Showing 159001 words to 162000 words out of 373688 words
Chapter 54 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
su wani gurin yan uwan su ko gidan kawarta sai kawai su fita garin suyi kwanakin da zasuyi ba ta gidan.
Gashi ir8n na fitsara ba komai bane a gurin ta don wayewan ta tana ganin yakai haka ita.
Al,amarin ciwon maji yasa Alhaji baro aikin shi ya dawo gida don ganin yadda jikin naya yake saboda hankslin shi yaki kwantawa da jin da yayi an bata gado.
Yana isowa ya wuce asibiti direct Don ganin jikin nata, ya samu Tana zaune ina tsaye agaban ta ina we, mata lemun tana Dan sha a hankali.
Baba yashigo dakin da,sallaman shi Nan muka shiga gaishe shi dadawo daga tafiyan da yayi.
Idanuwan shi kyar akan ruwan da ke kafe daga gefen mama ya Kara juyo kallon shi a gareta Yana mata sannu da jiki.
Ganin shi yasa mu kokarin Fara barin dakin don mu kauce masu daga dakin.
Yake cewa ku tsaya abinku Fatima ance kece Kika kawo ta asibitin har aka baku gado to Yaya likitan yace yanzu .
Nace cikin dukar dakai likitan yaiwa Yaya sadauki bayani dazun da safe Kuna ya Kara rubuto wasu maganin da za,a saye.
Yace zasu kwantar da it's na sati biyu anan don ta samu Hutu sosai a jikin ta tare da treatment din ta.
Ok hakan na dakyau ai said dai ku dinga barinta tana samun barci sosai zaifi Kara mata lafiya .
Bai dade dashigowa ba sai ga sadauki ya shigo dakin ya sayo maganin da likitan ya rubuta mai yana fadin da kyait muka samu maganin babu shi nan cikin asibiti.
Yaiwa mahaifin shi sannu da dawowa tare da tambayan shi Yaya aiki a can inda ya fito.
Muna waje zaune saiga Yaya Imiran yazo don sunyi waya da baba yace sure hadu a Nan asibiti dashi.
Zan iya cewa tunda mukazo asibiti bai shigo gurin Maji ba don ya Dubai lafiyan ta Amma salmanu Dan wurin mama Asiya zuwan shi biyu Kuma harda fruit yakawo Muna.
Ya na isowa ya gan mu, zaune mu uku nan Suka fara gai da shi cikin ladabi, Banda ni dake zaune ina mashi wani kallon raini kawai.
Tambaya yayi ko baba Yana ciki suka bashi da amsa da eh Yana Nan cikin dakin.
Yana kokarin shigewa naja wani tsuki da karfi Yana ji sai dai bai juyo ba ya shige ciki kawai abinshi.
Muryan anty maryam ce naji tana cewa ke may ya hana kiki gaida yayan mu Bintu?
Nace bai isa na gaida shi bane kila don da nagaida shi inda mutumin kirki ne.
Fitowan shi yasa su yin shiru suna mashi sai anjima, bintu tace haka dai za,a kare .
Wai ke Bintu harda yaya Imiran da ba,ruwan shi da kowa, amma sai k8n tsula mashi halinki na tsiya?
Maryam tace a,a anty Amira tunda kikaga haka akwai dai koni ranan mun dawo school bakiji, abinda yake fadawa Bintu bane,
Nace aini Anty Amira idan mutum bai shiga gonata ba ni bani shiga nashi don haka kibarni kawai dashi dan iska kawai.
Haba Bintu haka,kawai ki dinga zagan muna dan uwa a gaban mu haka gaskiya zamu saka wando kafa guda dake a gidan nan.
Nace maida yukanki kube anty Amira ai ni ba haka nake ba da ace da yai min ban dauki mataki ba,ai da ko yanzu bata kare muna,ba,wallahi.
Ke dai yanzu kin zama disturb wallah kamar ba Bintu Maji ba wallahi nace lokaci ne idan baka baki sai a shaka a,banza.
Wai don Allah may ya,hadaki da yaya Imirana kodai laifin maganan ranan ne har yanzu kike kule dashi.
Nace a,a ai anan cikin asibitin muka yi case din mu dashi ban ma,san yaya sadauki na gurin ba,sai da naji ya daka mai tsawa yace mai ya sake min hannu na.
Tace ashe kin kuru, ne harda yaya,sadauki a gurin lalaima Bintu kinyi nisa sosai wallahi.
Nace marin shi fa kawai nayi saudaya shine wani abu wallahi har yanzu a kule nake dashi a raina .
Da sauri sukace mari da,gaske mari Bintu nace don ma banda karfi aida abinda zan mai sai yafi mari wallahi.
