Showing 162001 words to 165000 words out of 373688 words

Chapter 55 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

koma dakin har yanzu Baba yana ciki suna hira da gwagona sai Maji dakan dan jefa masu baki jefi jefi.
Bai so haka,ba don hutu akace Maji ta samu ba yawan surutu ba gashi gwago tana sata magana kuma.
Ga mamakin shi sai yaga Maji ma ta kara sakewa sosai akan baya don yinin da sukayi da gwago suna da surutu batai yawan kwanciyar da takeyi ba ranan.
Da,ya,dawo da yamma gwago take cewa ita anan zata zauna da Maji sai dai ni na koma gida.
Yasan idan na koma,akwai matsala don gwago jikinta ya yi nauyi bazata iya abinda nakeyi ba kamar ni.
Yace ai ba matsala kubarta a,nan don koda ana son yin wani abu sai tai maku.
Haka muka zauna tun ranan da gwagona dake kawar wa maji da damuwanta.
Sarai Maji ta samu lafiya sosai yanzu har ita da kanta take bukatan sallama amma sadauki ya hada,baki da likita a barta har zuwa lokacin da sukace sunan son su sallamay ta.
Bayan na,wanke yan kayan da muke amfani dasu a,sibitin ne sai na fito waje na zauna don nasha iska don zama ciki ya isheni.
A nan inda nake zaune ya samay ni yake tambayana barci sukeyi ne dana fito nace mashi eh shiyasa nafito don kada na tayar da su.
Nai mamaki danaga yasa hankici daga gefena ya zauna wayan shi tai ruri ya dauka.
Magana sukeyi da wani akan zasu fita kasan waje wasa amma yace bazai samu zuwa ba don yana jinyar mahaifiyar shi asibiti.
Mutumin yake ce mashi da ya daure su fita don akwai kudi da yawa a wanan wasan da zasufita yi yace gaskiya sai mamana taji sauki zan iya fita wani wasa sai yakashe wayan nashi baijira mai mutumin zai fadi ba.
Yana kashe wayan ya furzu da iska daga bakin shi tare da dukar da kanshi saman cinyar kafar shi kamar wanda damuwa ta dama.
Tausayi ya bani a lokacin saidai shi ba abin tausayi ba ne don duk wanan halin da mama take ciki shine sanadin hakan ai.
Ban san ya akayi ba sai ji nayi ina cewa yaya sadauki don Allah kayi hakkuri da abinda zan fada maka bawai nakai na fadi bane amma dole tasa zan fada ma koda bazakai amfani dashi ba.
Kan shi ya dago yana kallona cikin mamaki tare da kura min ido, nikuma banji tsoron shi ba naci gaba da cewa.
Ba tare da fargaba,ba nace why baka tausayin kan ka dana mahaifiyar ka?
Nace yaya wanan ciwon ban fadawa kowa ba,kaine silar haka ga mama sanadin irin rayuwan da kakeyi yasa mama cikin waban halin.
Idan dare yayi mama bata barci ko yaushe tana kai kukanta ga Allah akan al,amarinka.
Amma kuma,,,
Sainai shiru na kasa,karasa abinda zan fadi yace amma kuma may fa.
Nace a hankali yaya sai naga kamar baka sani ba kai don kullun ba batun dainawa kakeyi ba sai kara nausa,kanka kake a cikin wanan harkan ta,shaye shaye kishiyoyinta suna fada maganan banza wanda ke saka,zurciyar ta,kara,fadawa cikin halaka.
Shiru nayi kamar yadda shima,yai shiru nace yau abin bakin cikine ace duk yawan gidan nan kaine kawai nata kuma kaine mai jawo masu magana.
Kowa fa yana da nashi illar amma sun boye nasu saikai dake yi afili ake ganin naka.
Don Allah yaya idan ma,sha zakayi ka tafi can nesa da ita inda ba wanda ya sani kayi abinka.
Amma da zaka bari gaba daya shine alheri gareka dama kowa naka don nan gaba ba haka zaka zauna ba.
Kaima iyali zaka tara yau idan yaranka suka taso suka ganka cikin wanan halin ashe baka ganin tarihi zai iya maimaita kan shi gaba.
Za ai masu gori za aiwa matarka gori za aiwa yan uwan ka gorin hakan.
Shi wanan abin an san jarabta ne daga Allah amma kuma sai bawa yayi kokarin nisanta kan shi daga gareshi don gudun zama mujiya a cikin al,umma .
Baiwa arziki yaya duk Allah yai maka kamarya da kanka abin alfahari yadda ko wace uwa zataji dadin yin alfahari da zurian ta.
