Showing 111001 words to 114000 words out of 373688 words
Chapter 38 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
din Maji hankali a tashe daidai duk su kuma sunyo waje inda Nafisa take tsaye da maryam.
Maji tana fadin ke Inna Isa kyale ta haka na barta taitayi ita kadai.
Daga nesa Umma ke fadin wallahi idan kuka kara dukan ta yau sai dai duk akai mu asibiti gidan nan .
Kaji man marasa mutunci haukan ashe ba,a kan sadauki kawai ya tsaya du, dukan ku kenan ya shafa.
Ke Nafisa may yakawo ki gurin wa yan nan matsiya ta ki jawa kanki tsiyan su irin ta gado ya shafe ki ke ma.
Nan take fadawa uwarta duk abinda yafaru uwar take cewa barsu tsiyane da talauci yai masu katutu a kai shine bakin cikin su gare ki.
Hassada ko sai dai su mutu dashi a gidan nan don babu mai kama kafar mu don mun riga mun masu nisa ko.
A haka zasu kare daki tsiya tsiya kamar madallacin malam ba komai sai tarin raggaduda kawai ciki.
Saurayi kuma sai sun ga har dan gidan gwauna a gidan nan gurin ku.
Sai lokacin sadauki dake tsaye daga kofa shigowa gidan tun farkon fitina yana tsaye yana sauraren su.
Ran shi yai matukar baci irin yadda yake jin ana zagin mahaifiyar shi da yan uwan shi a kan talauci.
Su madai su Amira duk da Maji tana masu fada bai sa sun fasa mayar masu da amsan zagin da suke masu ba don harda mama Asiya ta shige tsagal cikin fitinan tana cewa ai wanan mutanen kune baku san sherin su ba dama da kowa bakin ciki sukeyi a gidan nan.
Ke Amira shige daga ciki kada na kara jin muryan kowan ku yai tsaye yana nuna masu kofan dakin su da hannun shi.
Ranshi a bace idanuwan shi sun kada saura kiris ya fashe irin yadda ya hasala.
Yaran suka bi bayan uwar su da tafara shiga ciki ranta a bace yayin da ya juya inda taron mutanen gidan suke tsaye ya watsa masu jajayen idanuwan shi akan su.
Zo mutafi kinji don wanan mahaukacin yanzu yana iya muna haukan shi akai.
Gaba daya suka watse zuwa shiyan su a can suka yada zangon su yana jin sunci gaba da fitinar su ya shiga dakin mahaifiyar tasu.
Tsawa yadaka wa su Amira akan suyi shiru hakana bai son hayaniya ya isa.
To amma yaya don kawai an raina mu shine kowa ya kwaso sharan shi a kan mu zai yaba tsiyar shi.
Nace ya isa haka ya fadi cikin tsawa hakan yasa gaba daya sukai shiru da maganan.
Nan yakai zaune saman dayan kujeran da ya saba zama idan yashigo gidan, maimakon ya zauna yadda ya saba sai kawai yayi kwance tare da dora hannun shi daya saman kan shi daya na saman kijin shi.
Ya kai wasu mintina a hakan gaba daya dakin ba wanda yai magana daga cikin su.
Bintu ce ta mike don shigewa don dai ita gaskiya zaman ta a dakin duk a tsorace take dashi.
Don gani take cewa kiris ya rage ya kamasu da dukan tsiya a dakin.
Takai gaf da kofan zata shiga taji yana cewa "Ke kawo min abinci na na fita.
Da,sauri ta juya zuwa kitchen inda ta hado mashi abinci kamar yadda ya saba hada mashi wanan karon har da spoon din da yace dashi yake ci.
Bai masu magana ba ya mike zaune kamar zai dauki abinci sai kuma ya bude a,nan falon ya fara ci a hankali.
Maji ki yace daidai zaikai spoon din shi a baki batare da ya kalleta ba kiwa yaran nan magana su daina shiga harkan mutanen gidan nan ana zagin ki a banza.
Don bazan iya hakkurin wanan mugun zagin da ake maki ba a gidan nan haka.
Talauci dai ba mune muka azawa kan mu ba Allah ne yayi mu a haka ba yin kan mu bane ai.
Amma mutanen nan da,sun tashi da,wanan zasu zage ki ke da yaran ki, don tun ina karami nake jin wanan kalman daga bakin mama da Umma a gidan nan.
Sai kuma ni da na ja maki wanan gorin na dan shaye shaye da kuma cacan da suka ce ina yi wai.
