Showing 195001 words to 198000 words out of 373688 words

Chapter 66 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

abinda ya bashi din.
Kudi masu yawa ya ba mutumin sai yai dariya yace ba haka nake ba ni dari biyar kawai zaku bani ko shi kada kuce naki karba ne da ban karba ba wallahi.
Sunyi mamaki sosai muka kama hanya sai sokoto koda zamu dawo naita kakarin amai saidai da yake cikina ba komai sai kumfa kawai nake zubowa.
Bashar dasu mama suna ta faman yi min sannu amma,shi ko kallo ban ishe shi ba.
Da la,asar muka iso gida tun lokacin kowa ya fara abinda aka bashi yayi daga gurin bawan Allah.
Don har bashar saida ya anso nashi shima don mutimin shi da kan shi ya bashi taimakon.
Tun dawiwan mu nikan ina dunkule saman dogon kujera harda barcin wahala saida nayi.
Anty maryam ce ta dafo min liptop da lemun tsami na dan sha shine na dan ji dama sosai.
Ya shigo falon yayi wanka ya,sauya kayan jikin shi a lokacin yasa wando da rigan na maza mai dogon hannu.
Gani a kwance na dunkule yasa ya dan tsura min ido sai yaji na bashi tausayi sosai.
Yace ke may ke damun kine yanzu kuma?
A sanyaye nace cikin bata fuska kaina ke min ciwo.
Bari in nafita sai a sayo maki magani kisha.
Nace nagode.
Wanan gidiyan da nakan yi mai idan yai min alheri yakan ji matukar dadi a,ran shi don shi mutum ne mai son yaji ana godiya gare shi.
Sosai ya mayar da hankali shi ga maganin shi da mutumin ya bashi don yai matukar yarda da zancen mutumin ba din komai ba,rashin amsan kudin su da mutumin baiyi ba.
Ya dawo ya,sayo min magani harda na amai da kuma drinks mai sanyi na kwali.
Ina kwance na na dunkule a saman kujera su na kallo ni kuma gani kwance a dunkule sai dai ba barci nakeyi ba idona biyu.
Muryan shi naji yana tambayan su ita wanan barcin takeyi har yanzun ne ko jikin ne ke damun ta?
Maryam tace tace kanta kawai ke ciwo yanzu yace ke tashi ga magani ki sha ko zai lafa maki.
A hankali na mike zaune daga kwancen da nake sai dai still ina dunkule ga hijjab ga kuna blanket dana yafa ajikina.
Na karba tare da bare maganin na kai abakina saida na dago kai naga ya tsura min ido ashe ni yake kallo daga inda yake zaune.
Da sauri na dukar da kaina kasa bban tsaya shan drinks din ba yake cewa bazaki sha juice din ba ne?
Nace a,a ban iya sha yanzu sai nakai kwance daga inda na tashi yamike zai bar falon yana cewa idan bai bari ba sai akaiki asibiti ke nan.
Ya fice daga dakin na lumshe idanuwana tare da komawa barci a lokaci guda.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA BAMU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAR MU NA AKAN KI,,,,



Tun kawo laife na yaya sadauki ya kara tsananta min a gidan su, dan abu kadan zanyi ya dinga min fada cikin hasala da bacin rai.
Wanda shi kanshi bai san dalili yi min haka ba haka,kawai yake jin haushin yarinyar a ranshi.
Duk da maji tana mashi fadan haka amma ya kasa rangwanta kiyayyan da yake ji nawa a ranshi.
Idan yana gida ban fitowa falo sai naji ya fita daga gidan zan fito falo don nima haushin shi nake ji yanzu don a matsayin mugu macuci nake ganin shi.
Nasan kuma don saka mai idon da nakeyi ne abaya shine yasa yake jin takaicina haka.
Maji sai shirin bukina dake kara matsowa takeyi a hankali, irin su kayan kitchen da wasu uan abubuwa su take sai min.
Kabir yace idan anyi aure a sokoto zan zauna a gidan shi na garin sai idan anyi hutu zan diga zuwa gurin su Abuja.
Maji yakira ya fada mata tsarin da yayi akaina da ta tambaye shi kan al,amarin karatuna da nakeyi.
Sadauki ya shigo ya samu mama tana wayan da Kabir yana jin duk abinda suke fadi a karshe Kabir din ke cewa mama ko tsarin bai maki ba haka?
Maji tace gaskiya naji dadin hakan Allah ya albarkaci rayuwan auren ku, ya amsa cikin jin dadi da Amin mama.
Mama tace Kabir don Allah ka rike min Fatima amana don Fatima yarinyace dake bukatan kulawa yace insha Allahu mama kada kiji komai nima nasan da hakan.
