Showing 339001 words to 342000 words out of 373688 words

Chapter 114 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

Advertisement

dani don dama tare muke itace ke ta fama da lalura na ko a gida.
Hankalin kowa a tashe don yadda baba yake matukar jin jikin shi ko matsi bayayi sai na,uran taimako da,aka saka mashi ke aiki.
Zancen karan da akayi an tsayar da magana dole sai anga Ahmed anji ta bakin shi za,a,san yadda za,ayi.
Gashi har lokacin bai dawo garin ba kullun akaje gidan baya gari Jamila take fadi.
Ashe ta dawo ya samu labari gurin wani abokin shi shine yake boyewa kada su ganshi.
Sai dare sosai yake komawa gida ya kwanta tun da safe ya bar gidan ya koma maboyan shi ya boye.
Duk wani dan gidan hankalin shi a tashe yake yadda baba ake hasashen ya samu faralazy ne barin shi guda na dama.
Gashi har zuwa lokacin yana unconscious bai san inda yake ba sai cewa likitoci keyi akwai improvement ga lafiyan shi.
An yanke shawaran za,a fita dashi waje wani abokin sadauki likita yace a kawo shi gurin su su duba shi a Germany.
Komai an cika na tafiyan su waje da baba lokaci kawai ake jira na fita da mummu kawai sai shi sadauki da,Sagir aka shirya tafiyan da za,ayi.
Ina zaune Iyya tana tsaye a kaina ta wade min lemo zan sha ya shigo dakin zai min sallama.
Tana ganin shi ta fara gaudashi tare da mashi yaya maijiki yace Alhamdullahi Iyya zamu tafi yau da,daren nan lagos gobe da safe zamu daga dashi.
Iyya tace kai duniya gaskiya wanan yaron wallahi bai kyauta muna ba wallahi wanan sallon yaudaran nashi yayi yawa ina zai kai alhakin wanan bawan Allah da,sanadin shi ya mayar haka ?
Ya tako zuwa inda nake ina tsotson lemun da Iyya ta wade min a hankali yace yaya jikin naki Fatima ?
Nace naji sauki yaya yaya jikin baba din yake ya dan lumshe idanuwan shi a hankali yace yaji sauki yau insha Allahu zamu tafi.
Ki kula da shan maganin ki Fatima kin dai ga yadda kike fama ban how long zaki yi ba anan yadda likita yai min bayani zasu dan rike ki suga yadda jikin naki zai kasance kafin su sallamay ki daga nan.
Idanuwana na lumshe ina jin wani ba dadi yace naso mu aikawa mutanen gida don su san halin da kike ciki amma maji ta hana tace kada mu tayar masu da hankslin su suma.
A bari har aga yaya jikin naki zai kasance tukun sai a fada masu amma ni naso su sani kila za,a samu wanda yazo daga can ya zauna dake.
Shiru nayi ban da ta cewa sai dai naga aiko yayane ya kamata a basu hakkin su a matsayin su na mahaifa na.
Don idan sunji bazasuji dadi ba daga baya sai dai banda yadda zanyi don ban da tacewa ni yanzu.
Muna tare muna hira jefi jefi dashi wanda na lura bai a cikin hankalin shi a lokacin.
Yace zai tafi gida ya shirya ya bar zancen makarantan Sa,ade a hannun bashar yana ganin zuwa wani Monday za,a kaita makaran ta.
Musa ma Bashar zai kula da zuwa mai visiting kamar yadda ya saba zuwa mai.
Nace na gode a hankali ya mike yace zai tafi ya dawo idan ya kimtsa nace Allah ya tsare ya fita.
Da yamman ne wani abokin bashar ke fada masu cewa yaga yaya Ahmed yana garin don sun hadu dashi da rana a,wani shago yana sayayya.
A gida kuma mama Asiya da yan uwanta suna cikin matukar tashin hankali sosai don tana gudun wani abu ya faru da mijinsu a sanadin dan ta.
Wanda tasan ba zasu yafe mata ba don halin da danta ya jefa gidan ko yanzu bata da shakata a gidan kowa sai zagin su yakeyi tanaji tana gani babu yadda zatayi akai sai hakkuri.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BAKI GA ALLAH YA SAKA MUNA AKANKI YAR UWA,,,


Ya dawo acikin shirin shi ina kwance Iyya tana kokarin fita da ta gan shi yace, Iyya ni zan tafi don Allah mutumiyar ki a kulla da ita sosai naso ace ina garin don na bata kullawa sai dai hakkan baisamu ba.
