Showing 330001 words to 333000 words out of 373688 words
Chapter 111 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
ba sai da take ce min wai may kike tunane ne haka Fatima ?
Na lumshe idanuwana nai murmushi tare da sauke ajiyan zuciya nace wallahi ba komai anty tace ba komai kike zurfin tunane haka.
Nace maryam yaya ya fara min zancen haihuwa fa tace to may ye abin damuwan kai ciki.
Ya baki mana yagani in baki dauka ba wayasani ko lefin shine banaki ba kadama ki damu kan ki da wanan har yaushe akai auren da za,a fara wanan magana haka.
Ba kowa ya zuga shi ba nasan Nafisa ce tun ranan naji tana ce mai wai ita yanzun baby din shi kawai take jira suzo don ita sune yaran ta.
Kuma nasan tana fada mai hakane kawai don ya maryar da hankalin shi ga zancen.
Idan ma yai maki magana kice mashi yabaki aiba kece zakiba kanki bako ?
Maganan ta yai min dadi sai da na shirya mata komai sanan na kirashi yazo ya dauke ni tace na dauki duk abinda nake so daga cikin abinda ta samu.
Dariya nayi nace haba dai anty aiko da ban gode ma Allah ba yanzun haka fa ina da turamay sunkai ashirin da ban dinka ba aje.
Tace kaji masuyi don jallah inda nice ai ban iya ganin turumi ban din ka ba tace da tuni nagama dasu.
Na dan bata rai nace kin san halin yaya shifa yafi son ko yaushe ya sayo min dogayen riguna irin na kasashe da yake zuwa kuma yafin yaga na sasu.
Tace kuma wallahi suna maki matukar kyau ko dazun naji wasu na gulman ki ai wai duk shigan da kikayi kamar kece kika halicci kanki.
Nace kai kaji mutane da gulma kuma ina ruwan su dani tace wallahi Fatima kin dace da Allah yasa yaya yazama mijin ki da bakece matar shi ba da sai dai muyi taganin abu a gidan wasu.
Allah yana da hikima da basira kila dalilin hakane ya jefo rayuwan ki a cikin mu fa?
Nai murmushi nace sanin gaibu sai lillahi anty amma gaskiya yaya baida matsalan komai inba wanan shan ba kuma yanzu sai nake gani kamar yama daina yi.
Mun ware turame wasu umma da Inna harda iyyya Rabi saida maryam tace aba turmi daga ciki da kannen mijinta su sahura su biyu.
Sai goma yazo ya dauke ni muka bar gida zuwa namu gidan kowan mu har iya duk mun gaji a lokacin.
Wanka mukayi don kowa a koshe yake sai kwanciya ba school yasa na kwanta washe gari bamu fito ba sai after eleven muka fito daga daki kowa agajiye yake.
Nan muke falo ranan bai fita zuwa ko ina ba sai dai wayan da yake ta faman bugawa kawai.
****** ********* ******
Ranan bayan suna da kamar sati biyu wanda bai zaunu ba don ginan sabon site din su da akeyi ya mayar da hankali sosai ga aiki.
Ya dawo da la,asar don ya huta yace yabajin kan shi na mashi balain sarawa a lokacin.
Sai wayan shi yai kara Baba sani naji yace yadauka suka gaisa dashi baba din ke fadin yana son ganin shi da dare anjima ya amsa da to Baba ina nan zuwa insha Allahu.
Magani na kawo mashi cikin wani dan karamin plate da ruwa a cup ya hadiye maganin.
Can naji yaja tsuki yana fadin ko kuma yau mai baba Sani ya samu yake nemana a gidan shi.
Mutumin da abaya ya tsane ni kamar may ko gidan shi cewa yayi bai son yana gani na,shida baba Shaibu ni tun lokacin suka fita raina wallahi.
Zancen auren Raiya ne ma da baba ya matsa lokacin sai anyi yasa nake dan zuwa kada ran shi yabaci idan yaji banzuwa.
Amma haka idan naje kiranta zasu yi tamin wullakanci yara da samarin gidan suna cewa ga dan wiwi din nan yazo.
Na dan yi murmushi don nasan cikin bacin rai yake magana nace ba babanka bane yaya duk abinda sukayi ai don kan su wallahi.
Kadai je kaji may yake neman ka dashi yafi kada yace kuma yakiraka kaki zuwa kiran nashi.