To amma ba komai Allah na gani shida ya dora min wanan lalurar shine zai yaya min shi dakan shi aduk lokaci da yaso.
Ke kuma Amira na roke ki da kuyi hakkuri da kowa a gidan nan don rayuwan mahaifiyar mu kin dai san ita ba mai son fitina bace a ranta.
Haka ke maryan wanan zuciyar taki matsayinki na mace ki rage shi don gidan wani zaki tafi.
Inda Bintu take zaune ya kalla tare da,watsa mata harara yace ke kuma da sauri Bintu ta dukar da kanta a kasa tare da mannewa jikin kujeran da Maji take zaune a kai.
Yace kada ki yarda naji ance kinjawa uwar mu bacin rai a kanki a gidan nan zaki hadu dani.
Sai lokacin Maji da takaici ya isa tai magana tace kai ku tsaya wasu,wasun ku amma kada ka hada da yar mutane da bataji batagani ba da kowa a gidan nan iyakarta imu a shiyan nan ba ruwan ta da kowa a gidan nan.
Inda na tsayar da ita anan take bata taba saka kanta ga harkan kowa ba cikin gidan nan.
Don haka tafita a ido ka kada kasa min "ya a cikin zancen ku wallahi kaji na fada maka gaskiya.
Mikewa yayi ya ce kun daiji abinda na fada maku kowa ta kiyayyeni akan hakan.
Barin dakin yayi kamar wanda aka tsakara baiko juya ba yafice abinshi har lokacin yana jin hargowan Umma daga part din su.
Zancen bai kare ba don da maigidan yadawo an samay shi da zancen yana ji yace a kira mashi su Amira da maryam tun kan hajiya Umma tafita daga gurin shi har Nafisa din.
Bayan kowar su tashigo tare da uwarta harda mama Asiya da yaranta yan mata, yana cin abincin shi hankali kwance ga hajiya kubura dake girki daga gefen shi suna zuba soyayyan su a cikin style.
Alhaji kaifa kace a kiramu kuma kabar mu a zaune kana harkan gaban ka inji mama Asiya da kishi ya kumay a lokacin na irin yadda yakeyi da mummy.
Mummy tace ke hjy Asiya ko so kike kuma yabar cin abincin ya tsaya shirmen kishin ku na kullun da baku san angirma ba har yara sun fara irin shi.
Kada ki fara ki fada min maganan banza wallahi yanzu a jimu a gidan nan don ke baki da kunya kowa so kike yabi ki kamar yadda kika mayar dashi a gurin ki.
Alhaji wanda yagama wanke hannun shi da hjy kubura ke zuba mashi ruwa yace ta mayar dawa wai ni ko wa ?
Shiru tayi don tasan idan ta tanka yanzu zai iya watse ta a gaban kowa babu ruwan shi da yara na gurin.
Gurin Amira ya juya yana cewa mamana yanzu Umman ku ke fada min wai kun taru kunwa Nafisa duka yau a gidan.
Sai kuma ya juya gurin Maji yana fadin ina bakuwar yar ki ita bata zo bane don nasan ba,a dukan Nafisa bata sa hannun ta ba.
Nafisa tai but tace wallahi danaci uban ta ko murmushi yayi tare da duban Umma yace kin dai ji tarbiyan ki ko ?
Yace wa yar mama Asiya karama hauwa kira min yarinyar dake dakin maijidda tazo da sauri yarinyar ta mike zuwa kiran Bintu.
Ta na shiga bako sallama Bintu da ke zaune hankali a tashe ta kurawa tv ido sai dai hankalin ta ba,a kallon yake ba sai ji tayi ance ke yar kauye baba na kiran ki.
Tare da watsa mata harara tana yatsune fuska tare da bin dakin da kallon wulakanci ta juya da sauri bintu ta jawo hijjab din ta dake gefe har kasa tasaka.
Tare da bin bayan yarinyar don bata masan falon baban ba duk zaman ta gidan da tayi ba ruwan ta da sanin komai.
Saida tajawo kofan dakin Maji da zata fito tasaka key tabar dakin da key din a hannun ta.
Inda taga hauwa ta shiga nan ta shiga itama tare da sallama dauke a bakin ta.
Maji da hjy kubura sai Alhajin ne suka karba mata sallaman ta da tayi tare da samun guri ta tsugun na ta sunkuyar da kanta kasa tana fadin.