Yadda yake dan iska haka yake ganin kowa dan iskane shine harda daukan kazamin hannun shi wai zai shafa min jiki niko nakai mai mari sosai Allah yaban sa,a na samay shi da kyau.
Da sauri Amira tace don Allah da gaske marin shi kikayi nace wallahi Allah kuwa nan na,basu labarin abinda ya faru a tsakanin mu dashi har takai na mare shi.
Maryam tace dan iskan mutum kawai mara mutunci yau da wani ne da uwar shi ta samu abin kasawa a,ture tana baradawa a gari.
"Dan kowa ,dan banza ne, nata ne diyan kwarai a duniya, nace wallahi ni ko gobe yai min maganan iskanci sai na,dauki mataki ko a gaban waye.
Maryam tace ya ganki haka ya zaci irin yan matan shi da ya saba yaudara ne.
Nace shi dai jarabar shi ce ta motsa kawai har idon shi ya rufe, irin yan iskan ga ai su kowa bi suke basu da zabi mace da mai aure da mara aure in sun, samu, duk so sukeyi.
Nace Allah ya kyauta Allah dai ya,shirye mu, don wanan shima ba karamin masifa bane wallahi.
Don ai zina ya mafi komai muni a rayuwan mutum da ban kyama, ga al,umma.
Nifa ban yarda da maza don a mayaudara nake daukan su baki daya inji Amira nace ai ba duka maza bane basu da hali don ko matan ma,akwai marasa hali a cikin su sosai don sai kiga diya,mace yanzun tana abinda wani da namijin ma ba,zaiyi ba.
Har Baba yafito shi da su sadauki suka rakashi nan muka mike a inda muke zaune muna mashi a huta lafiya.
Sadauki dake tsaye ya bude motan ya dago kai ya kalli gurin da mu ke tsaye, yai muna inkiya da dakin da,maji ke ciki .
Nan take, na juya da sauri na nufi dakin suko sauran basu gane may yake nufi ba don haka suka tsaya jiran baba dake waya ya gama.
Ina shiga daki nasamu, maji ta farka daga barcin da ya dauke ta, na karasa gurin, da take ina mata ya jikin
Tace min ina yayan ku Fatima ya tafine ko yana cikin asibitin nace to na dai barsu waje da Baba zai tafi gida .
Kamar kira sai gashi ya turo kofan ganina tsaye a,bayan mama ina gyara mata filo yasa shi karasowa gurin da sauri yana cewa Maji kin falka,ashe ya jikin yanzu da sauki dai yanzu ko?
Likita ya shigo ganin ta a,zaune yake tambayan ta mama ya jikin naki da sauki ko
Ya dan dubata ya dago yana cewa abata abinci taci zuwa shidda na yamma za,azo ai mata allura.
Sadauki yace wani iri abinci ya kamata a,bata yanzu wanda zaifi mata, amfani.
Likita ya dago kai yana fadin tea mai kauri da fruit sai kuma anta da koda mai kyau ta dinga ci.
Sai kuma likitan yai shiru tare da kurama sadauki ido yace you look like U,F footballer yace cikin dakewa yes iam d one,
Nan suka fara shocking din hannun su suna gaisawa mutun yana faman dada wasan yaya,sadauki.
Likita baifi yan mintina da fita ba sai ga,wasu group din likitoci sun shigo lokacin yana gyarawa mahaifiyar shi kwanciya suke fadin lalai kuwa shine shine.
Nan suka cika dakin da surutu wa yannan group su shigo su fita wasu su shigo har abin ya fara isa ta don sun hana mama samun hutu.
Saida dare Baba ya,dawo tare da su Umma da mama Asiya ya,taso su gaba bayan ya gama masu fitina rashin zuwa duba yar uwar su dake kwance asibiti.
Inda yace na,tabbatar wallahi da dayan kune a,asibiti da maijidda sai inda karfin ta ya kare.
Nan dai yai masu tas yasa fito su zo tare su duba lafiyan ta .
Sun kai wani lokaci sai, suka mike zuwa gida, dama duk a matse suke kamar dole suka zo gaida ita.
Suna fita Mama tana kwance na mike na gyara ko ina tas a dakin tare da,kawar da,wasu kaya dake waje.
Sai ga,Sadauki ya,shigo dakin ya,aje ledan da ya,shigo dasu gurin flask ya nufa ya tsiyaya ruwan zafi tare da hada tea mai kauri sosai.
Yazo gabana ina zaune yake cewa gashi na,dube shi nace tasha tea ai kafin ta kwanta.
Fuskan shi a daure yake cewa ke zaki sha ba Maji ba, ya kara miko min yace karbi mana kisha idan kin gama ga nama a leda kici tunda wa yan nan sun tafi gida don lalaci.
