Showing 207001 words to 210000 words out of 373688 words

Chapter 70 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

yayi ya hada da nashi ya matse guri guda ba,tare da ysi min magana ba na,wani dan lokaci mai tsawo.
Cikin yar siririyar murya nace mai sakeni yaya don har yanzu fa ka san,akwai sauran lokacin hakan gare mu.
Yace cikin murya mai kasala hakane Fatima yanzun dai ina son idan kin koma saiki fadawa maryam duk wani abinda ya dace ku shirya shi da,wuri don da an daura aure abuja zamu wuce acan zaki sha amarcinki.
Kunya maganan shi ta bani da sauri na bude kofan motan kafana daya a waje nace maganan ka tana sani jin nauyi da kunya wallahi.
Yace nima haka ya dan kwaikwaye ni.
Mukai sallama dashi tinda safe ya kama hanya sai Abuja don aikin su ba hutu.
Sai da na kara kwana biyu a gurin mamana nazo gurin Baba na nai kwana daya na dawo sokoto da zama.

****** ********* ******
Mamana ta sokoto cikin gyarana take sosai abubuwa take bani na kara lafiya da gyaran jikin na.
Nai kyau nasha gyara sosai na canza gaba daya duk wanda ya ganni sai yai maganan hakan.
Amma har lokacin banjin dadi a cikin raina nasan cewa jimamayn rabuwa da su mamane yake damuna a zuciyana.
Don in suna min sheri sai naji kamar nai kuka ban son zolayan da,suke min na amarya ta angi yar shagali yar biyan bukata yar garali.
Amirah tace makullin mota ke akaba, wani sauran canji ke akaba, nikanji wani iri a raina sosai.
Ko yaushe Kabir muna waya dashi yake ce min zasu tafi kasan Benin wani taro na kasa da kasa.
Cikin dare yaya,sadauki ya dira a sokoto sai ganin shi mukayi kwatsam.
Murnan ganin shi kamar kullun yan uwan shi da mahaifiyan shi sukayi nima dai nai farin ciki da ganin shi don ban boye ba sai dana baiyyana a fili.
Ranan har ina mashi tayin abinci sai lokaci ya,dago yana kallona gaba daya sadauki yaga na sake mai .
Da sauri ya kawar da idanuwan shi daga kallona na kara tambaysn shi da cewa.
Yaya a kawo maka abinci ne kaci?
Yace au yau kuma duk murnan za,a gidan tsoho ne yasaka ake min tayin abinci haka?
Kasan fa amarya ce dole abita sannu yaya duk cikin murna ne hakan ai.
Na bata fuska na dan marairaice nace haba Anty Amirah sai ana maganan gaskiya kuma ki jefo wani zance can na fadi cikin shagwaba.
Yaushe rabo da kiba yayan mu abinci Bintu ?
Nace kai anty Amirah nifa yayanane yadda kike son shi haka nake son shi don haka kada ki bata ni gurin yayan mu ko yayana ?
See her bakiji kunya ba ni wai maji yar taki duk murnan auren ne yau take cewa nima yayan ta ne?
Yaya ni kima yar kaunar taka har zakai shakkan haka a gareni nifa yanzu banda kaman ka a duniya don ku ne uwata da ubana.
Murmushi yayi ciki ciki, yace to kawo min abincin na wuce ina yar dariyan jin dadin mun shirya da yayan mu yau.
Nakawo mai abinci na aje nace ko na karo ne yaya ?
Yace kai Maji wanan yarinyar taki fa ta rainani da yawa may kika mayar danine wai ?
Yaya nace a taikace.
Na dora da fadin wanda yafi min komai a duniya .
Yace har da dan tsohon mijin ki ke nan?
Nace ai shi mijine kai ko dan uwa rabin jiki.
Sosai yaji dadin zance na har cikin ranshi yake cewa a rayuwan shi ashe haka yarinyan nan take sauki kai ne da ita haka, ninr dai ban fahince ta ba ashe?
Waya da Kabir ya bugo min ne ya dakatar dani nabar gurin zan wuce niji yana fadin tsoho yai kira ke nan ?
