Showing 276001 words to 279000 words out of 373688 words
Chapter 93 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
nake cewa anty ashe yau zaki koma yanzu yaya yake fada min haka.
Tace eh zan koma nabarki kiyi yadda ranki ke so ai nasan kece da aanan kullin don na tare maki guri jarababban yarinyar kawai.
Haba anty may kika tare min aiko kina nan ba,a fasa abinda za,ayi kinga ashe zaman ki bai hana komai.
Bintu kada fa ki kawo min rashin kunya wai ke adole ga wace ta san dadin namiji ko ?
Dariya nayi nace anty aure ne fa kema idan kikayi zaki gane haka ba wai jaraba bane dadin aure ne kawai.
Lalai yau Bintu har nikikewa gorin aure har wani aure ne kikayi har kika san dadin shi ke.
Kai haba anty kema aikin gani gashi kuwa kamar har ya damay ki kullun kina magana a kan shi.
Da ki baro idan kayan yaya yazo ki karbi tsaraban ki zaifi ki koma hakana don kada mutanen gida suga kin dawo empty.
Dama sjine gurin ku ai ku mamaye komai nashi ya zama naki ke da yan uwanki kawai.
Ba abinda zaki taba sai nazo gidan nan don nasan halin yayana dole nice mai raba mashi kayan shi.
Nace da ke nan kuma anty yanzun kan ai akwai mairabo tsakanin ku ina fadin haka na fito daga dakin na barta tana yabo min magana.
Mun karya duk da a takure nake amma ban yarda Amira ta fahinci komai ba akan zaman mu dashi a gida.
Munan cikin karyawa Abdul ya shigo gidan nan suka shiga gaisawa da yayan shi ina gefe nace yaya Abdul ina kwana ya juyo gareni yace sarautan mata yaya kike?
Nace mai na zubo ma, abinci ko yace kaman kin san bar karya ba nace nasani mana yaya tunda gauro kake.
Bintu yaushe mijinki yai aure da zaki fara kira min gauro saurana fa kusan shekara bakwai ko takwas.
Kai yaya wallahi kada kaiwa kanka baki nasan komai fa ina Nadiya take da zakace haka?
Yana zaune yanajin hiran mu da yaya Abdul inda ya juya kan Amira yace kin shirya ne ku tafi ?
Yaya ko kaima kora na kakeyi ne kaman wanan mara kunyan yar kauyen dake fanin ta samu guri.
A,a Nafisa yaushe kuma kuka fara haka da Bintu ina Bintu tai kama da yar kauye ko ada can balle yanzu da ta zama wata princess can da ita.
Nace yaya Abdul fada mata dai ko zata bude idon ta tagani ni dai nasan akwai wata a kasa tsakanina da Anty kawai amma ni nasan nawaye ai yanzu.
Dariya magana ta tabashi yadda nai magana waina waye Amira tace kaiyya haka kike gani ashe ke don kinga yanzun kina rayuwa a cikin wanan gidan .
Abar rayuwan kauye ko nace kai anty ho ke manta ni diyar mamace tun yaushe mama ta mayar dani yar gatan ta.
Dama ai shine gurin ku ashigo a mamaye komai ai aleale sai yadda akayi da dangin miji ko?
Kai Amira tashi ku tafi please bani son irin maganan nan for god sake kaunan kice fa kubar wanan irin maganan mana ?
Yaya Bintu ce kaunata ko wa shiru yayi yadda na fahinci baiji dadin kalaman ta ba a gare ni.
Kallon mamaki take mashi tamike tare da shiga dakin da ta mayar nata ganin tafito da jakar tasa namike zan karba.
Tace kada ki soma taba min jakkana munafuka zamu zuba ni dake don babu gurin zama agidan nan gurin ki.
Ido muka hada yai min wani shu,umin murshi na mugunta tafita batare da tace dashi uffan ba.
Mikewa yayi yabi bayan su ina mata agaida mutanen gida.
Gurin da mukaci abinci na gyara muna tare da kawar da duk wani abinda ya dace a gidan .
Daki na koma ina zaune ban san barci ya dauke ni ba a gurin can yadawo suna falo da musa ya mike zai fita yace ina zaka tafi ustaz yace akwai inda nake fita gurin mai shago muna hira ko dasu maigadi.
Yaron nafita yaji zaman falon ya ishe shi don haka ya mike zuwa waje jin dayayi shuri ban fito ba yashiga dakin.
Dakina ya shiga ina kwance na dunkule saman gado kamar wata yar jaririya dani.
