Showing 243001 words to 246000 words out of 373688 words
Chapter 82 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
nada natsuwa da hakkuri.
Cikin farin ciki Baba yace ikon Allah haka abin yake gaskiya nai farin ciki yau dajin wanan labari don ni kaina na dade ina wanan tunanen a raina.
Sai gashi Allah ya karba min addua na a cikin sauki da dadin rai maganan tazo min .
Zanga sadauki din in mashi murnan wanan babban albishir din da kikai min.
Tafita ta barshi da dadin rai sai murna yake har ya kasa boye farin cikin shi a fili.
Washe gari Baba ya aika akira mashi sadauki anyi sa,a ya dawo daga exercises din safe da yake fita da zaran sun fito daga sallah.
Rigan jikin shi ya sauya, ya nufi falon mahaifin shi don amsa kiran shi da saurin shi don yasan ba kasafai Baba ke aikowa kiran shi ba.
Da sallama ya shiga falon ya samu Baba ya daga kofi zai kurba tea da yake sha.
Yana ganin dan nashi ya sauke kofin ya fasa kurbawa yana cewa sanda sadauki sandagagare.
Zo nan zonan ka zauna yau in gwada maka farincikina dana kwana inayi jiya.
Mamakin may baba yaji akanshi yakeyi don rabon da yaji wanan kirarin da baba kan mashi inyai abin jin dadi tun yana karamin yaron shi kafin ya fara shaye shayen su bata.
Yace matso mana Babaatsonan kusa dani naji albishir din Alheri a gurin uwar ka jiya da dare .
Tazo tana fada min kun shirya tsakanin ka da yarinyar nan Fatima zan iya cewa nafi kowa farin cikin wanan hadin naku don na dade ina maka fatan haka a raina don Fatima yarinyar arzikice a gareka duk wani namiji da yasan kan shi zai so ace ya mallaki wanan yarinyar a matsayin uwar yayan shi nan gaba.
Duk bayanin da baba keyi sadauki ji yake kaman an watsa mashi ruwan zafi tun daga saman shi har kan shi .
Yadaga kai ya fadawa Baba ba gaskiya bane wannan zancen, amma sai yaga farin cikin da mahaifin shi ke ciki yafi karfin ya musulta shi a lokacin.
Ya san da zaran yace zai fada mashi gaskiyan zancen shi bai san komai ba akai farin cikin rayuwan shi zai iya sayawa zuwa bacin rai ta zama mashi sana din tashin ciwon shi.
Wanan dalilin yasa yaja bakin shi yai shiru, yana karba irin adduan fatan Alherin da mahaufin nashi ke mashi akan zacen.
Sukai sallama ya mike gwiwan shi duk ya mutu da kyat yake iya daga kafan shi da yake takawa a kasa dakin shi ya nufa cikin wani yanayi na susucewa a lokaci daya.
Yana shiga ya fada kan katifan gadon shi yayi yayi a lokacin ya samu ko dan kuka yayi ko zai samu relief, amma abin ya faskara mai.
Wayan shi dake gefe ke ringing har yagaji ya katse don kan shi bai daga ba sai kuma ga kiran ya kara shigo mashi lokaci guda ya daga daniyar zagin mai damun shi.
Bashar ne ya daga wayan yana tsaki yace yaya akayine wai Bashar din yace yana kofan gida.
Yace shigo ina dakina yana shigo yanayin da yasamay shi a ciiki yabashi tsoro sosai.
Lafiya may ya samay ka haka kuma ?
Ya watso maahi wani harara yace ban sani ba mugu ai kana daga cikin munafukan dake son wargaza min rayuwana nasani ba yau ba.
Bashar na zama yace may kuma mukayi mi muna fukan da bamu son ganin farin cikin ka?
Maimakon ya bashi amsa sai ya juyar da kan shi kawai gefe daya bai kalleshi ba.
Wai may ke faruwa ne wai ka koma haka lokaci guda kaman wani tababe yakara tambayan shi mikewa yayi zaune daga kwanciyan da yake yana cewa.
Kana nufin baka san sherin da maji ta kulla min bane agidan nan wai ?
Innalillahi kana da hankali kuwa yau man ?
Maji ce kuma zata kulla ma sheri a rayuwanka ?
Wani kallo ya watsa mashi yace ba sheri banr may nene?
Murmushi Bashar din yayi yace don Allah may akayi ne wai ?
Yace kaaai wai maji ta fadawa Baba wai mun shirya tsakanina da wanan yarinyae mun amince zamuyi aure.
Wata yarinya ke nan kake nufi wai?
