ba da kamshi ke tashi cikin shi mukaji ana nocking din kofan shigowa don a rufe yake musa na tura ya bude kofan.
Yayin da Amirah ta sako idanuwan ta don ganin mai shigowa falon a lokacin don a shirye take da cin mutunci a ran ta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKK8N WASU PLEASE,,,,
IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYABA,,,,
Shine ya shigo gidan kai tsaye yana saye a cikin kananan kaya farare cikin mutunci musa da ya gane shi yake mashi sannun da zuwa .
Murna da yar tsalle Amira tayi sai a gaban sho tana