Showing 153001 words to 156000 words out of 373688 words

Chapter 52 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

amma,sai yayi kamar ya,bari sai kuma,ya,tsunci kan shi dakara komawa gasha kuma.
Ya Allah ka kawo min agaji cikin wanan halin rayuwan da nake ciki.


Ai hakkuri da,wanan bayawa yau nagode da,bani lokacin ku da kukeyi kullun Allah yasa,mu gama,da duniya lafiya yan uwa


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


A LOKACIN MU KE,,,,,


Yanzu al,amarin Aliyu yakai har gidaje masu sayen ruwan pure water shi suke aiken shi.
Ko kuma,su aike shi dakunan su na,gwauraye yakai masu abu ko ya dauko masu idan ya dawo su dan yi mashi dan ihi sani na kudi ko wani dan abin kwadai.
Uwaye lokaci muke yanzu da,ba,yarinya mace ce kawai zaka,nisanta tata irin wa yan nan abubuwan ba har da,namiji idan kina dashi dole idon ki yana a,kan shi tun dai in ya fara shiga adolarcent year din shi na,balaga.
To yanzun ma yakai ko yaro baikai wanan shekarun ba,yawon yara,yai yawa don sun san komai na,rayuwa,da birni da kauye.
Maria ba abinda ya damay ta binciken al,amarin dan ta sai alfahari take Allah ya hore mata da mai hazaka ga kan talla gare shi yana da sa,an samun ciniki sosai.
Bata kula da cewa wani lokaci idan yadawo baya damuwa da cin abincin gida sai dai yace mata ai ya koshi.
Daga cikin masu aiken shi a kwai wani matashi anace dashi sisko don irin wankan da yakeyi na matasan zamani.
Amma shi ba ruwan shi da yan mata sai dai yawan son wasa da yara musan man maza.
Haka yasa sisko ya ke son Aliyu sosai a rayuwan shi don yana yawan ba yaron kudi ya sayo mai abu idan ya dawo da canji ko nawa ne sai yace ya barshi kawai.
Haka yasa har Allah Allah Aliyu yake da,sisko yafito majalisar su hira idan bai gan shi ba ya kafa tanbayan yau sisko bai fito bane wai.
Shiko idan ya fito ya,shiga wasa da yaron ke nan yana dan matsan shi cikin jikin shi.
Har sai yagaji tace yaje ta sayo masu wani abu daga cikin kayan zaki ya dauki rabi ya,ba yaron rabi tace ya,dauka duka.
Su kuma mutanen dake zama,gurin basu damu da saka masu ido ba,su dai kawai suna ganin tasu ce tazo daya,kawai kamar yadda,jin mutane kan hadu.
Rana Sisko bai fito ba har kwana,biyu don haka Aliyu ya matsa,har saida,akai mashi kwatancen gidan su Sisko din.
Yana zuwa,ya,samay shi a dakin da,yake haya,daga wajen wani gidan haya kasancewar shi gwaro yake daga,dakin kofan gida.
Kwance yake dakin rubb da ciki yana kallon wani film a tv dakin shi,
Yaron ya dan tsaya daga,waje yai sallama ya gane muryan shi yake cewa,a,a Aliyu mai pure water shigo mana.
Waya gwada ma gidana yaron yace tambaya nayi aka nuna min ance baka da lafiya shine nazo dubaka.
Yace wa yaron ya zauna su nan zaune yana dan mashi wasa ne yake cewa ya ya karbi kudi ya sayo masu cock su sha da maltina.
Yaron ya,sayo suna,sha,suna hira yake tambayan shi ruwan nawa ya,dauko yace mai ta,dari uku ce yaciro dari uku ya,bashi yana cewa, idan baka,son talla tunda kaga,dakina,sai ka,dinga,zuwa muna,kallo sai na,saye ma,ruwan ko.
Cikin jin dadi Aliyu ya,karbi kudin yafita yana godiya tun daga wanan ranan take zuwa gurin Sisko don yasan lokacin da yake gida.