Wata yarinya kake damuna akan ta gidan nan ?
Yace kana nufin wai Bintu?
Yace ita mana.
Alhamdullahi Alhamdullahi kai wani hikima sai manya wallahi tanan maji tafito muna Allah mun gode ma.
Ya dago jajayen idon shi yana kallon Bashar dake ta kwada hamdalla haka cikin mamaki.
Yace wanan abinda maji ta kulla min da may yakama Bassh?
Maji tarasa wace zata lakaka min auren ta sai wanan solaman yarinyar da kwatakwata bata cikin tsarina.
O Lindan ce tsarin ka ke nan ko yar arniyan ka mai dan buje ko ?
Wani wawan nashi yakai ma bashar din ya kauce ma nashi ta hanyan ja baya.
Sadauki ya mike tsaye yace haba man may zanyi da wanan yarinyar ko maryam dina fa batakai shekaru ba a duniya wai itace za,ace na aura ?.
Ita Fatima ba mace kake kallon ta ba ke nan ko ?
Wallahi zakasha mamaki kace na fada ma dan hakin daka rai shike tsone maka ido watarana.
Kai may ya kawo kane ?
Yace manta yau zamu zamfara ne dakai ko kuwa?
Yace bazan tafi ba.
Dariya ya kama mashi yace kafara angwancin ke nan ko?
Zanci ubanka fa Bash wallahi idan ka kara bata min rai yanzu zan rufe daki dakai nai maka tsinanen dukan tsiya.
Bashar yace sai dai yanzu kuma ka rufe daki da Fatima amma bani ba Bashar ba ya juya yafara tafiya yace bari ma na shiga cikin nai ma maji godiyan wanan babban albishir din da kai min.
Da sauri sadauki ya jawo shi ta baya yave kada ka farashi wallahi har ta zaci ko nayi na,am ne da zancen har ina farin ciki da zancen ne.
Farin ciki kan ka kanayin shi komai dadewa zakace na fada maka ai.
Wallahi kada ka fara kaje gurin maji na fada maka, Bashar yace mai da yukan ka a kube kamanta nima maji sarakuwa tave ina kunyan ta yanzu.
Kaima kuma ya kamata ka fara kunyan ta daga yau dan ta zama sarakuwar ka kaman ni daga haka yafita dakin da sauri don yana iya shakoshi ta baya yadda yaga ya hasala.
Dan iska da ka tsaya kaga tsiya a dakin nan ya dade tsaye dafe da bango sai tsaki yake shi daya a dakin.
Sai can yaji taahin motan Bashar daga gidan ya sauke ajiyan zuciya kawai
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,
IDAN KIN KARANTA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NE SHEDAN HAKA MUNA BINKI BASHI,,,,
O lala ka kai mara mutunci sadauki ka gwada min baka da tarbiya yau, dana so nace sai na bi ra,ayin Fatima akan wanan zance amma yanzu tunda haka ne abin bari kaji indai har ni ce na haife ka ko bana raye sai ka auri Fatima.
Kuma idan ka sake ta ban yafe maka ba a rayuwa na, ba sadauki ba har ni da ke tsaye sai da nakai zaune cikin kuka ina fadin.
Don Allah mama kada ki min haka wallahi bashi ba koni ban ra,ayin wanan hadi bani son shi mama na tsane shi kamar yadda na tsani mutuwa na.
Inda nake ta karaso tare da dafa ni kadan tace Fatima, bani son ki da fadin haka nasan baki so amma don ni da Allah dashi kan shi mara tunanen abinda zai je ya dawo idan ya auri wata can sabba zakiyi.
Kaina na noke a cikin kafafuna ina rusa kuka wanda baka yasa mama ta kasan lalashina a lokacin.
Sai ji nayi tana fadin kafita min a shiya tunda ban isa da kai ba baka kaunan farincikina baka damu da rayuwan ka ba balle nawa.
Zai yi magana tai mashi alama da hannu ya rabu da ita don Allah ya dan tsaya jin sai yaja kafan shi ya fita daga dakin.
Kaina ta dawo ta zauna a gefe na tare da dafani tace Fatima ina fatan kin fara fahintar manufana na son yin wanin hadin danake kokarin yi.
Don haka nake son fada maki sai kin jajirce sosai a cikin wanan al,amarin don akwai aiki sosai ja a nan gaba kafin komai ya dawo muna normal life.
Cikin kuka nace mama ni ba zan iya ba don bazan iya zama da miji mai duka ba bai da tausayi mama bai san darajan mace ba ko kadan.