Nasan ban da matsalar hakan don ke da maji kuna kusa da ita bana son tana wanan rashin cin abincin da batayi yana matukar damu na sosai ko ba dadi abata koda kadan ne please.
Iyya tace uban dakina kada ka damu tsakani da Allah nake zaune tare da ku zanyi wa Fatima duk abinda kasan zan iya yiwa yar cikina shi insha Allahu.
Ya ciro kudi masu yawa yabata yace ga wanan ki rike a hannun ki ku dinga lalura dashi a nan din.
Tai mai godiya ta fita daga dakin ta barmu mu biyu dagani sai shi a dakin.
Isowa yayi inda nake kwance yana cewa na,shirya zamu tafi yanzu bakin gadon da nake kwance ya zauna ya kamo hannuwa na.
Yana fadin Fatima don Allah ki kula da kanki ki tausayawa abinda ke a jikin ki please.
Idan baki ci abinci ba yaya zaki samu kuzari har baby na ya samu shima please ki tausaya min ko ba dadi ki dan dinga cin yan abubuwan gina jiki don kuzarin ku.
Kune rayuwana Fatima kune zan kalla nayi farinciki don kune jindadin farin cikina.
Nasan bakya jin dadi amma ki kara tausayawa kanku please badon ni ba for the sake of our baby please.
Idanuwa na na dago sun ciko da hawaye nace yaya ina son ci amma ko naci din fitina yake zama min nai ta amai sai na fitar da abinda naci nake dan samu lafiya.
Ya dora kanshi saman goshina ta yadda muke iya shakan nufashin junan mu.
Yace sorry my baby nasan kina wahala wallahi dada halin karban ciwon nan a hannuki da na karba maki kin huta ke ma.
Hawayen da nake dannewa ne suka silalo daga idanuwana a hankali.
Yasa hannu ya goge min yace ko bakya son na tafine Fatima?
Sai na barsu mummy da sagir su tafi su kadai na zauna nai jinyanki da kaina.
Nace cikin kada kai tare da bude bakina da kyat nace no yaya Baba yafi bukatan ka a hanlin yanzu.
Tausayin ka kawai nake jin irin yadda rayuwa yazo muna cikin wanan dan kankanin lokaci haka komai ya jagule a lokaci daya.
Yace cikin dan murmushi tare da rugomoni zuwa jikin shi da kyau yace duk bawa yana da tashi kalar jerabawan a kullun don haka wanan wani sabon gwajin Imanin bawa ne yazo muna.
Ki kula da rayuwan ki don likita ta fada min kina matukar bukatan hutu sosai saboda kalar mahaifan ki ba mai daukan wahala bace haka.
Nace insha Allahu yaya zanyi yadda kace Allah ya tsare min kai a duk inda kace yace amin cikin dadin rai.
Yace Fatima wanan baby ya wahal da maman shi da yawa udan yafito ashe bazan yi punished din shi ba kuwa?
Dariya nayi dama shi yake son ji gare ni kafin ya tafi nace ni har cewa nake a cire min shi na huta wallahi.
Sai naga ya sake ni ya lame kwance saman gado yana fitar da numfashi tare da furzo iska daga bakin shi.
Yace Fatima ko bakya son nawa ne da gaske da har kika iya furta wanan kalman haka a gabana ?
Nace haba yaya kaima ai kasan ina son ka wahala dai ne yai min yawa wallahi yaya.
Yace to kiyi hakkuri please ki haife min shi nai maki alkawari baku kyakyawan kulla dake da ko maynene a tare da ke insha Allahu nace naji yaya.
Kudi ya ciro masu yawa yabani yace karbi wanan ki boye a gurin ki don ban san abinda baya zai yi ba.
Nace ni may zan saye anan wanda akace zai kwana biyu a cikin asibiti yace karbi dai ki rike a hannun ki in case zai maki amfani.
Ya rugomayni na dan tsawo lokaci ya mike yana cewa zamu tafi nima kokari saukowa nake daga saman gadon da nake kwance.
Ina kuma zaki tafi na dan marairaice nace ina son ganin tafiyan baba ne yaya.
Ido ya kura min kamar zaiyi magana sai kuma ya mika min hannun shi alaman nazo mu tafi tare muka fito bayan na saka dan silifas a kafana tare da saka hijjib dina.
Tare muka fito daga dakin yana rike da hannuna nan naga kowa na gidan mu yana gurin maza da mata manya da yara.
Idanuwan su akaina har muka karaso suna gaisawa dani bai saki hannu na ba har lokacin muna tare muka shiga inda Baba yake kwance harkaf an shirya shi kamar ace ya tashi ya tashi.