Nace amma,,,,,
Yace ke dakata haka ya isheni na kuma gode da kika kalli idona kika fada min gaskiyan abinda babu wani mahalukin da ya taba tarona ya fada min irin haka.
Nasan kinyi kokari yadda kika kalli idona yau kika fada min damuwarku akaina wanda yan uwana dangina abokaina ba wanda zai iya fada min shi.
Koke nasan saida kika shirya fada min don naga saida babu kowa a tare damu kikai min wanan magana ko haka na gode insha Allahu nima ina kokarin ganin na daina don bayanin da likita yai min a officer din shi nasan zancen da Umma taiwa majine last week ya hefata cikin wanan halin.
Da sauri nace ashe kaima ka sani yaya mikewa yayi yanackakabe wandon shi yace tundani ba mutum bane yaya zan sani.
Ya sakai ya wuce ya barni zaune a gurin take naji kamar ancire min wani dutse a zuciyana nace a raina koba komai dai na samu ya saurareni dole ne kuma daga cikin zance na yai amfani da wani yai mashi tasiri aran shi.
Ina gurin a zaune yafito hakan yasani sanin har lokacin barci sukeyi basu tashi ba.
Yana isowa inda nake yake cewa ni zan tafi idan sun farka ki fada masu cewa nazo sai na dawo anjima.
Yatafi abin shi nabi bayan shi da kallo ga mutum har mutum amma kuma babu shedun alheri tare dashi.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKK8N WASU PLEASE,,,,,,


A LOKACIN MU KE,,,,,,,,,,,


An sallamo mu daga asibiti bayan gwaje gwajen da akayi kan mama an tabbatar da ta samu lafiya yanzu sosai,
Sai dai likita ya kara jaddada muna cewa a guje bata mata rayuwanta, wanan kalamin na likita a gaban kowa akayi shi.
Duk yaran mama suna kusa haka yaya sadauki yakoso su zuwa gida motat tashi bata daukan mu duka don haka ni da maryam muka hawo Nepep zuwa gida da sauran kayan mu.
A kofan gida muna sauka na hango yaya Imirana da wata yarinya yar makwabtar mu ya rike mata hannu yana wasa da ita.
Kawar da kaina nayi tankatmr ban ganshi ba amma da yake baida zuciya muna kawowa kusa sai cewa yayi adon gari kun dawo.
Yaya mune kuma adon gari yau inji maryam yai dariya yace inbada abinki maryam ai yan mata adon gari ne ko?
Wanan yarinyar da Maji zata ban ita aida na more wallahi ta juya tana wa Bintu yace ita fa.
Ai babban adon garice wanan tun dai in ta samu guri zakiga ta baje ne kwana biyi lokacin caji ya fara daukan ta.
Nace ba adon gari ba adon dawa mara mutunci kawai, maryam tace ke Bintu yayan nawa kike zagi a gabana yanzu zamuyi fada kuwa.
Ban tsaya basu amsa ba na kwashi kaya zuwa cikin gida, ban san yana tsaye ba jikin motanshi sai da nazo shigewa na gan shi a tsaye ya sha bakin glass a idon shi.
Ni dai na,shige yabini da harara kawai, tun kan nashigo nake jin hayaniyan yan gidan ga kida na tashi dakin Umma.
Haka yasani sanin Nafisa tana gida a lokacin don idan tana na zakaji sauti yana tashi a dakin su.
Na samu su mama da gwagona zaune a falo nan na zube kayan suna min kun iso nace eh.
Nazauna ina cewa wai Allah mun gode ma, jiki dan tafiyan nan kikewa wai inji Amirah.
Kafin nai magana cikin muryan mara lafiya mama tace tunda baki san kwana rayen da takeyi akaina ba ai zaki fada mata hakan.
Amirah tace cikin make murya maji tare fa muke kwana da Bintu don dai na daina kwana biyu kawai.
Kudai kuka sani ace uwar mutum na asibiti amma ku har kunji dadin kwana a gida.
Ashe badon Allah ya kawomin wanan yarinyar ba sai dai na karata can ni kadai.
Gwagona tace a,a haba hjy ai bazasuyi haka don dai sunga ita din tana masu kara ne kada su raina mata shiyasa.
Mai masa bari yaran nan ban san irin su ba kodan sunga su kadaine min suke min wanan halin ban sani ba.
Amirah ta tashi tashige daki tai fushi da maganan mama, nice ma na tashi nabi bayan ta har zan shiga gwagona ke cewa dawo mana ki kwashe kayan zuwa ciki kada a barsu nan watse.
Maji tace ai kinga abinda nake fadi din waya fara dawowa cikin su ba ita ba amma batai azancin ta kwashe ba.