Na dauki lokaci muna waya dashi sannan na fito falon na samu yana cin abinci suna fira da mahaifiyar shi.
Yana fada mata cewa maji mutumin nan fa abin tsoro ne wallahi sosai don yanzu.
Daniel bai yarda ko mu hada hanya dashi duk yadda muke da yawa a guri zakiga ya koma gefe daya.
Nace mugu ke nan dan ban Allah yafishi wallahi don ba abinda zasu iya dakai don kai daga Allah kake.
Dariya sukayi nace wallahi anty na rasa may yasa mutane suke yawan saka ma yaya wanan irin kiyayyan haka.
Maji tace hassadane kawai Fatima kin san in Allah ya haska mutum dole dama sai ya samu wanan kalubalin daga mahassada.
Mukan Allah ya kara tsare muna kai a duk inda kake yaya sai kuma addu,a don Allah akara zagewa don makamin mumunine.
Yau kan ni naga yar taki ta canza fa.
Dama haka take kaine dai baka gane ba kana ganin tana maka kokari kaiko kana ganin kamar sa idone.
Ya ce na sani maji.
Ta faye kauyancine shiyasa nake sake mata layi.
Bintu Kabir har yanzu bai dawo bane daga Benin din ?
Nace yace ysu da dare zasu sauka a lagos sai gobe zai karaso abuja zuwa jibi ya iso nan.
Ku dinga sa insha Allahu mana a zancen ku Fatima inji maji.
Nace insha Allahu mama,,
Kokefa to kuna magana kamar ba musulmai ba.
Ita fa maryam ta matsu Kabir yazo ta amshi dumus don zancen ta na kudine kawai.
Ya mike yana cewa zai shiga yai wanka yaje gun Bashar don yana son ganin shi.
Munyi hira sosai da daren kafin mu kwata bayan nai wanka nai shirin kwanciya saiga wayan kabir yana fada min suna lagos yanzun suka sauka da safe zai karasa gida.
Mundan jima muna fira sai na kwanta da farinciki a raina.
Mafarkin danayine yasa na tashi ina sallah kafin ai kiran sallah tare da rokon Allah sauki koma maye.
Da safe na dan makara nai sallah nai wanka a gaban mirro na kalli irin yadda nasha gyara na canza gaba daya kamar bani bace Bintu.
Wayan Kabir ne ya shigo yana fada min zasu wuce zuwa Abuja nai mashi Allah ya kai su lafiya nan ma sai da ya dan taba min yan maganganun soyayya sosai mukai sallama dashi.
Ga abin karyawa a gaba sai hira su Amirah keyi amma na kasaci a lokacin.
Mama tace badai auren ne ya saki tunane ba har kike kallon abinci haka a gaban ki.
Nai murmushi nace kai haba mama aure kuma bayan gaki ?
Tace gani ina gadai Kabir dinki ko ?
Amirah tace da ciwon kanki ba inji mama Sare da tace haka ranan.
Nace ni ai basu gabana Anty don duk fitanan matar shi bai taba daga min hankali ba ni.
Hajiya Kubura ta shigo da manyan ledoji guda uku nan muka shiga gaida ita.
Tace hjy maijidda ni dai ga dan nawa gudun mawar ba yawa sai ayi hakkuri dashi.
Kai hjy harda dawi niya haka takarba tana budewa ledan farko kuloline set har da flask din su sai dayan ledan turaren wutane masu kyau da kamshi sosai.
Dayan kuma kayan matane aka hada masu tsadan gaske a cikin wasu robobi masu kyau.
Godiya sosai mama tai mata su ka dan taba hira kan bukin tana cewa insha Allahu da ita za,a tafi kauyen mu gurin daurin aure.
Mama tai mata godiya tace kai haba ai shine zama tare din.
Wayasan inda zaici albarkacin yaro shima watarana Bintu ai mutum ce sosai wallahi.
Zata fita suka hade da saudauki dake shigowa a lokacin nan suka gausa dashi tafice daga falon.
Yai zaune ragwab saman kujera fuskan shi babu annuri acikin sa sai mama ke cewa may kuma yafaru nagan ka haka ?