Yana zaune ya fahinci da wa mama take waya ya lumshe idanuwan shi jin hiran nasu yake kamar a fili Kabir yake ya shake shi.
Sai tsuki yayi lokacin suna sallama zata kashe wayan yace tsohon banza kawai.
Kaidawa kuma kake tsuki anyi wani abin ne ko may?
Yace cikin daure fuska kawai dai nayi ne don wanan shirmay danaji anayi.
Shi waye da zai dinga yiwa mutane barazana kamar wani attajiri can.
A,a ikon Allah waikai sadauki ina ruwanka da zancen nan ne?
Ina da ka mayar da kanka abin kwarai agurin kane za,a zo neman auren yaran nan.
Yace wani maji da ban bashi ba kawai mutum ya tsufa amma yana halin yara .
Idan aure yake so bai zuwa ya samu bazawara su shirya sai yafake zai bata yar mutane.
Ya juya inda nake zaune raina yabaci don abinda yake min yafara isata, yace jita don Allah daga kawai ance mutumi a abuja yake duk kin wani rude a kan shi don kawai kije abuja.
Baki tsaya kin tsarawa rayuwan ki abinda zai fishekiba mutum da iyali haka ke karama dake may zaki gane a gurin shi inba wahala ba.
Kai dakata ya isa haka na,rasa gane dalilin dayasa kake wanan abin haka
Yadago ya kalli uwar yace may nakeyi maji iyaka dai ina fadin gaskiyane ni kawai.
Duk abinda na hango mata kun kasa hangen shi sai faman rawan kai takeyi ita zatayi aure wawiya kawai doluwa.
A,a wai sadauki kana da hankali kuwa da may wanan abin yai kama hakane wai?
Mikewa nayi fuuu, nabar falon cikin fushi na shige ciki abina don ban iya tsayawa sauraren wanan shirmay na shi.
Tun ranan idan yaya sadauki ya shigo falon duk hiran da ake haka zan mike tsam na shige daki abina.
Ranan muna tahiran mu cikin dariya har maman tamu tana saka muna baki a hiran mu don hiran wasu samari da suka zo wai suna son maryam muke yi muna dariya.
Ya shigowa suna mashi ina wuni da jan shi da hira yana batun zama namikw tsaye tsam daga inda nake zaune, ina cewa.
Zan shiga na kwanta maryam tace wazai kwanta yanzu ke da baki barci koda rana shine yanzu da yamman nan zakice wai zaki kwanta.
Ya dago lumsarsun idanuwan shi masu nuna a gajiye yake a lokacin don tun safe yafita daga gida .
Ya dora su a kaina gaba daya yaga na canza mashi na koma wata fresh sosai dani don nima ban san may mama take yawan bamu ba muna ci muna,sha na gyara jiki kawai .
Ko kiftawa bayayi don mamakin sauyawa na a lokaci guda da yaga nayi mashi a lokaci guda.
Mama taga yadda yake kallona sai abin ya bata mamaki kwarai da gaske amma sai ta dauka wani sherin yake son fadi akaina kuma.
Don haka tai shiru tana sauraren taji abinda zai fadi a lokacin tai mashi tsiya.
Maryam dai tasan yar tsama muke duk kwanakin nan ta dai dubeni saboda ta san ba,kwanciyan zanyi ba ganin yaya ne kawai yasani barin falon nashige tana ce min atashi lafiya ko?
Nashige batare da na,kara,waiga inda yake ba ballw yace ga abinda nai mashi kuma.
A bangaren sadauki kuwa, fuska ya kara,daurewa batare da ya kara bi ta kaina ba don yasan mama tana jiran shi ne.
Maryam daga inda take tai mashi kuri da ido tana dariya cikin kyata tace ban san wanan fadan na yaya da Bintu ba wallahi.
Bai tanka mata ba sai tsukin da yaja ya dan dafe kan shi yana fadin rabu da,wawiyan banza kawai gaskiya ne bata so a fada mata.
Daga gurin da maji take cikin takaici tace gaskiyan may kada tai auren ko may ?
Yace ni fadan gaskiya nake mata saurin may take da,bazata iya tsayawa ta karasa makatantar taba ne wai, duk tsoho ya, hure mata kunne bata jin kiran yanzu sai
When it's too late to her zata gane kuren ta ai.
Allah dai ya tabbatar muna da abinda yafi zama alheri a gare ta.
Ina shiga daki kamar jira kabir yakw na shiga dakin sai ga kiran wayan shi ya shigo min.
