Showing 267001 words to 270000 words out of 373688 words
Chapter 90 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
rufe kaina gyara min kwanciya yayi ya kashe A C dake aiki a dakin.
Yafita falo ya koma ya zaina shida musa yana fada ma musa wai yau banda lafiya ne shiyasa nake kwance.
Can yaji anshigo gidan ya daga kai Bashar ne ya gani yace cikin daure fuska kai kuma may yakawo ka ne wai nace ma yau hutu nake so fa.
Yace au don nazo nayi laifi ke nan ko yace dana sani na wuce school wajen madam dina yafi min zuwa nan ai min wulakanci haka.
Ya zauna yana fafin kaunata tana school ita ma ko ?
Yace bataje bata jin dafin jikin ta yau da sauri bashar yace subbahanallahi may yasa may ta kuma ?
Sai da yai dan tsuki yake cewa fever ne kawai ke dan damun ta.
Kallon yadda sadauki ya daure fuska yayi ga dariya nadon kamashi amma ya dake inda ya yakushe shi a wuya da gefen fuska dana wuya yace subbahanallahi may kuma ya yakushe ma fuska haka kamar kayi dabe da mussa haka?
Yace kai dan iska ban sani ba mutune kaman yan jarida dakai da matarka ban san wanda yafi gulma ba wallahi.
Don Allah daka ta man kaman fa kasha yakusa nake gani jiya dakata mu gani mana.
Filon kujera dake gefwn shi ya dauka ya jefa mashi a fuska ya cabe yana cewa oho yanzu nagane kace min ka shigo gari kawai mutumina.
Fita min gida kaima watau munafukan matar ka taje ta fada maka shine kazo don ka karas da idon ka ko ?
No kadain kiramin da mata munafuka ni Maryam bata dawo gida ba tana makaranta kuma ba abinda ta fada min zuwa nayi mutafi illela gurin zancen kayan nan da zasu shigo muna.
Yace cikin taba baki ni yau ba inda zan tafi don wanan raguwar banzan ta kawo min cikas sai shegen rakin tsiya kamar wata jaririya can da ita.
Kai man wallahi ka fadi gaskiya abinda ake lalashin mace kodai kai kai mata may gaba daya ne wai ka illanta masu yarinya ga banza saboda alluran ku na yan kwallo na maka caji ko ?
Kaidai dan iska ne wallahi bashar kashe ta ma nayi ba illantawa ba bar gida don Allah naji da abindake damuna ni please.
Sai yaja tsuki yace ni wallahi maji ce bani ma son taji zancen nan Allah, bashar yace a ina zataji shi.
Gurin maryam mana bashar yace haba kai ina tana ma fara fadin wan nan magana ina bazata fadi ba zanyi warning din ta ai.
Amma sai dai sun makara don suna magan har maryam takira wayan mama tana fada mata cewa maji yaufa sai ki dafawa yarki bagaruwa don komai zam wallahi.
Murmushi maji tayi tace masha Allahu nan take cewa sai dai bata da lafiya tana can nade kuma na tafi yaya ya kore ni.
Suna gama waya mama tashirya sai gidan mu wanan ne karo na farko da tazo gidan namu tun bayan gama bukin mu.
Suna hiran su a falo suna dariya sai jin sallaman ta sukayi a falon kawai.
Damm gaban shi ya fadi ya dukar da kanshi a kasa haka kawai yaji yau ba zai iya hada ido da maji din ba karo na farko kenan a rayuwan shi.
Suna gaishe ta bata tsaya amsa masu ba da dadi take fadin ina dakin fatiman yake ne da hannu ya nuna mata.
A hankali tasa hannu ta daga bargon da nake ciki a rufe a lokacin saboda maganin da nasha har na fara zufan jin sauki fever ya dan sauka min sai dai jikin nawa akwai sauran zafi still.
Jin an tabani yasa na dan bude idona a hankali mamace na gani tsaye a kaina tace Fatima yaya jikin naki ina kokarin tashi take ce min koma ki kwanta abinki.
Kinsha magani ko nace mata cikin karfin hali eh mama ta kara min sannu da jikin na amsa da kyat tare da dan mikewa zaune na dukar da idona sam ban iya hada ido da mama din yau.
Bathroom naga ta nufa saida ta cika kwamin wankan da ruwa ta kawo wani gari ta zuba tace na tashi nashiga ciki na zauna zan dan ji daman jiki na taimin sallama ta fita abinta.