Yace wallahi maji yanzun nake jin news wai Jirgi yai accident daga lagos zuwa Abuja da safen nan kuma akwai wani abokina da zai zo Abuja yau nasan yana cikin jirgin.
Da karfi nace Kabir,,,
Nace wayyo Allah na mama wallahi da Kabir a cikin jirgin nan dazun yai min waya gashi zai shiga jirgi zuwa Abuja.
Daga haka kuma ban san may yafaruba again ?
Ganin na tafii suuu, zan fadi yashi tsale daya yakamoni na fada a jikin shi suuu a somay.
Innalillahi don Allah ku taimaka min kubani ruwa mamatake fadin hakana a gigice cikin rudewa.
Su Amira duk sun rude suma tana cewa a bincika mana aji idan dashi a cikin jirgin ko ?
Ke debo muna ruwa a fridge don Allah kin tsaya kina surutun tsiya sadauki ke fadin haka cikin tsawa wa Amirah.
Ana yayyafa min ruwa nai ajiyanzuciya na bude idona da sauri na zabura daga jikin shi nace mama da gaske Kabir ko ?
Tace dagata a bincika inyana cikin jirgin dauko wayanta mu kira shi mugani?
Anyi kira wayan wai yana kashe.
Kara komawa nayi suuu na sumay a jikin shi yace kama nin ita ina zuwa don Allah.
Maji ta karbeni daga jikin shi tace kiramin hjy Kubura maryam.
Sai gasu tare a gigice tana fadin may ya faru maji take fada mata a takaice abinda ya faru.
Salati ta cika tace sai Allah idan bai ciki wallahi ku kunna Tv mugani don Allah.
Suna kunnawa ga jirgin annuno inda yafadi a wani daji ga yan ceto suna ta faman kawo agaji ga jirgin.
Sadauki ya shigo dakin yace bari mu kaita asibiti maji tace gaskiya kan.
Ita da hjy kubura sukazo dani asibiti nan likita yace bari a dan min allura na samu barci a gani.
Hankalin kowa a tashe yake don har Alhaji yazo asibitin da wayana sukai amfani gurin kiran matanshi dana rubutawa yaya babba.
Wayan na rigin ba,a dauka ba sai gap da zai tsinke ne wani dan yaro ya dauka yana fadin.
Maman bata nan yanzu akazo aka kwashe wai baban mu yayi hatsarin jirgi sun mutu.
Salati suka saka daga inda yake yakai kallon shi gareni ina kwance sharkaf kamar gawa sai numfashin da nakeyi kawai a lokacin.
Sadauki ne ya fara ganin sunayen wa yanda ke cikin jirgin sunan Kabir ne na ashirin da biyar daga jerin sunayen list din wa yanda abin ya faru dasu.
Kuma babu wanda ya tsira daga jirgin duk wanda ke ciki ya mutu a jirgin.
Ban falka ba sai da la,asar na dan bude idona a hankali nake bin dakin da kallo sai dai ban fahinci inda nake ba sai muryan mama naji tana fadin.
Fatima kin tashi ne sai abinda ya faru ya fara dawo min arai a hankali wasu hawaye suka fara dan silalo min a hankali daga idona.
Dafani mama tayi tana fadin Fatima kiyi hakkuri kinji duk mairai mamaci duk wanda lokacin shi yayi tafiya zaiyi.
Allah baiyi Kabir mijin ki bane, sai kiyi hakkuri kibarwa Allah .
Allah da ya halicce shi yafi mu son shi ya karbi abinshi a lokacin da yaso.
Nace a hankali cikin wani murya mai ban tausayi ,mama Kabir ya mutu ko ?
Tace Fatima sai dai hakkuri Kabir yariga mu gidan gaskiya.
A hankali na fara rera kuka mama tana dan buga min baya tana fadin kiyi hakkuri kin ji Fatima.
Shi yanzu adduan mu yafiso da wanan kukan da kikeyi.
Kubarta tayi kukan don shine zai dan sa ta samu relief.
Nai kuka sosai na wani lokaci can na mike zaune da sauri suke fadin ina zaki kuma,?
Nace sallah zanyi mama naga kamar azahar tayi mamatace sai dai la,asar yanzu kan don har munyi sallah mu.