Har bakin gadon muka karasa yaya yadan duka daidai kan shi yace Baba ga Fatima tazo tai maka sallama.
Yadan jawonin zuwa kusa da Baba nace Baba Allah ya tsare hanya Allah ya baka lafiya ka dawo cikin mu lafiya.
Ikon Allah sai kawai baba ya dan bude idanuwan shi a hankali wanda sunce ya kwana biyu bai bude idon shi ba.
Yana bin mu da kallo a hankali na kara cewa Baba Allah ya baka lafiya ka dawo ka dauki jikan ka da hannun ka.
Sai ya dan sake murmushi a hankali wanan yasa kowa dake gurin jin dadi sosai har likitan dake tsaye yana gyara shi yace gaskiya da za,a samu irin wanan da yake so a tare dashi ko yaushe za,a samu improvement sosai ga lafiyan shi.
Nace muyi addua kafin a wuce nan na gyara na dinga kwararo mashi adduoin samun lafiya ana karbawa da Ameen.
Muna tsaye aka fito dashi aka saka shi a ambulance din asibiti zuwa airport.
Sai da aka rufe motar yaya ya dawo har inda nake bai damu da,wai mutane suna gurin ba yai hugging dina a jikin shi yana dan bubuga min baya kamar yana lalashi na tace be strong Fatima Allah ya baku lafiya.
Ya juya ya tafi kowa sai kuka yakeyi don yadda aka fita da baba ko mutum baida Imani sai ya tausaya mashi.
Da gata na kwato bawa daga hannun Alah da gata ya kwato Baba cikin wanan halin rayuwan da yake ciki a wanan lokacin.
Gaba daya diyan shi yan uwanshi abokan arziki jikoki saraikai duk suna gurin tsaye cikin tashin hankali a lokacin.
Rahama tana gurin da iyayyenta a gaban idon ta komai yafaru tana kallo.
Wani kishi ya rufe mata idon ta don ganin yadda yaya yake wani jiji dani kamar diyar wata da wani.
Tace sai tayi magani na sai ta mayar da wanan son tsakanin mu ya koma kiyayya watarana a cikin ranta take zancen ta.
Uwarta ma kishine ya rufe mata ido suna hanya take magana cewa jifa yadda yaron nan yake wani jiji da yarinyar nan.
Ai don dai baki tare dashi ne idan kina gidan wane ita yar talkawan tsiya kawai.
Baban yace ai barshi da gaiyya zan daura masu aure inga yadda zai yi da ita idan nakai mashi ita gidan shi.
Muna kallo suka fice daga asibitin suka barmu nan aka fara watsewa daya bayan daya ana mai fatan samun lafiya.
Na kalli duk taron nan watsewa zasuyi su tafi su barni a cikin asibitin ni da Iyya kawai .
Sai naji wasu hawaye sun zubo min Nafisa ta kama min hannu tace kada ki damu matar yayana Allah na tare da ke.
Tare da ita muka koma dakin da nake bayan nayi sallama da mutane mama da maryam da mijinta ne suka biyo ni zuwa dakin.
Sun dan jima a gurin mu sukace zasu tafi sai dai da safe idan sun dawo kuma insha Allahu.
Nafisa tace ita yau a gurina zata zauna mama ta zaci wasa takeyi sai da tace Allah maji yau a nan gurin Fatima zan kwana na debe mata kewan yayana.
Nan mama ta tafi tabarta sai dai mama bataso haka ba don tasan halin Nafisa na watsewa.
Amma batai komai ba wallahi sai hiran da mukeyi akan matsalan baba kawai da zamu kwanta ta hau dogon kujera iya tasa bargo a kasa ta kwanta sai safe.
Washe gari da muka tashi Nafisa bata tsaya an kawo abin karyawa ba ta wuce gida.

****** ********* ******
Sun isa Germany da baba lafiya an kuma duba lafiyan shi har ana samun sauki sosai suna isa yaya yake kiran layina tare da tambayana karfin jikina.
Ganin an wuce da baba yasa yaya Ahmed fitowa daga maboyar shi ya na komai nashi normal.
Sun buga suna fadawa sadauki fitowan shi yace abar case din har ya dawo don kotu ta fadawa dan masani cewa bai da hujjan tayar da maigida a gidsn shi sai ya samu lafiya an yi sharia.
Sadauki baya son ayi maganan kan zancen sayar da gidan nasu na gado da akayi duk da zancen ya karade gari anji labarin abinda Ahmed yayi wa mahaifin shi.