Yace ai zan tafi naji may yake nemana dashi kuma ne wai kwanaki fa da haihuwan na na maryam sai da maji tasani gaba na basu yan kudade duk kan su har gwagwanin mu.
Nace Allah ya saka da,alheri ai duk yiwa kaine hakan ma.
Sai da yai sallah ishai ya shirya cikin wani shadda mai ruwan maku dinkin garen hannu haka ma rigar iya cinya akayi mai shi, ya nufi gidan baba sani ban kawo komai ba tun da kanin mahaifin shi ne.
Yana isa ya buga waya yace gashi kofan gida ya iso baba yace ya iso mana yashigo yana falo zaune.
Yasamay shi zaune tare da matar shi ya gama cin abinci suka gaisa duk cikin kyankyamin yadda falon ya koma yake.
Ya tambaye shi harko ki shi da matar shi yace duk Alhamdullahi.
Can baba yace dama ba wani abu bane yasa na kira sai akan zancen ka da yar uwar ka Raiya ne naga gara kawai ace anyi abin nan tunda dai ita ba wai auren tayi ta kuma gama karatun ta bana.
Dama dai can kuna son junan ku dan matsalane aka samu na munafunci ya shiga tsakani.
Ba karamin mamaki Sadauki yaji ba yadda baba yau ya murje idon shi ya iya mai wanan magana.
Ya manta yadda yaci wa mahaufin shi fuska yana kirarin wai zai bawa yar shi mashayi dan wiwi dan giya.
Ya kuma tuna Irin halin da maji tashiga a lokacin irin cin fuskan da akayi mashi kan wanan auren hadin da akaso yi bayan tun Raiya tana karama duk sallah sai ankai mata kayan toshi.
Itama kanta Raiya din sai da taci mai fuska daya buga mata waya lokacin da yaji labarin sai ce mashi tayi.
In aure ka in kaika ina kama big girl ace na tsaya auren wani mashayi wanda baida aikin yi sai shaye shayen tsiya kada ka kara kirana daga yau na fada maka .
Yana tuno haka ya dago kai yai murmushi yacd Baba naji abinda kace amma na farko kasan nayi aure ko.
Nabiyu kuma ita Raiya fa ta bude bakinta tace min bata sona bata kaunana idan na haihu cikin maji kada na kara kiranta.
Don haka Baba don Allah abar zancen da yawuce yawuce kawai Allah ya bata mafi alheri a gareta ni yayan ta har gobe najini zanyi duk wani abinda duk wani yaya yakewa kaunar shi.
Mama suwaiba tace haba Umar ai kasan halin yarinta har nawa Raiya take hakkuri zakayi tunda kuna son juna.
Yamike yana cewa gaskiya Baba abar wanan zancen ba zai yuyu ba tun da tun farko an fara shi da tsegumi masuyi kuma ba fasawa sukayi ba.
Baba yace dakai da Raiya duk daya kuke a gare ni don haka ina da ikon yin komai akan ku murmushi kawai yai masu yace shi zai koma ayi hakkuri.
Raiya da yan uwan ta suna labe sunajin yadda akayi sukace kingani kin wa kanki tace aiko yaki ko yaso sai na shiga gidan nan wallahi koda tsiya ne.
Jifa irin kafirar motar da ranan mukaga matar shi naja dayan tace kice dai ta koma kamar diyar wani presedent da ita.
Dan iska kudi yake samu har na tsiya wallahi ba ance albashin su ma,wai yafi na wasu gwaunoni ba kudi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YABI MUNA HAKKIN MU AKAN KI
Tukin mota yake yana tunanen wanan hali na Baba sani wanda ya rasa gane kan shi.
Son kaine ko kuwa rashin tunanen may yadace ne don yai matukar jin wanan magana daga bakin Baba Sani din.
Ko da ya iso gida ya samu har nayi barci ko shima sai da ya gama duk abinda zaiyi ya hawo gadon ya kwanta.
Inda nake kwance ina barci ne ya kalla kamar ya tayar dani sai kuma ya fasa ya dan kura min ido yana kallon yadda nake barcina a tsanake.
Tausayi yaji na bashi yasan dani da iyayyena sun mai komai yadda suka dauke ni suka bashi .
Bayan nashi jinin sun kyamace shi sun ki shi saboda halaiyan shi da sukace baida kyau.
Amma kuma shine yau kuma da ake ganin kamar ya zama wani abin kwarai zasu dawo suce wai dashi zasuyi.
Kai wai mutanen duniya ne suka lalace koko duniyan ce ta lalace haka da kan ta.