****** ********* ******
Raiha yanzu bata shayin kowa don ta riga ta bushe fitilar ta ko, a wani yammaci sun shirya da Nura zasu wani bukin wata kawar Nura din a wani unguwa.
Acika an yi yawa gurin taron ida shahararun yan mata ke gwada kwalliyan su.
An fara program din ne Raiha da Nura suka,ratso ta gaban mutane suka,shigo inda ake reception din.
Idon mutane caaa a kan su don kwalliyan su gaskiya,ba laifi ko a gidan wa zasu iya zuwa a hakan.
A hankali suke duban gurin da babu mutane da yawa a saman kujerun zaman dake gurin .
Can suka hango wata yarinya zaune ita kadai dan nesa da,bango take zaune.
Don haka can suka nufa suma,suka zauna sun so su basar da juna amma,sai take ce masu sannun ku fa.
Su ma,suka amsa da,yauwa ya,garin dai ta ansa da lafiya kina tare da,wani ne ?
Nura dake gyara zaman ta take tambayan yarinyar da,suka,sama a gurin ita kadai.
No ni kadai ne ina jiran wani ne dama kuma,ba,a barshi ya shigo ba wai baida pass.
Kallon junan,su sukayi sai kuma,suka,danyi murmushi kawai au shi wanan bukin har da wani pass ake nunawa cikin sa.
Yarinyar tace wai haka sukace maza ba kowa za,a bari ya shigo ba,wai sai wanda yake da pass din.
Ok ke kuma,sai kika kyaleshi kawai a,waje ya zauna yana dakonki kawai.
Sister maye naki a cikin, ne wai mu dai ba mun samu wajen zama ba kawai.
Abinda yaba yarinyar mamaki shine yadda haddadun gayu ke zuwa kawo wa su Raiha gaisuwa har saman table din da suke.
Wasu sukanyi zaton tare da yarinyar suke sai su dan so kutsa kan su gare ta sai Raiha ta dakatar dasu tana cewa kai wanan bakuwar hannu ce fa,bata san kaiba tukun.
Bayan su mata san masu ji da kan su sun tafi Nura ta juya gurin yarinyar tana cewa waike ya sunan ki ne.
Ta dago daga dannan wayan da takeyi tana cewa, wani tace ke mana.
Yarinyar tace hmm sunana Nafisa Abubakar ok anan garin kike da zamane ta amsa da cewa cikin dan dago kanta,
Eh nan ne gari mu muna zama a sama,road ne nida iyayyena.
Nan dai Nura take dan jan ta da fira da,zasu tafine sukai musayan waya.
Nafisa ta riga su fita don haka sai abin hawa yai mata,wuya a lokaci don matasa na cikin hole din sosai ana ta shan shagali a ciki.
Sunzo wuce wa ne Raiha dake driving ta hango Nafisa tsaye sanan titi sai faman kallon inda zata samu abin hawa takeyi.
Nurace tace don Allah tsaya mu ragewa wanan yarinyar hanya don yarinyar taimin wallahi.
Ban gane tai maki ba,damay tai maki ne wai a,a kema kin sani don idan ta,waye ai zata faso itama.
Nan dai Raiha tai ribas suka tsaya,suka taya mata shiga su sauketa a gida bata musa ba kodon a ganta da,wa yan nan haddadun gayun abin bajintane ai.
Tashiga suna tafe Nura tana marming din wankan dake tashi a motar tare da dan dakilar wayan ta da yazama rabin rayuwan mutanen yanzu.
Can ta dago ta juya kadan inda Nafisa take zaune komai na yan matan yana burge ta wallahi don sun matukar wayewa.
May ma,sunan ki kace tace a hankali Nafisa nake , tace ok ban nombanki watara ai za,ai zumunci ko Nafisa taji dadi dama tana so tana gudun ta zubar da kan tane garesu.
Nan sukai musayan nomba a tsakanin su inda takirata da nombanta itama tace a hankali wazan sa don ban san sunan ku ba .
Nura tace a baki bukaci hakan bane mukan ai mun tambayi naki don kin bamu gurin zama.
Nuratace zaki iya kira na da Nuriya ko Nura ita kuma wanan driver din zaki iya ce mara Raihanatu.
Wallahi sister zamuyi tsiya dake idan kina bata min suna ba Raihanatu ba yar iskan banza sunana Raiha kiji baby.
A daidai kofan gidan su da tai masu kwatance suka tsaya da motan su a daidai lokacin da Bintu ke fitowa daga cikin gidan ita da maryam.
Wani kallon banza suka,watsa masu suka,wuce su nan Nura ke tambaya wanan yaran yan gidan nan ne naga sun wani hade rai da,suka gan mu mana.
