Showing 234001 words to 237000 words out of 373688 words
Chapter 79 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
dama nan kuma na shiga gyara nafito da tulin shara daga dakin don irin gyaran da ake mai na sama sama ba,a kwakwalo komai da kyau.
Dakin sai gashi yafito tsab dashi kamar dakin mace nace mata may za,a girka ne da rana
Tai murmushi tace ai bamu girki rana sai dai da yamma idan ya dan samo muna sai mu girka jiya ma da kikazo ai sa,a ki kayi yasayo muna dawa shine nan nai muna tuwon shi har kika samu.
Haushi ne ko tausayin ta zai kamani na rasa may mama ta zaunayi gidan wanan mashayin har lokacin nan.
Yanzu gashi har sun kai ga tara yara har shidda dashi babu zancen fita gare ta kuma ke nan.
Bance mata komai ba nafita na kira musa ya sayo muna rogo da zogala a bakin yar kasuwan su.
Nai zaune na gyara shi kowa yaci ya koshi muka sha ruwa abin mu nayi hakane don mu kyale mugun mijin ta da baida katabus ga iyalin shi ko yaushe.
Dan na lura yanzun idan nazo komai bai saye in an tabaye shi sai yace a tambayi Bintu ko tana da canji a sayo.
Yana ko dawowa yake tambayan ba,a gika komai bane a gidan mamana tace ka kawo abin girki ne halan ?
Yace baga Bintu tazo ba bata sayo bane a girka din ?
Naga idan tazo takan dan yo muna dabara yanzun aci shiyasa yanzun nake farin cikin zuwan ta furin mu ai don nasan idan tazo hankali na a kwance yake da kayan bani banin ki.
Tace to bata sayo ba yau don haka sai ka canza tunanen ka kafita kasamo muna.
Yace kin tambaye tane tace maki babu a gun ta da zaki ce na fita in na fita ina zan samo tunda ba sana,a nakeyi ba ni.
Sai kawai naji yana kirana ke Bintu Bintu fa na amsa daga dakin da nake nace na,am Baba na fito.
Yace cewa nayi baki zo muna da komai bane wanan tafiyan don naji shiru har yanzu bakice muna komai ba?
Nace ban zo da shi ba a takaice.
Kallona yake don jin yadda na bashi amsa duk nima ban so bashi amsa a haka ba don ko banza mijin mahaifiya na ne shi.
Ina fafin haka na juya ban tsaya ba balle naji may zai kara fadi kuma tunda ba ta ido ne dashi ba.
Yanzun kai bakaji kunyan tambayan ta wanan magana ba haka wani sana,a takeyi ne a can kokuwa itama ba karshin wasu take bane wai ?
Yace na dai fahinci abin akwai rainin hankali watay kin hada baki da uwar ki kada ku taimaka ko to oho akan ku zai kare ai munafukai kawai.
Idan naga abin rainin wayo ne sai yarinya ta koma gidan uban ta wallahi tunda nan ba gidan su bane ?
Zance ke nan kake fadi ai matsawan ina gidan nan dole ne yarinyar nan ta zauna a gidan nan ita ma.
Yafita yana fadin oya shege ka fasa ni daku kuwa a gidan nan mama tace ai ni wallahi dana huta ta wanan wahalan.
Ni dai ina jin su nace mashayin banza kawai a raina a haka zaka kare har girma yazo maka baka bar tabara ba har yanzu.
Muryan kani na musa dake zaune ta waje naji yana fadin ni wallahi mama da ma kin gudu din mu huta da halin baba mu koma can birni gurin yaya Bintu muma mu huta kawai.
Daga daki nace kai musa baka da hankali ne ina ruwan ka da saka baki ga maganan man ya ne wai ?
Da yamma muka shirya nace su rakani unguwa duk da ban fadi inda zan tafi ba sai gidan su marigayi Kabir naje gaida mahaifiyan shi.
Matan bata gane mu ba sai da muka shiga har dakin ta muka gaisa da ita, sai dan shiru can tace ban ko gane ki ba.
Nai dan murmushi nace Fatima ce diyar Hausin dan Amo, tace Allah sarki Fatima kuwa haka akayi gaskiya ban gane ki ba wallahi.
Nan ta,rasa inda zata sani don murnan gani na tace yaushe kika zo garin namu nace mata jiya nazo Inna.
Nan muka zauna muka kara gaisuwa dasu da sauran matan gidan suna kara jajanta min mutuwan Kabir din.