Zanyi magana yace min shishsh bana son magana shaye shi kawai
Ban san ya akayi na fara kurban shayin ba saida naji na dan kai cup a bakina karo na farko.
Yace yaushe, likitan yace za,a kara mata allura ne wanda ya saura ai mata.
Nace ni ban ma tsaya tambayan shi ba,don ya ishi mutane da labarin kwallo kawai ya fita.
Ke kuma shine baki so zancen kwallo ko don kina jin haushi da hassada ko?
A kwallo ne mutum zaiyi bakin ciki ko kan may aiki wahala.
Kallona yake galala,har na, mike tsaye tare da dauko baredin na zauna a makure nasha ya dan kai kurbi hudu batare da bread ba.
Na aje tare da son na,rufe sauran sai yake cewa to ki jawo kazan kici don cikin ki ya kara,walwalewa da kyau.
Nace wanan ma,Alhamdullahi don nakoshi tace shiyasa bakya kiba har yanzu kamar a kallaki saboda baki son cin abinci.
Ya mike yaje bakin gadon mama ya dan tsaya can yake cewa ina ga shidda na safe zasuyi mata allura don gaka idan basu zo ba sai ki bisu.
Nace mashi tau ya kai kofa yake cewa idan ta farka kice mata na tafi sai da safe in Allah ya kaimu.
Yana fita naja kofan na rufe nan na, dako ledan naman na fara ci tare da karasa shan cup din tea dina.
Sai da nai nak na ture dama duk iya,shegena,a gaban mutane ne ban ita cin abinci saboda kawaicin da nakeyi kawai.
Zuwa dare maji ta,farka nan na mike ina mata sannu tare da tambayanta ko tana son cin wani abu.
Tace a,a tana tambayana su Amira nace yau a gida zasu kwana don likita yace mu dan rage yawa don ki samu hutu.
Tace hmmm kai Fatima boye su kuma,zakiyi bayan nasan halin abina sun dai tafi gida don su samu barci yau ko?
Banyi magana ba sai hira take min mai kama da nasiha tana ta bani labaran tun kafin nazo gidan su irin yadda su ke kwasa da kishiyoyin ta.
Nace mama Allah ya kyauta amma mutane kamar ba,a mutuwa sai a manta da ranan haduwa da Allah.
Sai kusan asuba,muka,samu barci sosai Allah ya taimaka na,farka da akazo yiwa mama Alluran karshe.
Ban koma barci ba na dauro alwala nahau sallaya na fara sallah har akai sallah asuba ina gurin a zaune abina.
Zaune nake inajan tasbi amma kuma zuciyata tana tunane akan hiran mu da maji daren jiya da irin wahalan da tasha a gidan miji amma tazauna tai hakkuri don yaranta.
Gashi kuma yau an wayi gari saboda dan tilon danta guda ciwo nason shigan ta.
Har na,soma gyangyadi a gurin sai jin muryan mutum nayi a akaina yana fadin ki kwanta mana ki dan huta hakana.
Yaya sadauki ne yana saye da kayan exercise na maza dogon wando da rigan shi mai dogon hannu dark blue.
Yanufi gadon mama yana duban ta sai ya juyo inda nake ina kallon su yake cewa, tasha maganin an kuma yi mata alluran kuwa?
Nace eh sunzo sunyi mata sun bata magani shiyasa mata ke barci haka don maganin barci yake sa mutum sosai.
Ya ce ba tare da ya juya ba ina ga daga wanan allura ya kare sai dai magani kawai.
Jin nai shiru yasa shi juyawa gyangyadi nake nai barci a gurin hakan ya nuna mai ina son hutu nima.
Kujera yaja zuwa gaban gadon mama yana mai kura mata ido cikin jin tausayin ta ta ramay tai baki duk ta canza kaman ta.
Yana nan zaune har wata nurse tashigo dakin take tayar da,maji zasu bata maganin safe. Shine dalilin farkawan mu ni da mama din
Sai da nurse din tagama ta tafine maji take tambayan dan nata sai yanzu yazo ne.
Yai murmushi yace maji na,tsaye nazo maki da,budurwana ta gaida ke sai na samu bata shirya ba .
Murmushi naji uwar tayi tana cewa kai kama isa kaida akaiwa mata tun kana karami kasan dai Alhaji ba zai canza maganan shi ba.
Sai yace wai wa kike nufi Maji Rahaman Baba Sani ko wa wai?
Tace itace mana ba itace matar taka ba da iyayyenku suka yima ko kw canza watace.
Yace maji ni may zanyi da Rahama yanzu ga mata yan gayu ko ina suna kawo min hari sai wace na zaba.