Kyale su yan kishiyane bakin ciki suke kawai dashi kuma zasu mutu yan hassada kawai.
Sukai sallama ta shiga gida suka,wuce sai sautin kida ke tashi daga motan su.
Bayan motan sadauki dake fitowa yagani tare da,bin Nafisa da harara ta make gefe ya fice abinshi.
Tana,shiga ciki take cewa,uwarta ni ban san may naiwa wanan dan mayen ba,sai ya wani kama hararana.
Da,sauri uwar ke cewa wa sadauki wallahi ahir din shi dake bari ma,na,samu uwar shi tun yanzu.
Ta mike sai dakin maji sunyi daidai da ita a tsakar gida take cewa Hawau kiwa danki fada wallahi ya,fita idon Nafisa don ban haifar mashi ita ba.
Shidake da abin fadi tab ga tsuliyane har zaicd zai sakawa wani ido akan may?
Da yake iskancin shi a gidan nan waya hanashi yin abinda yaga dama da zai wani sa,wa yarinya ido.
Baima da kunya da bai kalli inda Nafisa take ba,sau nawa yake zubar da abin kunya babu mai kwasa a gidan nan.
Kai bama gidan nan ba,duk gari kowa yasan irin tabargazan dayake mai abin kunya kala kala har basu faduwa ma.
Tana juya sadauki yana tsaye sai su maryam da Bintu daga gefe Amira tana tsaye daga kofan su cikin mamaki don ba dama ta tanka saboda mahaifiyar su ta hane su da hakan.
Maji tace tau yaya in ma sadauki nada abin fadin da har bai faduwa ina dai uban su daya da Nafisa ni ban san yadda zan raba tsajanin su ba.
Umma tace in baki sani ba,aini na sani don ba kare bin damo yabar ganin dan wanan abinda yake torokon yana samu ko zai rudeni na kasa daukan wa diyata incin ta.
Wallahi duk randa yai gigin taba min yarinyar ranan ba kwaya, yaje sha ba ko dan babule yake sha zai gane kuren shi.
Abin kunya ma hada alaka da irin ku ko barnan suna har yana wani kirarin wai yar uwan shi ce ita.
Wai may akayi ne Maji ?
Sadauki dake karasowa yake tambayan mahaifiyar tashi cikin bacin rai.
Hannu kawai Maji ta daga mashi tace babu ruwanka bari ta fada min abindake ranta dama,ba yau ba take dashi.
Kada ki min rashin kunya kan wanan tabararen dan naki mara mutunci wanda ya zama abin nune ga mutane.
Ina fatan Allah ya,shirye shi dashi da,duk wani mai irin halin shi ma.
Daga,baya ke nan bayan an kasa,ba,yaro tarbiya,tun farko sai yanzune za,a roki Allah kuma.
Ta,wuce a fusace tana fadin wallahi shege ka,fasa a gidan nan ni daku marasa mutunci kawai masu abinfadi lodi lodi kawai.
Daki suka,shige gaba dayan su suna fadin wai may kuma yafaru yanzu yanzu ne wai ?
Maimakon uwar tai magana,sai kawai ta,fashe da kuka mai tsuma zuciyan duk wanda ke kusa a lokacin.
Sadauki yace wai maji don Allah may yajawo wanan cin mutuncin ne haka wai?
Kai ma ,
Wazai ja min in bakai ba mai abin fadi lodilodin da akace aiba karya aka fadi ba ba a fadin ne ko yaushe.
May yakai ka ga yarta wata yar tata kuma ya tambaya da sauri don bai san kan wanda ake zance ba.
Maji tace Nafisa mana,
May naiwa Nafisa kuma ya tambaya a cikin mamaki?
Ai duk abinda kai mata ka,sani tunda baka rabuwa da yarta bayan kasan gorin da zai biyo min baya.
Wallahi azeemun ban cewa Nafisa kala ba kuma Allah ne shedun hakan wallahi.
Koma dai maye kaka sani kaita hi kana jamin gorin da banda baki akan shi.
Mamaki takaici, bakin ciki suka rufe mai zuciya sai muryan Bintu sukaji tana cewa aiko kowa nada abin fadi don itama ai ta haifi yar iska.
Ranan ai ganin Nafisa nayi kwance saman jikin namiji a mota shiba iskanci bane.
Ke Fatima kada kiwa yar uwar ki sheri don ta bata min rai don sheri kare ne mai shi yake bi, don haka ki bari.
Haka Allah yaso zamana acikin su don haka sai kowa yayi hakkuri.
Da,wanan bai fitar da kanshi daban acikin halin yan uwa ba da duk ban ga hakan ba.
Ta mike zuwa ciki ranta a bace mata don zafin maganan da aka,fada mata bata da,bakin mayarwa.