Nan suke fada min iyalin shi yanzu suna sokoto zaune don karatun yaran shi daya bari.
Nace Allah sarki aiko ban sani ba dana shiga inda suke tace min dama ai a uguwar GRA yake da gida an raba gado anba kowa nashi shind ita Saude da yaran ta suka samu gidan .
Nan dai nan dan zauna har zuwa dan wani lokaci nai mata sallama muka bargida bamu ratse ko ina ba sai gida.
Mun shigo bamu dade ba sai ga yaron gidan ya biyo mu da sakon wai inji mahaifiyan su.
Ana wata ga wata sai ga wani dan kanin Kabir da suke uwa daya dashi ya aiko wai yana so na da aure yana son ya maye gurbin yayan shi da ni.
****** ********* ******
An wuni an kwana har dare duk shigowan da yakeyi a gidan baiga Bintu ba a ran shi yake tambayan wanan ko lafiya take ne ban gan ta ba duk kwanakin nan ?.
Yana son ya tambaya sai daibai son raini ko tuhuman wani abu ga tambayan da zaiyi na ina nake kwana biyu baya gani na.
Da yamma ya shigo gidan baiko shiga part, din shi ya wuto cikin gida direct nan ya zube a falon mahaifiyan shi.
Wayan shi ya jawo daga aljihun shi, bayan sun gaisa dasu rasa may ke mai dadi shine ya ciro waya.
Ya fara yin game da ita sukosai hiran su suke suna kallo hankalin su a kwance abin su sabanin shi dake a cikin damuwa.
Can yace maryam
Ta amsa da na,am yayan mu .
Yace wai ina wanan yarinyar take ne kwana biyu bana ganin ta ?
Tace yaya sadauki Fatima kake nufi ?
Yace ita din mana.
Tace ta tafi kauyen su yau kwana uku ke nan taje gun mahaifan ta ne wai zata kwana biyu a can.
Wani irin faduwan gaba yaji a lokaci guda, yace a ran shi kodai saboda abinda ya faru ne a tsakanin mu ta bar gidan nan don ni.
Duk sanyin AC dana gari da akeyi bai hana ahi feso wani irin zufa ba a lokaci guda.
Take kamannin shi ya sauya a cikin, lokaci guda, idanuwan shi sun sauya kala zuwa ja a lokaci guda.
Tankar wanda aka watsa wa barkono yace a kasale yaushe tace zata dawo ne wai ?
Tace zata kwana biyu a can don haka ba rana ke nan sai dai idan mun ganta kawai.
Yace ba kun kusa komawa school ba shine zatai tafiya taje ta zauna har wani lokaci.
Maryam tace ai muna da sauran lokaci ga hutun mu yaya kila sai hutun ya kare zata dawo ai?
Maryam tace lafiya kuwa yaya kake tambayan ta cikin son kara tuhuman ta akan shi.
Yace No babu komai dama zanyi bakine shine nake son ta hada min wanan abin dama yan wasu abubuwa.
Daga haka yaja tsaki ya mike tsaye yabar falon a lokacin maryam ta dan matsa gurin Amira bakin ta tab da gulma tace a hankali.
Cikin yanayi irin ta mai rada tace wai anty may kika fahin ta ga yayan mu da yake tambayan Bintu.
Tace eh nima nai mamakin jin yana tambayan Bintu don naga shi bai damu da kowa ba ai.
Hmm baki fahinci komai ba,wallahi amma ni nasan yaya yafara kamuwa da son Bintu wallahi.
Kai haba wata Bintu can wanda ke shiga duniya yana ganin mata kala kala shine zai tsaya son wata Bintu can.
A ganin ki ba tunda ke baki san so ba har yanzu kina nan zaune a na soyewa a gida baki sani ba.
Ke dai wallahi akwai ki da shirmay tsiya maryam may zaiyi da Bintu wace kullun cikin fada suke a gidan nan .
Mugun takaicin ta fa yake ji shine ke ko yar kayan soyayya kike ganin kamar shi suke yi.
Maji da tasamu suna firan tace waye wai,?
Amirah tace wai yaya sadauki take cewa wai soyayya suke da Bintu kila a boye haba may zaiyi da Bintu ga yan mata yan gayu iri iri a gari ko ina.
Eh tun da ita Fatiman ba mutum bace ko ke kin fita kama mai kyau ba da zakice hakana.
Shi damay yafita ?
Ai da ta taimakawa rayuwan shi wallahi dayayi arziki in ya aure ta.