Mama ta kwalla min kira wai nazo za ai program din da nake so wasan kwaikwayo a NTA sokoto wanda nake so ina kallo ina dariya don shirin irin namu ne na mutanen kauye.
Hakan bai hanani yin wayana ba don can na manne gefe guda yadda,ba mai jin abida nake fadi.
Kallo daya zakai min ka fahinci cewa ina cikin nishadi da wayan da nakeyi ga kuma kallon film din da nakeyi a tv duk a lokaci daya.
Muryan kabir ce ta ratso dodon kunne na yana cewa Fatima nayi rashin ki kwana biyu aiki ya hana nazo na gane ki.
Nayi murmushi tare da lunshe idanuwa na na gyara zama da kyau.
Ban bashi amsa ba sai yar murmushin da nayi har yana jiyo ni a,wayan a lokacin .
Ya naji kina murmushi ko baki yarda na damu da nazo na ganki bane wai?
Na koma yin murmushi mai hade da sautin dariya wanda ya jawo hankalin kowa a kaina a lokacin.
Nace may zai hana na yarda duk da dai nasan akwai wasu a,tare da kai ba,wai wani damuwa zakayi sosai hakana ba ai.
Yace kowa daga cikin ku ina bashi hakkin shi ai nace ai nasan da hakan, yace da kyau da kika fahince ni.
Yace wai kin san wani abu kuwa nace a,a cikin dan girgiza kaina kamar yana gani na a fili.
Nace sai ka fada dai,
Yace wai ko Fatima kin san yadda nake jinki a cikin raina kuwa, ?
Wallahi da ina da iko ko kuda bazan yarda ya sauka a kanki ba.
Don ina ji a jikina ke wani abune da,Allah ya jefo min a cikin rayuwana mai muhinmanci a gareni.
Murmurshi nake irin mai kyalkyatawan nan nace kai amma kuwa nikan nayi sa,a,a,rayuwana wallahi.
Insha Allahu zanci gaba da kullan maka da kaina a duk inda nake .
Nace ni wallahi zancen kama har yasa na manta ban tabayeka lafiyan anty na ba da yara.
Yace duk suna nan lafiya yanzu tare muke da uwargida ta dan shiga shago tayi sayayyane.
A rude nace wai har na zaci ai a gaban ta kake waya dani haka wallahi.
Yace aiko a gaban ta sai nayi don ba ta damuwa tama fini matsuwa kizo gidan ai yanzu.
Na saki wata yar siririyar dariya nace kai ka taba ganin kishi har tafi ango damun akawo mata kishiya a duniya.
Yace baki san halin ta bane shiyasa amma ni nasan zanji dadin zaman ku a tare sosai wallahi.
Nace ni dai ka rufa min asiri kada dayar matarka tani tace zamu hade mata kai don muna shiya daya da ita.
Yace ai itama tasan cewa Haulatu na waya dake tai fada harta gaji tunda babu yadda zatayi.
Nace ni nasan dama idan ta sani sai anyi rikici don bata da dama,wallahi gurin kishi.
Maryam tace kai kai wanan matar dai tun ba,a shiga ba na hango ita ce matsalar ku ke da Kabir .
Dariya na kama tare da kashe ina cewa kai anty maryam watau kina jin hiran mu ashe?
Tace duk abinda kuke fadi inajin ku ai in ya damu ba sai yazo ya zauna ba yai ta kore maki kudan da baison yasauka a kanki.
Ya suke da hiran mu yakai geji yakawo iya wuya sai yaga fita dakin yafi mashi jin takaici kawai.
Ya mike yanace maji zan fita sai na dawo tace mai a dawo lafiya tare da ci gaba da kallon ta.
Yana fita Amira tace ke Bintu watarana sai yaya ya make bakin nan naki akan wanan wayan da baiso.
Mutum da mijin shi zai make ta idan yaji takaici yaje ya samo tashi matar mana shima inji maji takeba Amirah amsa.

Bai dauki lokaci ba sosai yakoma tafiyan shi don yanzu bai zama a gida shi sosai ga,wasan kwallo ga kuma business din daya fara gadan gadan na sayar da motoci da mashin mashin,
Haka yasa baida lokacin zama a gari yana fita business din shi da neman kudin shi.
Cikin dan lokaci guda sai ga sunan sadauki ya daga sosai a gari.
Abinda su mama suke gudun dai ya faru Allah ya nufi sai ya faru din don suna gani kuma suna jin yadda Allah yai ikon shi akan abinda suka so kada ya faru da dan kishiyan su.
Mama Asiya ce suna zaune suna hira take cewa, wallahi yaya wanan yoron shigen yaro ne kidiba fa,ba yan mu ba yanzu ko uban shi ya tsushe nisa ba kusa ba .