Ina wuni Baba, cikin lada bi tare da sunkuyar da kanta a kasa, yace tare da nuna ta da hannu kun gani,
Sannan ya karba mata gaisuwan nata yace ku diba ke Asiya da kika samay ni kan maijjidda ta dauko bakuwar yarinya takawo min gida.
Kinga abinda tabi ta jawo ta a jikin ta tarbiya natsuwa da sanin ya kamata ga yar kauyen yar makwabtan da kika ce.
Hajiya kubura dake gefd tace kai Allah dai ya sawaka idan kuma anyi magana ace wai wani ke hassada.
Ke kubura wai may kike so ma dashi ne ki fada min don kin san daidai nake da ke wallahi.
Ai kaji maganan ke nan yanzu ku dakata da wanan bashi nakiraku yi ba anan ina son nasan may yakai har ke Amira kuka taru kuka daki Nafisa yau a gidan nan.
Anyi magana kuma uwar ku ta daure maku harda ita ta shiga zancen, ana haka kuma mahaukacin wanku shima ya shigo ya saya ya zama nashi.
Nafisa ta tare zancen dacewa baba bakin cikine fa kawai don sunga ana zuwa gurina su ba,a zuwa kiran su kamar sauran yan mata.
Alhaji yace a gidan har ake haka banda labari Nafisat ?
Allah ya kyauta kawai yace tare da girgiza kan shi cikin takaici yana kada kafan shi irin na magidantan da abu ya daurewa kai.
Yace ke tare da kallon inda Bintu take zaune yace mayye sunan ki ne ma ?
Tace a hankali Bintu Baba, yai yar murmushin manya yace Fatima bintu ke nan ko?
Eh Baba ta bashi amsa yace ki fada min abinda kika sani akan fadan da akayi a gidan nan yau.
Shiru Bintu tayi na dan lokaci kamar ba zatai magana ba sai kuma can tace.
Baba muna daki bayan anty Amira ta shigo gida nan tafara bashi labarin abinda ta sani da irin kalamin da kowa ya fadi har marin da Maryam taiwa Nafisat din.
Amma maryam wallahi kin kyauta min inji hjy Kubuta tare da kallon gurin da maryam take zaune.
Eh zaki fadi haka mana tunda ba yarki akaiwa hakan ba a gidan.
Hjy Umma ce uwargidan su mahaifiyar Nafisa ta ke fadin haka din cikin bacin rai.
Batare da Alhaji ya kalli gurin da take ba yace kubura ban son na kara jin bakin ki a zancen nan.
Daga haka yai shiru bai kara cewa komai ba kuma again, ya juya gurin Umma yace to kinji ke maimuna zagin uwarsu tayi har dakin ta kuma tana zaune babu kunya don kawai an bata mata rai akan saurayin ta da yazo kiranta ba,a fada mata ba.
Alhaji kada ka juya zancen nan fa dukan min ya akayi kuma shi nazo fada maka din ka dauki mataki a kai.
Yace wani mataki zan dauka idan kece su Amira suka shiga gidan kike sukai maki haka a gaban ki wani mataki yaran ki dake gurin zasu daukan masu ?.
Shiru Umma tayi yace ba amsa ke nan sunyi daidai dai din ke nan ko ?
Tace yanzu mai kake son nace tunda na fahinci ka daure masu gindi akan abinda sukayi sunyi daidai.
Yace kin taba gani mai kai takaka yayi nasara gurin maida magana balle harda cin mutuncin uwa a ciki.
Ai ko ke ne suka kawo wa takaka akai masu hakan iya matakin da,zan iya dauka ke nan a kan su kinji na fada maki.
Ke kuma Nafisa wani yaro ne yake zuwa gurin ki gidan nan ban sani ba har kike iya tsayawa kiwa yan uwanki cin muntunci akan shi don ya aiko kiranki ba,a fada maki ba ranki ya baci kibi yarki har daki kina zagin ta don samun guri.
Shiru Amira tayi tare da dukar da kanta cikin tsawa ya daka mata tsawa yana fadin badake nake ba nace dan gidan uban waye ke zuwa gurin ki gidan nan har kofan gida na ?
Sai ga Nafisa tana hawaye don daga ita har uwarta basu zaci abin zai juye masu haka ba a lokaci guda.
Yace tunda aure kike so ba karatu ba sai ki turo min yaron yazo ai maganan aure dashi.
Ya juya gurin hajiya Umma yace maimuna yanzun saboda Allah kin san yarinyar nan tana tara min samari a kofan gida haka shine baki fada min ba saboda Allah da girmanki ?