Ita Bintu din dai maji ?
Oh baki san shi al,amarin aure ba ke nan ashe da sauran ko ke tunda baki da fahintan komai.
Ni na dade da sanin abinda yakeyi kyaleshi kawai nayi kada najawa yar mutane matsala.
Kai haba maji don Allah kubar wanan zancen mana kada ku ja wani matsala kuma yarinya na zaman zaman ta yasa ta agaba.
Kai amma dai anty Amirah nan .
Watarana kice na fada maki ai.
Ita dai Amirah jin su takeyi kawai don tasan haka ma bazai taba yuyuwa ba ai.
Wata Bintu can yar kauye kuma ba diyan kowa ba, a gari.
Sai ma taji ranta ya ba i kawai da zancen don abin haushima ya bata ita a ran ta.
Yaya sadauki na barin falon dakin shi ya shiga ya fada kan gadon shi yayi lamo saman gado.
Tan kar wanda yake barci, sai dai ba barcin yake ba yar damuwa ce da bai san dalili ba ya dami zuciyar shi kawai.
Can ya tambayi kan shi wai may yasa har yake son damun kan shi akan yar karamar yarinya hakane.
Gashi a yadda ya lura da yarinyar bata ma gama sanin komai ba na rayuwa don akwa childish a tare da ita har yanzu a rayuwan ta.
Karancin shekaru uwa uba kauyanci bata san ko inaba daga sokoto sai kauyen su kawai.
Shi dake son mace nagani nafada na gwadawa tsara shima ya faso zai tsaya ga yar kauye kuma karama haka dako twenty bata cika ba har yanzu.
Sai yaji take wata zuciya tana gargadin shi dacewa kai baba ina kai ina wanan tunanen kuma wai ?
Washegari tunda safe yashigo yana cewa shi zai tafi Abuja yanzun nan maryam tace a,a yaya wai ya zancen bakin da kace kuma zakayi har ina shirin masu abinda kace ai masu din.
Yace No maryam ki barshi kawai sun fasa zuwa din zanyi tafiya ne nima yau din nan.
Bashar yana jiran shi a kofan gida nan suka samay shi da suka rakashi, Bashar ko a,gaban kowa bai ita boye kaunan shi ga maryan yanzu sai ya baiyana shi a fili.
Don suna fito tana dauke da yar jakan tafiyan yayan ta, da ta karba ta saba a kafadan ta.
Daga cikin mota da Bashar yake zaune suna karasowa idon shi akan maryam yake cewa Madam how far?
Ita ko tai wani shake murya tace bakomai yace ya su mama tace suna lafiya.
Har sadauki ya zauna a mota Bashar sai soyewan shi yake yi hankali a kwance.
Dallah malam ja mota mu tafi da wanan bakin shirmay naka babu kunya da kake min.
Easy man, take it easy bani nakar zomon ba fa, kaga ni fa ban hanaka ba don ni ba motsoraci bane irin ka.
Wani harara yakai wa Bashar yace wallahi zaka kaini makura Allah da wanan halin rashin kunyan da ka tsiro wa mutane daga sama.
Bashar dai yaja motan shi yanawa sahiban shi bye bye, suka bar gurin suma suka juya zuwa cikin gida.
Airport ya kai shi nan ya shiga jirgi da ya tashi da sha biyun rana suka tafi Abuja, bai so buga wanan wasan ba amma halin da yake ciki yaji kawai gara ya je ya buga ball din shi ko zai samu sauki a zuciyan shi.
Duk da kwallon da ya buga bai hana shi jin abinda yake ji a zucuyar shi ba har yanzu.
Suna waya da mutanen gida amma bai, taba jin wani yai zancen yarinyar ba ko yaji an anbaci sunan ta ko a waya.
Gashi girman kai ba zai iya barin shi ya tambayi kowa labarin ta ba don sai yana ganin kamar abinda yai mata ne yake ganin bai kyautawa yarinyar ba.
Don yana gani ai kaman zaman kaunan shi yarinyar take a gareshi amma shedan ya rude shi yai mata haka.
Yace a fili, kai kai gaskiya ban kyauta why don Allah why har haka ya kasance a tsakanin mu ne wai.
Ya dan kai wa katifan da yake kwance nashi da hannun shi na hagu da karfi sosai har sai da ya dan jin zafi a hannun shi.
A haka ya kai har sati biyu acan suna da wasan da zasu buga sati mai zuwa amma ya juyo ya dawo gida haka kawai.