Suna ganin abinda sauran yaran gidan keyi sun zaci alheri ne basu san cewa suma gidan wani zasuba.
Idan kaje gidan mutane kace kai baka iya motsa jikinka kai komai sai dai ai maka aiko akwai aiki babba.
Da sannu za,a koya masu tunda basu saba da hakan ba tun farko amma ai zasuyi insha Allahu .
Allah dai ya kyauta mai masa yaran nan halin su sai su wallahi basu san ciwon kan su ba.
Koma irin yadda ake min a gidan su baya damun su dawasu ne ai basai an fada masu abinda zasuyi ba wanda ya dace.
Kiyi hakkuri hajiya kowa da ir8n halin shi amma bari zasuyi idan ana lurar dasu.
Na samu Amira a daki tana, waya nashigo dakin , tabini da kallo tace yanzu duk kokarin da nake wai maji bata gani.
Nace Anty uwa uwace duk abinda suka,fada muna gyara ne a garemu mu godewa Allah da ya barmu dasu a raye.
Wanda baida uwa fa a duniya bai kuma damai kwabamashi fa.
For god sake may ye banyi a gidan nan ne wai amma kulun maji tace banyi daidai ba.
Fadan iyayye fa takine gare mu anty tun da tace haka yanzu da ta dawo gida sai ki matsa ki kula da ita yadda zata ji dadin ki.
Kallo na tayi kamar zatai magana sai kuma tai shiru kawai nikan na koma dakin mu na,shiga wanka don duk warin asibiti nake jin ina yi a jikina.
Bayan nafito ne na tara duk kayan da mukai amfani dashi asibiti na wanke su tas sannan nadawo falo na zauna sai naga Amirah tafito.
Taje gurin mama tace a kawo maki abinci ki dan ci ko da kadan ne maji don rana yayi lokacin shan maganin ki ya kusa.
Uwar taji dadin haka sosai don ta kasa boye farincikin ta tace tau akawo min Amirah.
Ta hado ta kawo mata har gaban ta tare da ruwa da maganin gaba daya.
Maji tace mata na gode Allah yai maku albarka da haka kuke min wa zaiji mu daku.
Gwagona tace tau gashi dai uwata ta gyara yanzu ai shiya fadan yake da dadi ga yaro don ya gyara kuskuren shi.
Tajuya inda nake tana cewa ke kuma Bintu wallahi ki bar yi wa maji komai daga yau kibarni ni zan mata.
Maryam tace wallahi saidai a raba amma ban yarda nima ai ina son albarkan .
Nan dai aka wasance zance ana dariya tajuyo tana daga min gira alaman godiya nima hannu na daga mata alaman komai ya wuce.

****** ********* ******
Kabir yazo duban jikin maji da ya shigo kauyen su kamar yadda ya saba duk karshen wata da yake zuwa.
Kabir ya iso gidan namu amma bai shiga ciki ba, ya tsaya daga kofan gida inda ya zauna cikin motar shi.
Yana saye da kananan kaya amma dinkin shadda ce akai mashi karamin dinki dashi.
Sai kamshin turare yakeyi ajikin shi yai matukar kyau dashi sai annuri yake .
Waya ya buga min cewa gashi ya iso a kofan gidan da nai mashi kwatance.
Na fito acikin hijjab dina duk da nasha kwaliya daga ciki amma na rufe jikina da hijjab.
Waya yake amma hankalin shi yana a kaina yana kallon yadda nake takona ina dan waige don ban sheda motar shi ba da yazo da ita.
Saida yai min horn nagane cewa shine acan gefe daya zaune cikin motar shi.
Ina isowa inda yake ya kashe wayan shi yana min wani kallo can kasan idon shi.
Na dan duka kadan ina cewa barka da isowa ya hanya ya mutanen gida suke?
Yace duk suna lafiya suna gaida ke amma uwargida tace tana fushi dake wai baki taba kiranta kun gaisa ba.
Nayi murmushi gami da cewa karufa min asiri don Allah, yaya ina ni ina kiran ta tace banda kunya.
Yace aiko gara ki daina jin komai don Haulatu tace bata dauke ki kishiya ba a matsayin yar uwa da kuka fito shiya daya ta dauke ki.
Nai murmushi kawai tare da cewa Allah sarki aiko na gode Allah ya bamu hakkurin zama da junan mu.
Ya amsa cikin jin dadi da fadin amin my love, har kin sa naji wani sanyi a,raina da na ga wanan gidan da kike har na fara fargaban kada wani ya kwace min ke anan.
Nace haba yayana ai kyau alkawari cikawa da bazanyi ba tun farko baxaka ga ma fuskana ba ai har mukai haka dakai.