Idan da da dan wani dakin ne yake haka dafa a gurin ki zan fara jin wanan labarin.
Yanzun dai nafahinci ka juye maganan ya zama laifi akan mu, shike nan nida diyana bamu da shakat kan yan mayen diyanka a gidan nan.
Duk abinda sukayi shine daidai mu bamuyi daidai ba indai duk wa yan nan marasa mutincin yaran Hauwa ne ka daurewa gidin ai suje suyi tayi.
Ba sabon al,amari bane gasu nan daga dan maye sai yan iska data tara muna a gida.
Ta mike fuuu, ta fita daga dakin inda shima yabi ta da kallon takaici mama Asiya ma mikewa tayi tana fita tana fadin babu dai adalci yanzu a gidan nan.
A dakin mutun kuma ace wai shine bai da gaskiya don samun guri da daurin gindi kawai.
Ya juya inda yaran suke ya kara masu fada akan baya son ya kara jin fitina daga gare su ko ya batawa mai shi rai suka mike suka mike suka bi bayan uwayen su rai a bace su ma.
Suna ganin ba ai sharian gaskiya ba a gurin don sune da gaskiya amma mahaifin su ya danne masu gaskiyan.
Bintu ma ganin yaran sun mike yasa ta mikewa tabi bayan su amma sai taji muryan Baba yana cewa ke Fatima sai ta koma ta tsuguna don taji may zai ce mata din.
Yace ban son naji ance kin saka kanki a harkan cikin gidan nan kamar yadda ban taba samun labarin banza ba a kanki fon haka ki kiyayye kin ji .
Ta amsa da to Baba nagode ta mike tabar dakin duk tsoro ya cika mata zuciyar ta ta samu su Amira suna jiran ta takawo masu key din kofan su data rufe masu.
Hauwa kici gaba da hakkuri don ance dan kuka mai jawa uwarshi jifa yau duk yaran ki bugu daya ake masu akan danki daya daya samu matsala,
Don haka saikin toshe kunnuwan ki don babba da yaro dashi zai zage ku duk wanda ya tashi a magana gudu zai fake ya harbe ki dashi.
Sai kuma ya jijiga kan shi a cikin takaici da jin zafin sadauki a ran shi yace Allah ya kauyata.
Sai lokacin hjy kubura tai magana tace rashin dai tunane ne ga mutane ai wanan matsalar ta shafi kowa a gidan nan don ba nata bane ita kadai.
Amma hakkuri da addua bai bar komai ba Allah ya sauwaka ya kiyayye gaba kawai za,ace.
Maji ta mike tare da cewa nagode Alhaji ranta babu dadi yabita da kallon tausayi kawai.
Har takai kofa hjy kubura tace gobe dai ba aiki don Allah ki ara min yarki ta tayani gyaran daki na.
Ta juyo tana cewa wai Fatima Alla ya kai gobe ai ita yaro ba kiuya ne bata jin nauyin jikin ta ko kadan.
A daki ta samu su Amira suna dariya Bintu wai ta rufe kofa da zata, fita daga dakin.
Tace ba dole ba don ni abin wallahi yanzu tsoro yake bani ma mutane haka ba tsoron Allah.
****** ********* ******
Sadauki yana fita jin shi yake kamar yana taka kaya don bacin rai, duk wanda ya yanzu ya tashi zagi akan shi akewa uwar shi gori.
Ya madai godewa Allah da jiya bai sha komai da da yai niyar sha yasan da yau gorin da Maji zata sha akan shi Allah kadai yadan irin sa.
Gashi saida ya zuba kwayan a bakin shi sai yaji kamar ance ya furzo su waje duk ya zube su a kasa suka narke yana kallon su.
Har ya usa filin kwallo zuciyar shi sai faman sake sake take mai kan abinda zaiyi wanda zai sa Maji ta danji sanyi akan shi.
Amma ya rasa mafita akan haka, haka ya samu guri ya zauna ranan yana kallon masu kwallo kawai ya kasa tsinanawa kan shi komai a lokacin.
Sai faman kulawa da warwarewa yake shi kadai a ran shi abin duniya duk ya damay shi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
Tun bayan dawowan Raiha daga tafiya gaba daya bata son fita zuwa ko ina ko yaushe tana gida sai faman barci takeyi kamar wace tai wani aiki.
Gaba daya ta kashe wayan ta kuma ta hana kowa ganin ta tayi hakane don gujewa Nasir kawai.
Kusan sati biyu yana sintiri a kofan gidan su gashi tun dawowanta