****** ********* ******
Ina gurin mama na zaune na sake raina ba abinda ke damuna yanzun in ba matsalan mijin ta ba da kulun a cikin tashin hankali suke a tsakanin akan ban kawo masu komai ba.
Amma nazo ina cinye mashi abincin gidan shi a banza shi gaskiya ba zai zauna da agola ba a gidan shi.
Naso na bar garin amma sai na dake na tsaya inga iya gudun shi ko zai kore ni ne ni kuma nasan yadda zan girgiza mashi auren shi.
Sai dai ya shigo yayi haukan shi ya fita babu mai tsinka mashi a cikin mu dan dama ma ita mama sukan kwasa dashi idan abin ya ishe ta.
Gidan kowa ban zuwa kullun ina gida zaune kamar wata matar aure can dani.
Ganin shi kawai sukayi da yammacin jumma,a ya diro garin nan suka gaisa mama take tambayan shi yaya akayi kuma ya dawo ba yace suna da wasa wani sati ba sai satin sama zai dawo gida.
Yace eh maji nadawo ne nai wani abu a garin kuma da akwai wasu takardu dana manta ban tafi dasu ba da zan tafi.
Yakai wani lokaci a zaune baiga giccina ba hakan yada shi sanin cewa har lokacin ban dawo ba ke nan garin.
Ya mike ya fita kaman wani mai jin kasala a lokacin, Bashar ya kira yazo idan an fito sallah su fita.
Ranan Monday maryam tafito a cikin shirin ta zata shiga makaran ta,a waye ta samay shi ya fito daga gurin exercise .
Sun gaisa yake tambayan ta ita wana har yanzu taki dawowa ba kun koma makaranta ba tace eh munyi waya da ita tace bata san ranan da zata dawo ba kila ma,
Fuska a daure yace ina ne garin su?
Tace, a yaya baka san garin su Bintu ba kai, duk zaman ta a gidan nan?
Yace don Allah malama fara bani amsan tambayana kafin kiyi min halin ku na yan kasa tukun na tambaya cikin tambaya.
Tace can rabah take nan dai tai mashi kwatancen yadda ake zuwa garin yace inda muka tafi gaisuwan wancan mutumin da tatashi aure kenan ya rasu ko tace mashi eh can ne ya amsa mata da ok good.
Zaka tafi garin ne yaya ta tambaye shi tare da kallon fuskan shi yace ban sani ba tambayan ki kawai nayi.
Sai batan kamar kwana biyu da tambayan maryam ranan da safe yace wa Bashar ya shirya zasu tafi wani dan kauye su dawo.
Sam Bashar bai kawo komai ba a ran shi nan yazi ya dauke shi shi yaja mota suka tafi.
Ban zuwa gidan kowa amma ranan haka kawai nace zan je na gaida kakanin mu kafin na tafi don saura kwana biyu na tafi.
Mun fita gida da kaman awa biyu suka shigo garin wani mai faci bakin titi suka tambaya gidan dan Amo shayi akai masu kwantacen gida.
Da farko da suka isa gidan yaso yai gardama ko banan ne gidan ba saboda ganin yadda gidan kaman ma yafi ko wani gida na uguwar lalacewa a shiyan.
Sallama suka ce ai masu da maigidan yaron da suka tura yace kai mai gidan kan yanzu ba,a samun shi gida yana can gurin moli.
Basu gane may yaro ke nufi yace yashiga yace wai bakine daga sokoto sun zo ganin Bintu.
Mamana tanajin haka tace, Bintu bata nan tafita amma ace su waye yace ace yaron hjy ne yazo tafiya da ita.
Jin haka yasa mama tace ace su shigo daga ciki ai su yan gidane nan ta tura yaron ya kirani gidan kakan nina, basu so shiga gidan ba amma dole suka shiga.
Shi dai bashar sai kallon ikon Allah yakeyi kawai don abin ba mamaki ba daure mai kai yayi.
Bin gidan yake da kallo da mamakin yadda dan adam ke rayuwa cikin wanan rubaben ginan haka da akoda yaushe yana iya rushewa.
Bai san cewa shigina in har akwai mahaluki a cikin shi ba Allah na karewa yadda yaso.
Tabarma mana ta shimfida masu daga dakin ta nan ma yai matukar mamaki wai dakin da ake rayuwane, acikin shi haka.
Ruwa ta debo masu acijin wani kufin silver ta sabo ta kawo masu bashar ya karbi ruwan ya dan kora a cikin shi.
Shikan bai san yaya