A falo ta samay sunyi zaune zugun da su sai jira yake yaji fadan da zatai mai sai dai tanafito ta dan zauna tana cewa nashigo ban tsaya mu gausa ba hankalina ya daga naga hakin da diyata take ciki.
Tace sai ai ta hakkuri da mata Allah yai maku albarka yabaku zuria dayyaba na gari masu albarka irin ku.
Ni zan koma sai anjima kazo ka dauko maku abinci kazo dashi tunda nasan bazata iya komai ba ita.
Mama ta mike ta fita tana masu sallama ta wuce zuwa gida nan ta barsu zaune cikin kunya.
Yace sai na batawa maryam rai wallahi haba dai akan may kuma may taimaka zaka saba mata kuma daga taimako
Kwarai naji dadin abinda mama ta taimaka min dashi haka yasa dana fito ban kwanta ba sai yunwan da nake ji kawai.
Shigowan shi dakin yasani saurin dukar da kaina yace yaya jikin naki da sauki nace mashi kawai.
Kin karya kuwa ya tambaye ni cikin son sani ko na karya sa safe nace a,a a hankali juyawa yayi yafita daga dakin.
Zuwa can sai gashi ya shigo dauke da cup din tea mai kauri a hannun shi daga gefe na ya zauna tare da mika min cup din.
Yana fadin ki shaye shi don ki dan kara samun saukin jikin naki wayan shi ce tai kara ya dauka sai da suke magana na fahinci da mama suke magana .
Yadda suke magana na fahinci mama tana cikin matukar farin ciki da walwala a tare da ita tana cewa ka fara ganin al,amarin Allah ko.
Nikan raina kamar an fasa min guduma tsakiyan shi nake ji don nasan dada shike nan ni tawa ta kare ke nan.
Shiko sai wani lumshe idanuwan shi kawai yake abu ya taru yai mai yawa a zuciyar shi.
Na farko tunanen irin ni,iman da ya diba daga jikin yarinyar da yake ma kallon kitse saman ruwa don bai taba zaton haka zai samu ba daga gurin Fatiman daya raina da farko .
Suranta sai gizo yake mashi a idanuwan shi ya kasa mantawa da abubuwan da suka faru a tsakanin a daren jiya din.
Idon shi ya sauke ga dogayen yatsuna dake rike da kufin da nake kurban shayi a hankali bai san lokacin da ya sauke wani irin ajiyan zuciya ba wanda har yasa na dago kai ina duban shi.
Sai kuma nauyi da kunyan yadda ya kasa sarara min har takai yai min rauni a jiki ance dama dan hakin da ka raina shikw tsona maka ido.
Nauyi da kunyan maji sun rufe mai zucita don bai taba tsanmanin cewa akwai wani rana da zaiji nauyi da kunya maji ba sai ya din nan.
Kofin nake kokarin ajewa a gefe ya kura min ido cikin daure fuska yake cewa kin shanye ne.
Na dan marairaice ina cewa, nasha yaya hannu ya miko min yana karban cup din gani sauran tea a ciki yake cewa wanan fa ?
Na dan marairai ce nace na koshi yaya please tausayi na bashi ya dauki cup din ya fita dashi.
Ba,a dauki wani lokaci ba saiga sako daga mama ferfesu ne na kaji da kayan cikin rago sunji kayan kamshi na gargajiya, sai kuma gassan naman rago mai zafi .
Da kanta ta bugo min waya akan na tashi na ci abin da akakawo tare kuma da jaddawa yaya akan ya tsare ni naci sosai.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,
IDAN KIN BIYA KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH,,,
A LOKACI MUKE
Washegari kamar yadda na saba tashi na kamala muna abin karyawa ina yi ina duban kofan dakin da Anty Amirah take ciki har na gama bata bude kofa ba.
Wanka nayi na gyara jikina duk da ba wani kwaliya nayi ba amma nayi kyau zani da riga ne na atamfan super the most classic one na daura.
Falo na fito na fara karyawa sai da na kusan gamawa ne, na ji ta bude kofan ta tafito daga dakin.
Cikin murmushi nake gaishe ta, inda ta amsa min cikin ko in kulla tare da zuwa tafara bude abinda na girka muna.
Sai can bayan ta zauna take cewa yanzun duk wanan abinda kika dafa haka wa zai ci su ne wai?
Nace dani dake ne fa anty sai masu gadi da zan dibanwa nakai masu.
Humm,ummm lalai dan tallaka bai iya samun guri ba wallahi, Bintu tun ba,a je ko ina ba kin fara wanan nan irin barna haka ?