Kallon yadda na dunkule kamar mai jin tsoro yayi ya dade a kaina saida na dan gyara kwanciya tare da kara dunkulewa yabar dakin.
Ikon Allah sai gashi nai mafalki da Kabi yanace min Fatima yau ina iliminki da,wayon ki suka shiga.
Kina kokari kasa cin jerabawan ki zaki halaka kanki kin kuwa san irin dumbin masifan da zaman dakika zaba da mijin ki yake haifa maki?
Ubangiji babu ruwanshi da halin shi rayuwan biyayya da zaman takewan ku zai duba abinda yakeyi tsakanin shi da Allah shi ne.
Muddin baki bi mijinki ba Allah zai kamaki da laifin haka, kuma makomar ki shine wuta.
Fatima kibi mijin ki kinji sauda kafa don Aljananki yana karkashin kafan shi ki faranta mashi ko yaushe kinji kaunata kad ki halaka kanki.
Sai nafara kuka murmushi naga yai min kawai yajuya yafara tafiya kaman cikin wasu duhun itatuwa ya bace abinshi.
Zubur na mike tare da salati sai zufan da yafara karyo min a goshi na kawai duk da A C dake aiki a dakin.
Kabir na furta a fili wasu irin hawaye naji suna zubi min nace Allah ya jikan ka bawan Allah kila sadaka yake so nai mashi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,
IDAN KUMA K8N BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA NA BARKI GA ALLAH YAR UWA,,,,
A LOKAC8N MUKE,,,
Tun ranan da wanan abin ya shiga a tsakanin mu na kasa sakin jikina a gidan.
Ban yarda mu hadu da yaya sadauki ko da a falo ne ganin na dan samu sauki yau natshi tunda safe ina son shiga school kasancewa monday ce yau din.
Tsaye nake a bakin zinc na kitchen ina dauraye kayan da akai amfani dashi daren jiya.
Ga kuma girkin dana dora ina sauri ingamawa kada na makara ko ya futo yasamay ni ban fita ba.
Jin kaman mutum tsaye a bayana yasani sauri juyowa ina kallon kofa shigowa kitchen din, .
Gaba nane yai mugun faduwa da ganin shi yana tsaye ya saka hannayen shi biyu ya raba kofan tsakiya jikin saye da kayan exercise din shi sunyi matukar yi mashi kyau a jikin shi.
Dan daburcewa nayi daganin shi bansan lokacin da nakai kasa ba a tsorace ina cewa ina kwana yaya.
Bai amsa ba,sai karasa shigowa daga cikin kitchen din da yayi gaba daya ina durkushe.
Tsayawa yayi tare da jingina jikin shi da bayan inda nake tsaye da farko yace wa kike boyewa kwana biyu a gidan nan.
Mikewa nayi don ganin bazai amsa min ga tambayan da ya jefo min kuma lokaci guda.
Fuskewa nayi nace may zan boyewa kuma ni don banda lafiya ne kawai.
Murmushi yayi yace may yasamay ki baki da lafiya kuma?
Turo baki nayi na karasa dauraye plate din dake a hannuna, na juya ji nayi ya finciko ni tabaya na.
Tsoro ne ta kamani jikina ya dauki rawa a lokaci guda don balain tsoron shi nake ji yanzu .
Idanuwa na a runtse tare da sauraren abin da zai biyo bayan rikon da yai min a lokacin.
Hannuwan shi naji saukan su a saman kirjina tare da rankofo kan shi a daidai wuyana a hankali.
Yana fadin abinda kike min rowan su ke nan gasu yau na kama su a hannuna.
Idona na ritse gam don jin abinda yaya ke min wanda ban taba ma kawo tunen hakan ba a tsakanin mu.
Cikin wata yar murya nace da kyat don darajan Allah yaya kadai na wanan abin please ?
Don Allah ka bari kada musa ya shigo ya samay mu a haka please.
Murmushi yayi yace idan yashigo and so what bada matata ya ganin ba.
Kara rintse idanuwa na nayi cikin rashin fahintar abinda yake min a lokaci zafi ne ko haushi ko ko dadi.
Da karfi na zille daga jikin shi na koma gefe ina mai da numfashi kaina a duke.
Murmushin keta yai min yana cewa matsoraciya kawai yau ina bakin naki yashiga kuma mai fadar bakat magana.
Idona da yakawo hawaye na dago kai nace don wanan cin zalin da ka dauko yi min a gidan nan bashi zai sabakina ya mutu ba ai mugu kawai mai ruwa biyu.