Yace nako gode da,wanan karamawan da akai mun yanzun hankalina ya kwanta sosai da jin kala man ki.
Nan muka dan dauki lokacin muna hira dashi sai dariya yake bani na yadda zamu zauna a gidan shi.
Tun daga nesa na hango motar shi tafe da karfi yazo ya park dan nesa kadan damu.
Tun karyo kwanan shi ya hango su mamaki yake irin yadda ya hangota tana dariya abinda bai taba ganin tanayi ba a rayuwan ta.
Kallon wanda suke tare yake inda yaga maishi ai ba yaro bane ya ma girmi duk yan gidan su balle shi.
Amma shine wanan yarinyar ta tsaya haka har take wasan baki a gaban shi koma may wanan zai iya fadawa budurwa har taji dadi haka.
Ko dai dama da wanan tsohon take waya tana wani kashe murya a gaban mutane ba kunya saboda wanan tsamuraren mutumin.
Wani ir8n haushi da takaicin yarinyar ne da baitaba jin irin shi ba ya kama shi.
Ya fito daga motan shi lokacin Kabir ke tambayana waye shi nace mashi yayanane na nan gidan.
Don haka yafuto suka gaisa sama sama dashi kamar mai sauri ya shige abinshi tare da gaura marfin motar shi.
Kabir ya juyo inda nake yace tau ikon Allah nace rabu dashi haka yake hutsune dama shi baida mutunci.
Dakin shi yanufa yana jin wani gumin bacin rai yana fetso mashi ya bude dakin shi ya shige hakana.
Mun dan kara dauka lokaci yai min sallama tare da mika sakon shi gurin mamana da bata da lafiya.
Nan yake ce min shi abinda yakawo ma yaji kunya don wanan gidan abin yai kadan wallahi.
Cikin mamaki nace haba aiba komai wake raina alheri sai mara godiyan Allah kawai.
Nan nasamo yara suka shiga dashi nace sukai dakin maman UF don sunfi gane ma hakan.
Mukai sallama yatafi sai banji dadin hakan ba don ban so mu rabi dashi ba don jin dadin dan kasancewar mu na dan lokaci a tare.
Har na shigo gida yana tsaye a kofan shi kamar may waya take yaji zuciyar shi na azazzalar shi tankat ya shake a lokacin.
Can kuma yai tsuki yace ina ma ruwana da yar iska komay zatayi taje tayi mana may ye hadina da itama dahar na damu kaina.
Sai zuwa dan wani lokaci ya shigo gidan inda ya samu kayan da Kabir ya kawo muna a falon mama.
Ya shigo wani iri dashi idon shi akan kayan duk da kayan ba laifi amma sai yaga ai duk komatsen banza ne kawai.
Ya samu guri ya zauna yana fadin wanan kayan kuma fa haka?
Amirah tace surukin kane yazo yaya mai neman Bintu shi yazo yakawo wa Maji na dubiya da Allah sawaka.
Ance mai mu bamu iya saye ne sai ya kwaso muna wani tarkace haka ba kyau gani.
Ko an fada mai mu makwadaita,,,,,
Kai don Allah ya isa kai wani irin suruki ne kuma maimakon kasa albarka sai kuma ka fara fadin maganan banza kawai don Allah kwashe min su zuwa ciki kinji maryam.
Maryam ta mike tana fadin ai yaya an fara kawo maku tarkace ke nan tun da maji ta tara zuka zukan yan mata haka har uku a dakin ta.
Amirah tace wanan kan nima nawa yana tafe sai aka sa dariya kawai gaba daya maji tace Allah kawo shi lafiya mugani ni dai naga ta ya ta saura naku din.
Wallahi Maji kina bata yaran nan haka fa na hango wanan yarinyar a,waje da wani tsoho tana wani washe baki kamar taga wani saurayin kwarai gaban ta.
Daga inda nake ciki ciki nace kai kaga tsoho nikan bai min tsufa ba wallahi ai aure ba inda baikai mace.
Maji tace wallahi ke dai ya ta ai in an kwana biyu zan fadawa babaku don yasani kada yaga kina tsayi dashi kofan gida yazana,min matsala.
Cikin hasala yace may kikace banji ba fadi mana naji ya fifito da idon shi waje.
Maji tace kai ban fason hauka ko kuma kayo shaye shayen nakane zaka sauke muna hauka anan.
Mikewa yayi tare da kutawa yace wallahi maji duk ke kesa yarinyar nan tana rena mutane bata jin tsoron kowa a gidan nan.
Na,sa ubana sai kai min fada ko in ba


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login