Yanzu shi Baba Sani har ya manta da cin fuskan da sukaiwa mahaifin shi shi da matar shi ne da zasu dawo suce shi ne kuma suke son ya auri yar su ko may ?
Da kyat dai ya samu har barci ya dauke shi yana cikin tunanen irin halin Baba sani da wasu mutanen da basu san kunya ba.
Da safe koda muka tashi ganin shi nayi kamar wanda baijin dadi don yau ko fita judging bai samu yi ba na safe.
Har nai wanka na shirya nafito naji shi shiru a daki na nufi dakin nashi na leka shi.
Yana kwance a saman gadon shi ya kifa cikin shi alaman motsin da naga yanayine yasa na gane ba barci yakeyi ba a lokacin.
Na nufi bakin gadon nashi ina fadin ina kwana yaya love?
Sai lokacin ya dan dago kai ya juyo gare ni har na kawo bakin gadon na dan zauna daga gefe tare da tokaro hannu na daya ta baya saman katifa na sa shi a tsakiya.
Yace yaya dare naga jiya kin samu barci sosai baki ma san dawowa na ba.
Murmushi nayi tare da dan dukar da kaina daidai saitin fuskan shi nace nima wallahi ban san yadda akayi har nai barci ba haka da wuri daga fa wai na dan jiraka kadawo shine barci mai nauyi ya dauke ni hakana.
Nace tashi kai wanka ka karya yaya yace ki tayar dani to duk banjin dadin jikin nan nawa yau.
Da sauri nace subbahanallahi yaya may ya samay ka kuma maimakon yabani amsa sai ya jawoni zuwa jikin shi yana sauke numfashi a hankali.
Can naji yace Fatima na amsa na,am yaya yace tunda kun samu hutu sai ki shirya nakai ki kiga su mama duk da ba haka naso mu tafi masu ba don akwai dan planing din da nake son yi a kan su.
Wani irin sanyi naji ya sauka min a raina ina fatan zaki je ki dawo batare da wani matsala ba dai.
Nai maza nace mashi matsalan may kuma yaya bayan gida na tafi gurin su mama.
Yace to fada min inji da kanki kwana nawa zakiyi a can idan kin tafi don inji ko kina da adalci .
Shiru nayi ina nazari nace nace ko nace sati uku don na samu na zagaye dangi da yan uwa da abokan arziki.
Sai kuma nai tunane ko a gidan baza su amince min nan da Rabah nai wanan kwanakin ba haka.
Amma a fili cewa nayi ko kwana nawa kace nayi ai zanyi ne na dawo , yadan shafo fuskana da hannun shi yace.
Ai ni nace ki fada don idan kin wuce nima zan tafi ghana ne akwai kayana da suka makale a can nake son zuwa na duba su.
Don haka ki fada naji sai dai kada ki manta duk hukuncin da zakiyi a tsakani na dake na rokeki kar ki so kanki a kaina da yawa kiyi tsakani da Allah.
Dariya maganan shi tabani don yasan na dade ina binshi kan ina son zuwa gida na duba su Baba amma ya hanani zuwa.
Yace No na san kin sani bayau ba kike min zancen zuwa gida ina basar dake kada yanzu kiji nace ki zaba kimin rashin adalci.
Kin san dai ina son ki Fatima kuma ko ban furta maki ba ke kin sani don kinga alama yafi a kirga.
Don haka ina kara jaddada maki ina matukar sonki a rayuwana Fatima fiye da duk yadda zaki tsammani gaba daya fatana da buri na shine bai wuce na nuna maki ba a kullun irin halarcin da kikai min ba.
Nace yau kuma duk may ya kawo hakan ne don zancen tafiya gidan ne ko dai baka da sha,awan ina raban iyayyena ne yaya ?
Yayi murmushi yace haba haba subbahanallahi ko daya wallahi bandai son kiyi nisa danine ko kadan yanzu Fatima.
Nace to nayi sati daya idan na tafi ko ?
Naji yayi murmushi tare da dago kai ya kalleni yace har sati Fatima sati daya fa kika ce.?
Nace a hankali to ka rage yaya idan yayi yawa ne, yace zaki iya yin kwana biyar ko nasan zai ishe ki kiyi duk abinda kike sonnyi can.
Nace to na gode yaya nagode yaji dadin hakan yana mikewa zaune na gyara mashi ya zauna da kyau.