Nace haba anty ina kuma barna haka ni dana tashi gurin mama ne kuma zan ce na yi barna.
Masu gadi fa har mutum uku ne gidan nan kuma shi da kanshi yace na dinga basu abinci suna ci.
Dakata Bintu may yakawo zancen yaya a nan magana ce iya ni dake mukeyin ta ko?
Kada ki soma kice zaki raba muna zumuncin mu da dan uwan mu don tare kika gan mu ke haye kawai kikai muna daga sama.
Kodan maji ta cuce shi ta mashi wanan cushe na auren ki har kike ganin kamar ke wata tsiyace yanzu.
Bari kiji koda ace auren so kukayi da yayana wallahi ke Bintu kinyi kadan ki rabani da dan uwana ana magana kin wani kawo zancen yaya kin saka a ciki mafari ki samu wani sheri ki kulla kice nace kada kiyi abinda yace kuma.
Kallon mamaki nake mata nace haba Anty may nai maki ne haka wai yanzu kike nuna min irin wanan rayuwan a tsakanin mu nifa kaunar kice anty.
Koshi yaya din bai gwada min irin wanan kiyayyan da kika dauko gwada min .
Yar uwar wa ai dake yar uwatace da killa zan dan raga maki ta wani guri amma ina hadin kifi da kaska kuma.
Sanan shi yaya ina yaga gurin nuna maki wani abu kisa uwarshi ta tsine mashi yana zaman zaman shi akan wata banza can.
Anty nice banza kuma yau ?
Kila da hafsatu nake magana .
Cewa mahaifiya ta data haife ni wai da ita take magana na dago cikin mama idanuwa sun kawo kwalla nace nagode Anty.
Kada ma ki gode din don wallahi ki sani Bintu nifa na tsane ki a rayuwana tunda kika sa maji taiwa yayana haka.
Murmushi nayi tare da mikewa ina kokarin daukan kulolin abinci na juye wa su maigadi nake cewa nagode babu komai.
Ina juyawa naji tana fadin mace a haka ba gaba ba wani fasali na mata kamar solama dake.
Mamaki nake ina tafiya yadda cikin dan lokaci ta sake akaina gaba daya duk ta manta da rayuwan mu a baya don kawai wanan auren na dan uwan ta da aka sakaniyi bada son raina ba.
Naji tana fadin wallahi duk wani muna funcin ki ke da gwagon ki tun farko na fahince ku kwadai ne kawai yakawo ku dama cikin rayuwan mu.
Allah ne shedan hakan kuma nace mata batare da na juyo ba tace ko kina so ko baki so sai wata tashigo gidan nan yar arziki taci arzikin yadda aka iya cin shi.
Haka zaman mu da ita ya kasance a gidan ba ruwan wani da wani har zuwa karfe hudu na yamma.
Sai iko da mulki take zuba min a cikin gidan har na kwammace dama ni kadai na zauna dayafi min.
Sallama yaya Bashar mukaji a falo ganin yadda muke a zaune yasa shi fara fahintar akwai matsala azaman mu da Amira a gidan.
Jin ayi wani sallama yasa na dago da sauri anty maryam ce sai kani na musa biye dasu da yar jakar kayan shi a hannun shi.
Na rasa wa zan tara a cikin su don murna na rugumay maryam ina murna tare da fadawa jikin ta.
Itama murna da ihun ganina takeyi sai wani uban tsoki da mukaji anty taja tare da mikewa tabar falon ta dan kalle tace taufa matsalan da kuma aka kawo maki kega a gida yar uwa.
Nai murmushi nace aikin san anty hukuma ce sai lalashi don ita halinta daban yake kin san.
Na juya gurin kanina ina mashi sannu da zuwa tare da tambayan shi mutanen gida na dago kai nace wa yaya Bashar nagode yaya yace ba ni bane mijin ki ne yace na dauko maki shi ai.
Yace madam ni zan tafi sai after eight zan dawo mu tafi lokacin kun gama gulman ku.
Mukai dariya na ce yayana ai bazata fara tai min gulman ka ba nakyale ta yace haka ne fa kuma Fatima shiyasa nake yin ki.
Yana fita na kawo masu abinci maryam ta harare ni tace ko kin man ta nima madam ce yanzu sai dana girka mukaci muka fito.
Nakai kani na dakin dake farkon shigowa falon wanda ina ganin dan baki aka gina shi.