Dariya uwar tayi tace adaiyi sanni kada ruwan ido yai ma mutum yawa amma dai kasan zancen Rahama ba,tashi yayi ba har yanzu.
Wai maji da gaske kuke zancen Rahama har yanzu a da dawasa ne bayan ko wani shekara sai na hada toshin sallah ankai mata.
Kwanaki ma naji Alhaji na zancen yakamata wai kuyi aure ku uku tundai kai da kudi yake shigowa yanzu ko yaushe.
Yace ni gaskiya da za a bani zabi gaskiya Rahama batai min ba tayi min local da yawa gaskiya.
Murmushi uwar tayi tace kai har kana da zabi bayan ka bata tsallen ka ko?
Kuma Rahama yar uwarka ce ta jini zata zauna dakai tayi hakkuri ba,ajiku ba akan baren da kake son daukowa kan ka.
Nace ko kuma waye Rahama cikin yan uwasu oho koma wacece idan lokaci yayi ai mu ganta.
Banji ya kara magana ba sai ma motsin da yaji nayi yasa shi tuna cewa ina dakin lokacin nan ya dakai kallon shi gareni, nikan na kawar da kaina gefe ina cewa kaidai ka,sani.
Na kara hada kaina na da bango ina mai lumshe idanuwana ni adole ga mai jin barci.
A ranshi yace muna fuka kawai kamar bata jin may ake fadi wai tana gyangyadi.
Idona a rufe amma tunanen wacece Rahama ya hanani sukuni wanda ban san dalilin yin hakan ba gareni.
Tun ina barcin karya har na gaskiyan yazo ya kamani ban farka ba sai kusan karfe daya da wani abuna rana.
Duk ko da hayaniyar masu shigo gaida mama a lokacin nikan sai faman barcina nakeyi hankali kwance.
Dana farka sai naga Baba ne zaune a dakin yana ba mama abinci da hannun shi.
Naso na sulale na fita amma sai hakan baiyi ba don suna jin motsina baba ya juyo yana cewa a,a Fatima kin tashi sannu kinji.
Jeki wanke fuska kizo ki karya kinji sannu da kokari jiya mamanki tace ta hanaki barci ko?
Nai murmushi nace Baba ina kwana ya gajiyan tafiya yace Fatima aikece dagajiya ke mai jinya.
Bandakin dake dakin na shiga na,wanke fuskana tare da dauro alwala don lokacin sallah ya kusa.
Ina fitowa Baba yace oya maza zoki debi abinci ki zauna kici don mamaki tace baki son cin abinci.
Inbanda abinki Fatima ana jinya ba acin abinci ai sai ciwo ya kamaki ke ma.
Na dai daure na dan dibi kadan a plate Baba yace wanan abin fa kamar za,aba yaro dan goye kin dai ga ko ita mai jinyan taci abinci yau sosai.
Alaman sauki ya samu ke nan don haka kara kici kema kada ciwo yakama,min yar amana na.
Sallama akayi dakin gwagona ce tashigo tare da sadauki daya dauko ta daga gida don bata san guri ba.
Nan suka fara gaisuwa da Alhaji tana tambayan shi ya maijikin da kuma yadda ta kara ji.
Baba yace, ai hjy masa yar ki zamanta a gurin mu yai amfani nan ya shiga yaba kokarin da nake masu a gidan.
Gwago tace ai Bintu yatinyace maihankali saidai kuma gata abin tausayi don rashin jin dadin rayuwan da ta tashi ciki.
Sadauki yashigo dakin rugumay da wasu kayan bukatun da yasayo amma gwago sai faman ba su Alhaji labarin rayuwana da irin wahalan danasha a gurin uwar riko na har yakai Baba na da kan shi yace azo dani birni wurinta ko zan samu sassauci a rayuwana.
Mamakin gwagona dake ta zuba yake ta zage sai faman yabon wanan yar nata mara kunya take haka a gaban mutane.
Nan dai yake tambayan maji ya jikin nata shine ya katse gwagona yake cewa ko likitan ya shigo da rana dubani idan baizo ba sai ya shiga gurin su.
Mama tace ai shigowan shi biyu yau yana tambayan ka nace ka tafi gida.
Ya mike yana fadin bari na duba ko yana office din shi inda ya mike zuwa wurin likitan.
Ya samu likita a office din shi bayan sun gaisa yake fada mashi yadda maji ta samu sauki fiye da yadda suke tsanmani yace kuma gaskiya wanan yarinyar tana kokari sosai wallahi.
Yace a ran shi kai may yasa wanan manyar yarinyar kowa dai yabonta yake ne haka yar kauye kawai.
Ya daiji dadin yadda likita tabashi bayanin kan mahaifiyar shi. Don ko ba komai yanzu hankalin shi ya dan kwanta ai.
Ya