Murmushi yayi ganin da nayi ya juyo kamar zai yo kaina na zille akasa tare da kare fuskana da hanaye na sai naji yai dariya yace ashe bake bace ?
Har ya kao kofa ya juyo ya tsaya yace, kuma idan na kara shigo na samu kin boye zakiga abinda zan maki gidan nan.
Yana fita na sauke ajiyan zuciya tare da mikewa na karasa abinda nakeyi ina yi ina kwallon kofa kada ya dawo again.
Sauri sauri nagama komai tare da shiryawa zuwa school don lokacin har dining sai dana hada komai na fito a cikin hijjab dina kamar kullun.
Naso nafita batare da na,sallamay shi ba sai naga rashin dacewan hakan gareni don haka na nufi dakin nashi.
A hankali na tura kofan daki da yar sallama a bakina, yana kwance saman gadon shi yai rigingine fuskan shi na kallon ruffing din dakin nashi.
Daga kofa na tsaya ina fadin zan tafi school, sai na dawo.
Da kyat ya iya dago kanshi idanuwan shi kamar yafara barci ne a hakan.
Kallo na yayi tun daga samana har kasa na sai ya mayar da kan shi yana fadin akwai mai a motan, nan kuwa nace ranan da na fita last akwai mai a cikin sa sai dai ban sanar ma yau din nan ba.
Mikewa naga yayi ba tare da yai min magana ba yafita a dakin nima bayan shi nabi muka fita a tare dashi .
Motan ya bude ya shiga ya tayar da ita ya dan dade a cikin ta yana service din motan ina tsaye daga gefe ina kallon shi.
Yafito daga cikin motan bayan ya gama warming dinta tare da ce min sai kin dawo ya juya ya shige gida.
Mun hadu maryam a school duk yadda taso ta zolaye ni taji yadda muka kwasa da yaya sam naki bada fuskan yin haka.
Dole ta gaji ta kyale ni muka canza hira kan hiran matar yaya Ahmad da akace sunyi fada har da buge buge har gurin yan sanda sukaje.
Amma kuma sun dawo anshirya kamar basuyi ba nace ai dama irin su irin matan nan yan duniya ne daidai dasu.
Tace ita kuma matar yaya Imirana ance kazama ce kumai tana dan kurba syrup akai akai,
Sai dana gama saurare nace wai ubangiji Allah ya kyauta kawai zamuce ga al,amarin don yanzu abubuwa daban daban lokacin nan da muke cikin ta.
Ba mu dawo gida ba sai yamma lis after six na shigo gidan agajiye dani daki na shiga na cire hijjab dina na fito kitchen don dora girkin dare.
Misa ne yashigo yana ce min sannu da dawowa yace yanzun ko yaya ya bargidan nan yana tambayan baki dawo ba.
Nace may zan mashi idan na dawo din sallon son yaiwa mutum muguntan shi dayasaba kawai.
Kai haba anty yayane kuma mugu ni dai wallahi yana bani shawa wallahi don ba ruwan shi rayuwan shi akwai sauki sosai.
Murmushi nayi a fili a zuciyata nace baka san komai ba yaro da baka fadi hakan ba.
A gurguje na hada girki na koma dakin shi dake a hargitse na gyara mashi tare da wanko bayi na feshe ko ina da kamshi nafito nazo na samu shikafan dana dora ya tsane na tuka tare da kwashewa.
Kafin a gama kiran magariba na gama hada komai na shige dakina wanka nayi tare da dauro alwala nafito.
Ban daga ba sai da nai sallah ishai na fito tare da kara feshe falon mu da kamshi kafin ya shigo gidan.
Na koma na zauna tare gyara jikina wani riga da wando na saka daga cikin kayan lefe suke English wear ne na gyara gashina da ribon jelae shi ya sako a baya.
Dan karamin gyale na yafa ga kaina na fito falo na samu musa ya shigo nace mai ya dibi abinci yaci dare ya soma yi.
Ya dabe ya dawo inda muke zaune ya faracin abincin muna hiran mu ta zumunci labarin rayuwan garin sokoto da ya gani yake bani ina dariya.
Haka yasa bamuji shigowan shi ba sai ganin shi mukayi har ya kawo tsakar falon.
Sannu da dawowa muka fara mashi ya amsa tare da zubewa saman kujera da alaman daga gurin wasan su na ball ya fito a lokacin.
Sai ya kasance shigan da nayi na takura da zama falon dan wani kallon da naga yai min ya wani lumshe idanuwan shi.