****** ********* ******
Wanan magana wasa wasa saida yakai maji kwace don tun lokacin da akayi shi Maji bata,kara lafiya,ba a jikin ta haka ta koma,sukuku don zancen Umma yana,gasa mata zuciyar ta sosai.
Bayan kamar sati da maganan zazzabin Maji ya tsananta ranan kwana mukayi ba muyi barci ba ,
Gashi sadauki baya gari yai tafiya Baba ma bai nan ya tafi kasar Niger state zancen noman shi.
Nace wa su Amira gaskiya ya kamata da,safe muje asibiti don bazamu zauna da ciwo ba haka a gida.
Amma sai Amirah take ce min wai mu dai bari Baba ya,dawo tukun muji mai zaice.
Da,asuba nazo tayar da ita tai sallah naga irin yadda take numfashi yana fita dai,dai.
Nace a raina kai wallahi nikan asibiti zamu da safe don in mun biye mata zata halaka a daki kwance sai paracetamol muke dirka mata.
Muna idar da,sallah Na samu Amira a kwance, nake ce mata zan fita na nemo mota idan gari yadan haska muje asibiti da mama.
Da wani mota zaku kin dai san babu mota yanzu a gida dashi akewa baba aikin gonan shi.
Nace ai akwai na haya ko?.
Ta zaci zance kawai nakeyi nafita ina mamakin hali irin na su Amira halin ko inkula da sukeyi uwar mutum ba lafiya amma su kamar ko a jikin su.
Gari na dan haske na,saka hijjab dina nafita daga gidan sai bakin titi nai sa,a na samu mai adaidaita sahu irin masuyin sakko gurin neman kudi.
Muka,shirya dashi nace ya kaimu asibitin koyarwa ta gawon nama, watau teaching hospital.
Na leka dakin su Amira suna,barcin su hankali a kwance na koma gurin Maji na samu sai nishi take guda, guda.
Cikin matsanancin tsoro da,firgici nace mama tashi muje asibiti aduba,ki.
Batai min mussuba kamar yadda na,zata, don haka na,dauki hijjab na,saka mata tare da son mu fita .
Cikin karfin hali take ce min, dauko jakata akwai kudi a ciki mu tafi dashi kada muje mu wulakan ta.
Har muka fita daga gidan kamar babu mutane kowa na,dakin shi rufe na,sayawa su Amirah kofa muka fita daga gidan.
Ban taba zuwa asibitin ba amma haka na daure muka shiga don ba wani nisa ne sosai a tsakanin mu ba.
Munyi sa,a don sanmakon mu yai muna rana muna zuwa aka kaita emergency don sunga yadda muka shigo da ita.
Bayan yan aune aunen da,sukai matane likitan yake cewa ke yarta ce na amsa mashi da eh,
Yace to ina manyan ku suke aka bari ke karama dake kika kawo mara lafiya haka acikin wanan yanayin asibiti ?
Nace, Baban mu baya gari shi da yayan mu sunyi tafiya yace alright yanzun dai zamu bata gado tare da bata taimakon gagawa tukun kafin mu auna ta muga may ke damun ta haka?
Sai da na,tabbatar da cewa an bamu gado anyi komai har an saka mata ruwa na dauki waya na kira Amirah wace cikin gigin barci take min magana.
Nace Anty gamu fa asibiti da mama an saka mata ruwa ma ko.
But tamike da mamaki azaton ta wasa ne don shirmay ta amma tana dubawa dakin Maji sai taga wayau har falo taje babu mu.
Bayan kiranta kamar kada na kira yaya sai dai nace bari na kirashi dai yasan halin da uwarshi take ciki.
Babana ta rubuta wajen sunan shi na danna kiran layin baifi ringing uku ba ya dauka yana cewa,
Maji yanzu nake son kiranki naji ya jikin don jiya Amirah ta fada min kina jin jiki sosai.
Nace ba mama bace nice Bintu gamunan asibiti da mama an bata gado.
Yace cikin wani irin murya what, anba Maji gado a,wani asibitine kuke?
Nace na,gawon nama watau Usman dan fodio teaching hospital.
Yace ke ba Amirah wayan please nace Amirah tana gida bata iso ba tukun
To wa ya kawo ta,assibitin ita Amirah tana mayye nace ta tsaya hada break ne.
Tsuki yaja tare da kashe wayan ashe bayan ya kashe Amirah yakira yace yaya jikin na maji wai may ke faruwa ne.
Tace wallahi yaya ban masan sun tafi Asibiti ba Bintu ce ta kirani take fada min yanzu wai suna asibiti.
Yace you are very stupid Amira yanzun saboda shegen barci tsiya har aka fita da Maji gida baki sani ba ke kina may ye har wanan yar kauyen yarinyar ta kaita asibiti.
Tas yai mata tare da umartan ta duk abinda take tai maza ta samay mu asibiti kafin ya bata mata rai.
Ina zaune na tasa maji da ta samu barci a gaba sai ga Amirah da maryam a gagauce.
Sun wani fuske sun dauki zafi dani ban damuba don nasan ni don Allah nayi masu.
Don danabita nasu sai dai ta halaka a gida saboda sanyin jikin su da narkewa.
Muna nan zaune sai ga likita yazo da takarda magani a rubuce yace suna bukatan wa yan nan.
Karba Amirah tayi tare da ficewa dakin dagani sai maryam ke kan mama din.
Ajima kadan sai gata tadawo da takardan tana fadin ke Bintu nifa ban san inda ake sayar da maganin su ba.
Nace a tambaya mana take cewa wai wa zata tambaya amsa nayi tare da daukan kudi ga post nafita.
Da tambaya,na gane gurin sai gani da maganin cike da leda nashigo dakin nan na mikawa nurse din dana samu tana


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login