Mama Asiya hankalinta yai matukar tashi yadda taga kowa gidan ya tsane ta ita da danta.
Don laifin Ahmed ya shafe laifin duk wani laifin yaron dake gidan gashi Alhaji bai ko yarda ya gaisa da ita a waya.
Ko yana waya akace ga mama zata gaida dashi zai kashe wayan yaki dauka.
Balle ga mummy kusa abin nema ya samu dama ba shiri a tsakanin ta dasu ko kadan.
Duk da baba yana asibiti cikin halin lahulai amma idan mutum ya shiga gidan zai ga kamar hankalin su a kwance yake.
Irin yadda suke busha shan su agidan ba wani damuwa a tare dasu a lokacin.
Ga wani shakuwa da yashiga tsakani na da Nafisa yanzu don ko wani lokaci tana gurina a asibiti muna tare.
Wani lokaci anan kawayen ta ke samun ta nan zasu wuni suna debe min kewa.
Banda matsala dasu wani lokaci idan suna hiran busha shan su a gabana nakan ce haba anty kamata yayi ace cikin maneman ku ku cafke daya ku aura.
Nura kance ke kaunata nifa mijin ki nake so na aura nakance aiko danaji dadi anty idan har zakiyi aure ki zauna ba sai mu zauna lafiya ba.
Kin sanni na san ki kinga ba fada a tsakanin mu sai so da kauna mu rike mijin mu tsakani da Allah.
Nuriya wallahi idan kina wanan maganan zamu sami sabani sosai wallahi Raiha ke fada mata haka duk lokacin da tai irin wanan magana.
Nafisa kuma takance may zaiyi da honko haka may ya rage jikin ki baya cus kin sha burga kamar rijiyar kwakwara da ke.
Nace ba komai zamu gyara ko anty Nura ai mace mai gyara bata baci ko ?
Raiha takan sha toka tace please abar wanan zancen bata so su ko watace sukaji mijina yana nema sai inda karfin su ya kare akai.
Tace Fatima kin muna fa wata matar aure ce zata sake jiki damu haka abinda ake gwada muna kyama keko kin muna rikon tsakani da Allah kamar wasu yan uwan ki naji fa kika mayar damu.
Yan uwan mu ma naji yanzun haka basu hurda damu don kaaai wanan halin da muka tsunci kan mu a ciki.
Mutane suna manta cewa ko su Allah yana iya jarabtan su a kan haka?
Duk lokacin da ya tashi yin ikon shi a kan mutum na tabbatar da yan gulma suna fadawa mijin ki kina hurda damu haka amma sanin koke wacece yasa bai damu ba duk dai yana halarci ne akan yar uwar shi dake cikin mu amma duk da haka Fatima kunyi muna wallahi.
Nan zamu wuni da su ai ta shiririta suna matukar bani tausayi ina yi ina masu gyara.
Yau ma sunzo mun jima muna hira dasu sosai har barci ya kwashe ni na barsu da Iyya suna hira sun sayo nama mai zafi da drinks sun baje suna ci.
Amira ne tashigo dakin da nake kwance wanda yanzu ya zama min dakina na komai.
Suna gaida ita amma,sai wani basar dasu takeyi sukaci gaba da harkan su kawai.
Bakin gadon da nake kwance ta karaso tana tayar dani daga barcin.
Iya da Raiha ke cewa haba kin san tana son hutu barta mana tai barcin ta kada ki tayar da ita.
Tace waye zai hanani tayar da ita Rabin dan musa ko wa wai takai hannu ta tabani na bude idanuwana.
Ina kallon ta nace anty kin shigo ne ashe tace a wulakance may wa yan nan sukeyi a nan ne haka ta nuna su a wulakance.
Sai sha,anin su sukeyi kamar basu san da ita ba afurin ko tanayi ma ba wanda ya kulata.
Na dan kakaro murmushi a fuskana nace anty kawayen anty Nafisa ne fa.
Tace and so what Nafisan may can kuma wai kinga bani son na kara ganin su a tare da ke kinji na ffada maki ko?
Tace sai dai ban sani ba ko kema harkan taku dayane dasu don banza bai kai zomo kasuwa.
Wasu hawaye suka zubo min nace haba anty cin fuska baida kyau haka wani abu mukeyi banda mutunci da zumunci kawai.
Tai mun wani kallon wulakanci tace zaki gane wallahi Nafisa tace Amira wallahi yadda kike da Fatima nima haka nake da ita don


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login