Can ya bude bakin shi da kyat yace musa ina gani gobe zaka wuce school don an gama maka shirin komai ko.
Daga ni har musa dago kai mukayi muna kallon shi a cikin kasala yake maganan shi yace.
Ban san ko akwai wani abinda zaka bukata ba kaje cikin buth din motana ka kwaso abinda akasoyo ma ka gani idan akwai abinda zaku kara sai ku duba ku gani.
Mikewa musa yayi yafita yabar abincin don dauki sai lokacin na dago kai na kalle shi ya rike goshin shi da hannun shi daya nace yaya mungode Allah ya saka da ,,,,,,
Hannu ya daga min yace is ok please nima ai kanina ne musa.
Kara cewa angode bai yi magana ba sai mikewan da yayi ya bar falon tunawa nayi ban hada mai ruwan wanka ba a lokaci da sauri na mike nabi bayan shi.
Na samay shi a tsaye yana kokarin cire kayan jikin shi sallama nayi na shigo ya bini da kallo kawai.
Bathroom na shige tare da joner mashi heater ruwan zafin da zai yi wanka dashi.
Nafito bayan na matsa mai su maclean da subulun da zai bukata na aje mai a gefe nafito din.
Nazo zan wuce yana daure da towel iya kugun shi da sauri zan wuce naji ya finciko ni zuwa jikin shi.
Yar kara nayi nace cikin wata irin murya wayyo yaya please kayi hakkuri don Allah matse ni yayi gam yana kokarin hada bakin shi da nawa.
Sai kokarin zillewa nake don gaba daya balain tsoron shi yanzu ya cika min zuciya na don bangane wannan son yawan hada jikin shi da yake son yi dani ba akoda yaushe.
Sosai ya tsayar dani sai tsotson bakina yake cikin wani irin sallo da shi yasan irin shi.
Kafafuwa na ne naji basu dauka na a lokacin gashi ya cika min baki da harshen shi ban iya maganan komai a lokacin jikina sai kyarma yake min.
Shi kan shi yaga dama ya sake ni tare da bina da shu,umin dariya yace zamu hadu dake ai matsoraciya kawai.
Sai dana sai ta kaina a tsaye inda nake tare da bin bayan shi da zai shige bathroom.
Lokacin ne na kara sheda girman jikin yaya sadauki sosai ashe karfafan mutum ne haka ban sani ba.
Na samu musa a falon ya kwaso kaya gasu nan birjit a gaban shi.
Jakkuna na kaya guda biyu na hango sai na karasa gurin yace anty kinga abinda yaya ya sayo min haka.
Nan muka shigo budewa daga kaya sawa takalma uniform sai kayan abinci na gwagwani da na sha su madara da sauran abubuwan sha.
Kallon kayan nake cikin mamaki don ba karamin kudi ne aka kashe ba gurin sayayyan wanan kayan masu yawa haka su bucket da kulan da zai ci abinci duk an sayo mashi man shafi su maclean da sabulun wanki dana wanka da turare.
Musa yace kai yaya I love you wallahi ban ma san irin godiyan da zan mashi ba idan yafito wallahi.
Murmushi nayi kawai naji dadi kwarai a raina don nuna kaunan da yayi wa dan kanina haka.
Can yafito cikin wasu yan kananan kaya a jikin shi rigan mai dan karamin hannu iya hammata sai wando three quater da yasa fari kal dashi sai kamshi ke tashi a jikin shi.
Direct dining erea ya nufa hakan yasa na mike na nufi gurin tare da daukan flask na fara zuba mai tuwon shikafa fara da miyan water leaf yaji agushi sosai da nama.
Dan kadan na tsakurawa kaina a plate a shiririce nake ci inda ya zauna ya kwashi abincin shi sosai.
Sau biyu yake cin abinci a wuni da safe idan ya karya sai kuma da dare wani lokaci kuma fruits salad kawai zai sha yakan ce wai ina son dirka mai abinci yaci yai kiba kwana biyu ya kasa yin wasan shi.
Waya yake yi yana kallon yadda nake wasa da abincin dake gabana duk da rashin yawan da baida shi.
Da ido yai min magana alaman maza na cinye shi na make kafada na alaman banyi, sai dai ban daina cin da nakeyi ba a yangance.
Mikewa nayi tsam na fara kwasan kayan zuwa kitchen ban fito ba sai da na tsaya na wanke kayan don na rage yawan aikina da safe.
Na dawo nasamay shi da musa yana gwada mai wasu takardu