Tai dan dariyan manya tace zaki iya Fatima zaki iyane na fada maki kuma ko bani raye zaki fadi da bakin ki, taimon da zaki min ke nan daya a rayuwana shine ki auri sadauki.
Don ke ce kadai yanzu nake ganin mafita a gurin ki, kece wace zata kwato min shi daga duk wani sherin rayuwa dake bibiyan shi.
Don Allah Fatima ki daure ki kanne ki fitar da duk wani shakku dake damun zuciyar ki, ki saka a ranki zaki sadaukar da rayuwan ki ne don Allah don ni kuma.
Sai naji ta fara kuka a hankali cikin kukan tana fadin Fatima ban da wani mafita da yafi wanan a yanzu haka yasa kike ganin ban tausaya maki ba.
Wanan hukuncin dana yake insha Allahu shine zai kawo karshen azzalumai masu bibiyan shi dashi wanda ba wai sun fasa ba ne har yanzu.
Don haka kada ki zargeni a zuciyar ki na nuna son kaina a gare ki yadda na haifi Amira da maryam haka nake daukan ke ma din nina haife ki da cikina.
Don duk abinda uwa ko da zaiwa mahaifiyan shi Fatima kina min a rayuwana may zai sa na bari wanan daman ya wuce wanan yaron ina kallo yaje ya dauko min wata sabuwar fitina cikin dakina.
Dan uwan mahaifin shi ma yakasa bashi yarshi kan halin da yake ciki balle wani bare can sabba ya ba shi nashi a zauna lafiya.
Hakan da nayi shine daidai a gare mu baki dayan mu sai dai a yanzu kurciya ba zai bari ki fahince ni ba.
Ba dago fuska na dake shabe shabe da hawaye nace mama na yarda insha Allahu duk abinda yaya zai min zanyi hakkuri na zauna dashi saboda Allah da kuma ke.
Ta rungumoni zuwa jikin ta tana fadin na gode Fatima na gode yadda kikai min Allah kema ya baki zuria masu albarka a rayuwan ki.
Insha Allahu bazakiyi dakin sani ba ga wanan auren da yardan ubangijin mu.
Tace tashi kije ki gyara fuskan ki kada wani ya shigo ya samay ki a haka a dauka ko wani abin ne can daban.
Yadda tace haka nayi na mike na shige dakin mu sai dai ban fito ba na zauna cikin dakin kawai.
Amirah dai ba ruwan ta dani don tamafi yayan ta daukan zafi akan zancen don kwata kwata ta daina min magana gaba daya a gidan.
Sai harara da habaici kawai ne a tsakanin mu da ita, maryam kan ce na fita zancen ta na kyale bata da wayau ne da bata biye wa son ranta ba.
Ina ji ina gani yanzu na koma wata abin boyo a cikin daki ban zama falo ko yaushe kunshe nake a cikin dakin mu ban san komai da akeyi ba a gidan.
Karatuna ne kawai ya tsayar dani garin don da na gudu na koma kauyen mu gurin iyayyena da zama amma kuma ba daman haka don karatuna zai iya tabuwa.
Ranan dai da dare na ce bari na dan fito cikin su a falo na dan zauna kadan na samu daga Amira sai maryam zaune suna hira.
Maryam na ganin na fito take cewa a,a matar yaya yau kin gaji da boya ne kin fito ki sarara ke ma kina wani shigewa daki kina kumshe kan ki a ciki kamar lalle kafa.
Nai dan dariya ina zama nake cewa anty maryam yanzun dai ke ake ji zama nake ina karatu don exam da ya kusa.
Kwadayi dai mabudin wahala ne wallahi, in mutum yace ba zai iya tsayawa inda Allah ya aje shi ba ai yana tare da wahala a ran shi.
Zaman daki kan yanzun aka farashi tinda mutum yace shi dan shishigi ne ya kai kan shi inda Allah bai kashi ba.
Ban yi magana ba sai samun guri nayi na zauna da kyau, tare da mayar da hankalina ga TV dake aiki a falon a lokacin.
Kada dai mutum ya manta matsayin shi ga Allah ya dauki kan shi ya kai inda Allah baikashi inji maryam.
Anty maryam please bar zancen nan don Allah kada mama takai ga jin may mukeyi a falon nan.
Idan ma taji ai haka kike so ke don yanzu nasan abinda ya kawo ki cikin mu kuma kuke kullawa keda munafukan gwagon ki.
Nai matukar jin zafin zancen sai na dan ritse idanuwa na tace yanzu basai ki zauna ki auri maji din ba tunda shi wanda ki ke son mannewa din ya tafi sai muga wanda zaki aura yanzu.