Muka koma dakina muka baje dama ta matsu ta samu abar mu, mu biyu mu wala.
Dakin tabi da kallo tace dankari gaskiya Bintu yaya yayi kokari wanan irin daulan haka gaskiya ki godewa Allah da hakan.
Nace da mama kuma ko da tai sanadin kawoni ciki ko?
Nace, anty maryam nifa duk wanan bai a gabana kawai dai ni gurina mu samu zaman lafiya a tsakanin mu.
Ta dafani tace, haba Bintu ki kwantar da hankalin ki komai zai zamo daidai a tsakanin ku da yaya.
Tun da safe fa shi ya tayar damu daga barci akan aje yau azo maki da musa tunda kince kina son yazo,
Bai dade da kiran shiba kuma sai ga maji itama ta kiramu tana fadin aje a zo maki da dan uwan ki don ta san Amirah ba zata tsinana maki komai ba.
Nai murshi kawai tace kai Bintu aure fa rahama ne wallahi, sai yanzu na gane dalilun da yasa iyayye kan damu da yarsu tai aure ashe.
Kin koga yadda yayana ke wani haba haba dani ko kuda bai son ya tabani kuma da zaran ya ga na dan shiga damuwa ya shiga tambayana ke nan may ya samay ki may yafaru kuma.
Tace kai bari ke dai yanzu ga yaya ya bata ni idan ban ji shi a jikina ba wallahi har damuwa nake shiga wallahi.
Dariya sosai tabani nace kai anty maryam wallahi baki dai barin halin ki watau, tace bari mutumiyar wallahi duk na matsu na ganki na dan baki wasu hit,.
Nan dai tata min hiran irin rayuwan dadin da suke yi da yaya bashar sai nake ji ashe ni ba ma aure nayi ba.
Jin nayi shiru sai sauraren ta nakeyi, tace yaya kuma kin barni sai faman zuba nakeyi ni kadai na san dai yaya sadauki yafi yayana waye wa.
Murmushi nayi nace anty kufa auren soyayya kukayi da yayana bashar niko da akai mashi dole akaina ina zan samu wanan daulan haka.
Allah dai kawai ya kyauta ga sabon fitina anty Amira abinda take fada min ko wanda akaiwa dole a kaina bai gwada min hakan.
Tace dan Allah fita batun ta yar bakin cikine ita da fadin rai ta dauki duniya da girma ita.
Tace ni yanzun dai na fahinci tunda kika shigo baki samu kan yaya ba ke nan ko?
Nace kamar yaya anty ni har wani kan shi zan samu can mutumin da akai mashi dole a kaina.
Tace ji nan Bintu kefa mace ce kuma ki tuna aljannan ki ta na a,karkashin kafan shi ne don haka idan zaki kama jiki ki ma gurin gyara gidan ki.
Nace anty wani gyara kullun fa sau biyu nake gyara gidan nan a wuni may kuma ake bukata bayan hakan ?
Kai amma ke ma Bintu ashe da gaskiya ke yar kauye ce wallahi.
Dalla ni ba gyaran gida nake nufi ba kinji ki saurara ki ji ba wani boyo ko kunya a tsakani na dake don ke yar uwata ce Bintu.
Da farko zaki fara shiga ta daukan hankalin shi ta yadda don ubanshi sai ya gigice a kanki badon Allah ba shifa namijine.
Namiji kuma kamar kenwa yake gurin son jiki abinci mai jan hankali zaki dinga mashi.
Sai tai shiru can tana fadin ke Bintu ke ma yar iska ce wallahi don nasan yanzun haka yar tsama kuke a tsakanin ku kuna yabawa juna magana.
Nace idan ya fada min nima ai dole na mayar mashi tace kin fadi wallahi.
Kwaran ki yake don kece da zunubi duk abinda zai fada maki ke yazama wajibi dole ki kwanta don kece a kasa.
Ladabi ya zama dole yanzu akanki idan abinci zaici ki tabbatar kina zaune tare dashi, ruwan wankan shi da suturan da zai sa duk kece da Alhakin hakan don ki sani.
Tace gyaran dakin shi duk a kanki ya rataya idan ya dawo sannu da zuwa idan zai fita Allah ya tsare ya bada sa,a.
Duk kika tsare haka wallahi ko baiwa Allah nina fada maki dole ya sauko ku daidata a tsakanin ku.
Gama sauki yanzun yadda yai tafiyan nan waima kuwa kin kirashi kuwa?
Nace ni kan