Umma tace ni wallahi ba inda na fara sanin haka zai iya faruwa damu sai wani rana da natafi dasu gurin buki.
Wata mata irin matan nan masu ido a bude take ce wa daganin na shigo da yaran gidan lokacin suna kananan su.
Matar tace wai wai wai wake da wanan hamshakin yaron haka?
Wai akwai magana nan gaba a gurin nan yaro karami haka da,wanan baiwa irin haka.
Don Allah ku daina fita dashi don gudin idon makiya don wallahi wanan da kuke gani ba karamin mutum bane gurin nan aje.
Umma tace na dauka fa da yaron nan take (Imirana) sai naga ta kama hannun Sadauki kawai tana wani zuba mashi kirari har da dukawan ta.
Tace a lokacin na dauka ko shirmay su ne na yan bori ko neman kudi sai kuma nakarajin shi a gurin maigadin ma,aikatan mu ranan shi ma ya kawo min sako gida sai ga sadauki yafito naga yana kada kai yana fadi cabdi babban mutum Allah ya raya muna kai watarana,akwai magana gidan nan.
Wallahi Asiya tun ranan nasan in bamuyi hankali ba diyan mu na zama shara a gidan nan muna ji muna gani.
Hmmm ashe bani kadai nasan da haka ba tace ni wallahi a gurin baffa malami na fara jin haka.
Ranan da,suka rakani na gayar dashi duk cikin su ba,wanda ya cewa yazo inda yake zaune saman buzun shi wai sai sadauki.
Naji yana cewa manyan gobe Allah ya taya riko Asiya ki rike yaron nan don watarana shine gatan ku ke da yaran nan.
Wallahi baki yadda wani mashe ya sokeni ba sai da na dawo gida abin ya tsaya min arai sosai wallahi.
Nasan baffa kamar mai rafanne yake da,wuya yai magana ya zama karya wallahi.
Kinga wanan makiran nasan itama tasan komai shiyasa take wani wayayya,tana nuna ita tana kaunan shi fiye da kowa.
Shekaran jiya Adamu ke ce min wai motar da yasayo yana shiga yanzu takai miliyan goma.
Ke don Allah dai ki bari tace wallahi yace haka yaji ana fadi a gari wai ba kowa kedashi ba yanzu a kasar nan.
Hmmm lalai Hawau takai makiran mace amma baki ganin wani alaman facakan kudi atare da ita kuma kin dai san yana bata dai.
,A,a ba gashi yaron nan yana fada min ba,wai shi yayowa uban odan kayan da aka,shigo masu dashi wanan wata yace kuma kayan sun samu shiga sosai.
Ai harda noman da Alhaji keyi yanzu shine mai bada kudi anayi don dai ranan naji suna,waya dashi.
Dan banzan yaro maikama da dutsen tsakar ruwa , Asiya karkare mata da cewa, wai bai san tudu ana rana ba.
Yanzu don Allah wazaice dan banza zai iya irin wanan dabara duk kwaya ta halaka shege kullun gashi a bushe kaman kayan rani.
Sai suka sa dariyan keta har suna tafawa tace aiko yanzu in sun san wata ai basu san wata ba ko?
Da yammaci, ranan laraba sadauki ya shirya yafita zuwa masana,antar shi don yaga halin da,su Bashar ke ciki da sana,an tasu.
Ranan shirin musulunci yayi wanda da,wuya kagan shi saye da tufafi irin na,al,adan hausawa.
Shadda ce gezenah mai ruwan kasa,sai maiko takeyi, sai dai dinkin gajeren hannu ce,anyi ma,rigar aiki a gaba mai kyau da daukan ido.
Sai yar hular da ya dora akan shi mai tsada kalar kayan jikin shi,takalman shi bakake sai shining sukeyi sunci polish.
Ga kanshi na tashi kamar duk kwalban ya juye a jikin shi a lokaci guda.
Gurin maji yafara shigo ya sanar da ita zai fita don har yanzu kudi bai hana shi yiwa iyayyen shi biyayya ba.
Kuma baisa yace don yayi gina yabar gidan mahaifan shi ba yanan ciki tare dasu saidai ya gyara gurin shi sosai harda na yan uwan shi.
Ina zaune antu maryam tana min kitso sai faman masifa take min ita gashina yai yawa wahala kawai nake bata.
Azaune nake ba dama na gudu daga falon gashi fuskana yana facing din inda yake tsaye yana dauko wayan shi dake ruri daga Aljihun shi.
Yace hello Bashar yaya akayine ?
Yanzu nake son fitowa tun dazu ina daki ina barci kasan wasan last week yabamu jiki


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login