Yace sai ki fara shiri don ni na gama maki shirin tafiya ko gobe insha Allahu zan kaiku ke da musa idan kuma iyya Rabi tana son tabiki ne sai ku tafi tare idan bazata ba sai ta tafi gida har ki dawo a rufe gidan.
Murna da dadin jin gobe zan tafi gida duk ya cika min zuciyata ina matukar kewan mahaifiya ta dana dade ban gan ta ba ya cikani.
Yace ni in nai wanka zan fita zuwa gida sai na fadawa mamanki zaki gida gobe goben idan mun shirya zamu wuce sai na biya dake ki sallamayta.
Nace nagode nagode yaya ya mike yana kokarin shiga bathroom don yai wanka.
Na juya zuwa dakina sai ma dadi ya kasa barina nasan may zanyi akai lokacin.
Wardrobe dina na bude tare da jawo troler dina na fara zaban kaysn da zan tafi dasu.
Idona yakai ga kan atamfofina da suke ajere ban faye amfani dasu ba nan nashiga zabo masu saukin dinkin da nasan mamana zata iya sawa na tara a gefe na.
Wanda nai yan matanci dasu kuma na jawo wani ghana most go na loda a aciki inkai a rabawa mutane shi.
Inda turamay suke na bude akwatin na fitar da wasu masu kyau suma na tara guri daya.
Ina tsaka ga aikin ne ya shigo dakin tare da bin kayan da kallo yace duk wa yan nan kayan fa haka ?
Ba dai duk na tafiyan bane sai nai mashi bayanin manufa ta dasu yai yar murmushi ya karaso inda nake a zaune saman godo yace No bazaki kai wa maman mu tsofin kaya ba Fatima ki bari a sayo mata nata kawai da zaki mata dasu idan nafita ban mashi musu ba sai nuna farin cikina da nayi.
Da zai fita ne yake cewa sai kiwa Iyya magana muji ko may ye ra,ayin ta ita kuma ga tafiyan.
Nace ok yanzu zan fita naje gurin ta naji yadda za,ayi akai.
Yana fita na samu iya a kitchen nake fada mata yadda mukayi da yaya din da kuma tambayanta may ta yake shawara akai.
Tace haba uwar daki na idan ma na zauna a garin may zanyi ai kafarki kafata tare zamu tafi dake nace Iyya na gode da wanan karamcin da kikai min.
Itama nan ta fara shirin tafiya na bata atafofi guda uku masu kyau tana ta godiya da jin dadi.
Tunda yaya ya fita gidan da safe bai dawo ba nima a cikin zumudi na wuni.
Ya shiga gidan su ya gaida mutanen gidan yadawo gurin mama suka gaisa da ita.
Yace bayan sunyi dan shiru gobe ne nake son Fatima ta tafi gida ta duba su insha Allahu.
Cikin mamaki mama tace gobe goben nan dai shine bamu da labari kan tafiyan sai yanzu zamu ji may kake so na hada mata na zuwa gida a matsayinta na karon farko kenan da zata ganin su.
Yace nima jiya ne naji ya kamata su tafidon dan hutun da suka samu din nan sai taje ta gan su ai ba dadewa zatayi ba,kwana biyar zasuyi ta dawo.
Baka dai kyauta min ba kama yayi naji da,wuri na dan hada mata tsaraba taje dashi mana.
Yace ai babu komai maji za,ayi abinda ya dace ayi kafin su wuce din nima zanyi tafiya zuwa ghana inshs Allahu.
Sai dan shiru bayan tai mai adduan Allah yakai lafiya a dawo lafiya da tace mai.
Lafiya kake kuwa yai dan murmushi yace lafiya nake maji tace naga kamar kana da damuwa a ranka yace ba komai maji.
Can yace Baba Sani bai zo gidan nan ba gurin Baba ?
May kuma ya faru mama ta tambaye shi da sauri yace jiya ya kirani da dare naje gidan shi.
Shine yafito min da zancen wai yana son a tayar da zancen aure na da Rahama.
Da sauri mama tace ba zai yuyu ba wallahi ko alama.
Shi yanzu baiji kunya ba da har zai fito maka da wanan zancen yanzu don yaga Allah ya mayar da kai mutum ko ?
May yasa mutane basu da ta idone wai haka ?
Idan ma kai ka yarda ni wallahi ban yarda ba da wanan zancen ko alama hakan ma ai tatsuniya ne.
Yanzu ko da yaga Allah ya daukaka shine har ya manta da irin cin mutuncin