Ko shekara dubu zai yi a can dole dai watarana ya dawo gida aiko?
Zasu ci gaba da sokawa juna magana sai ga mama tafito daga dakin ta da waya a hannun ta tanayi.
Da wata kawarta take waya tana cewa Insha Allahu ranan laraba mai zuwa za,a je kai kayan shiyasa na bugo na fada maki don ki shirya.
Amira ta kasa kannewa da uwar ta gama waya tace kayan wa za,a kai maji ?
Kayan auren yayan ku mana.
Can kauyen ko ina?
Ki tambaye shi mana kiji daga bakin shi ko?
Amirah da ta cika ta mike zuwa daki cikin kunan rai, waya ta dauka takira dan uwanta kira daya ga na biyu ya dauka.
Yace Amirah yaya akayine?
Tace yaya yanzu nake jin maji na waya wai ranan laraba za,a kai kayan auren ka kauye.
Dariya taji yayan natayi yace as maji wish zan kyale ta tayi duk abinda zatayi don lafiyan ta da kuma gujewa fadawa fushin ubangijina akan hakkin ta da ke kaina.
Amma ai nine mai auren ko let the vegan come into my house zata rena,kanta da kanta barni da yar iskan yarinya kawai.
Amira tace amma ni gaskiya yaya ina son ka dauki mataki gada ma ayi wanan auren kwatakwata wallahi don ina jin kunua ace wai Bintu ce matar ka gaskiya.
Class din ka ka kare ga wata Bintu can yar kauye wallahi nayi hating din yarinyar nan baka ga yadda ta wani kara komadewa bane ma yanzu.
Dariya yayi yace common Amirah fita zancen kawai ki bar su maji da munafukan nan maryam da Bash duk sune masu kara zuga maji ai zata zo ta same ni ne.
Suna gama wayan da Amira sai yaji gaban shi yai wani masifan faduwar gaba don ua tuna maganan maji da sukayi kaeshe dashi kan zancen auren.
Yadda ke kullawa zai wa Fatima muddin ta shigo gidan shi ga maji tai mai sharti akai.
Domin yadda yake ji a cikin ranshi a lokacin zai iya aiwatar da komai kan wanan manyar yarinyar dake son taiwa rayuwan shi karan tsaye.
Shi yasa ma yai saurin kashe wayan da sukeyi da Amira don maganan ta na kara tunzura mai ziciyar shi ce.
Duk yadda yake son yaiwa mahaifiyar shi biyaya akan auren zabin ta da tai mashi bai tsanmanin zai iya yin adalcin aure akan wanan yar kauyen dako Abuja bai iya fita da ita balle wani uwan duniya.
****** ********* ******
Kamar yadda maji ta fada haka din ne cikin satin da ya zagayo aka kawo lefen auren mu gidan mu.
Muna school har masu zuwa kai lefen suka taru suka dauka zuwa kauyen mu gurin kai kayan.
Akwati ne har guda goma sha biyu dankare da kayan irin na zamani, tsayawa fadar abinda aka zuba acikin akwatinan, sai abin ya zama tankar kauyancine saboda babu kadai ba asaka a ciki ba.
Nan abin yazama turiruwa ga matan kauyen zuwa kallon abin arziki.
Su gwago da yake sun san yadda ake a birni su ma basu bari abarsu a baya ba don suna tallakawa, suma sunyiwa yan kawo lefen abinda ya dace suyi.
Rago gassa abin sha da sauran takarce na kauyawa irin su fura da nono dakar hannu mai kyau cikke a raba mai marfi.
Yan kai kaya suka dawo suna yaba karamcin da akai masu a kauyen mu cikin jin dadi nan su hjy kubura aka shiga rabawa masu zuwa abinda aka samo don ita mama tabarwa yuka da naman zancen.
Har da su Umma da basu tafi ba ankai masu nasu sai dariya sukeyi wai ana gaba an koma baya.
Duk matan dake cikin gari yan gayu diyan masu kudi sunki dole an koma kauye inda ba asan ciyon kai ba an dauko yar kauye.
Amirah ta bugawa dan uwanta waya ta fada mashi duk abinda akeyi a gidan nasu har zagi da dariyan dasu umma keyi saida ta fada mashi.
Sadauki ya kira waya don ya shedawa mahaufin shi shifa gaskiya ba zai iya auren Fatima ba don yana da wace yake so Linda.
Don haka yake shirin fada mai ko zai samu mahaifin nashi ya fahince shi ba da son shi maji ke shirin wanan auren ba.
Don a