Bayan nayi sallah na zauna gurin ina addua sai kuma na barke da wani irin kuka gwanin ban tausayi dani.
Kiyi hakkuri suke ta fada min shigowan babane yana fadin ashe ta falka Fatima sannu kinji.
Kiyi hakkuri haka Allah ya nufa dake kada ki kara wanan rudewa ki zama musulma mai imani da duk irin kaddaran da Allah ya kawo maki a rayuwan ki.
Mama taso a sallamay ni amma sai Baba da sadauki sukace abarni harda safe aga yadda jikin nawa yake sai a sallamay ni.
Washegari ganin na samu sauki sosai sai dai ban magana da kowa don wani iri nake ji kamar zan shude.
Mun dawo gida inajin ana fadin wai ance a garinsu za ai sadakan ukun shi.
Baba ya shirya tafiya inda zamu ai sadakan uku damu inji Baba.
Haka yasa sadauki ya shiya don tafiyan yaso zuwa gurin mutuwan abokin shi duk daba musulmi bane amma saboda tafiyan mu yace sai an dawo ya wuce.
Motoci uku muka kama hanya dashi har da hajiya kubura da mama Asiya umma tace wai bata jin dadin jikin ta suka barta gida.
Muna isa tun daga nesa muka hango taron mutane a kofan gidan su Kabir, din haka ya kara sani sabon kuka sosai da kyat mama ta samu nai shiru suna min fadan na natsu na daina kuka.
Muna fitowa idanuwan mutane caaa akan mu nan aka fara fadin Allah sarki ga su Bintu nan sun iso
Nan kowa ya fara fadin Allahu akbar Allah bai nufi a zarga aure a tsakanin su ba haka ya kasance.
Sai gaisuwa ake muna nan muka shiga cikin gida a dakin mahaifiyan shi muka shiga.
Mutane sukayo caaa zuwa dakin don ganina ina saye da hijjab amma duk da haka mutum zai iya gani kwaliyan amarcin da akai min a jikina.
Mahaifiyan shi kamilar dattijuwa tana zaune da tasbaha a hannun ta mu kai mata gaisuwa ni dai ban iya magana ba don kukan da yaci karfina a lokacin.
Tace Fatima haka Allah ya nufa tsakanin ki da yaron nan Allah bai nufi akwai zaman aure a tsakanin ku ba.
Nan kuka na ya fito fili mutanen dakin suna fadin kiyi hakkuri kinji Allah yabaki wani wanda yafishi.
Sai naji an rikoni tabaya ana kuka Fatima Kabir ya tafi ya barmu Fatima.
Kabir ya tafi yana mutuwan son ki a ranshi kullun yana min nasiha akan narike ki amana idan kinshigo mu zauna lafiya amma Allah bai nufa ba Fatima.
Sai muka sa kuka nida ita duk da ban dago naga fuskanta ba.
Hakkuri aje tabamu ana muna nasiha sosai mai kashe jiki.
Nan mukejin ana fafin wai shi ko gawan shi ba,a gani ba sai alkur,anin shi da tasbaha da agogon hannun shi.
Nace Kabir Allah ubangiji ya karbi bakuncin ka.
Kowa ce Amin Bintu kiyi hakkuri kinji haka Allah ya nufa daku.
Can wata tace zoku gausa da dayar matar tashi gata can dayan dakin da yan uwanta.
Ni dasu mama muka shiga dakin mun samay ta tana waya muna gaida ita bata gaisa ba.
Sai mutanen dakin ne suka gaisa damu watake cewa wanan ce dama yarinyar da zai aura din ?
Wace ta rakomu dakin tace itace Wallahi, Allah baiyi aure a tsakani ba.
Mukan ai sheri aka kwaxo muna farar kafa yaja muna hasara.
Kai amma kuwa bakiyi ba wallahi gaki dai kamar mai ilimi saidai ashe baki da tauhidi?
Hajiya kubura ce taba ta amsa da hakan.
Tace banda tauhidi aiku kuna dashi aja muna tsiya ace kada mu fadi.
Kika dai jawa kanki ke da kishi har akan mamaci inji mama Asiya ta karbe.
Kamata yayi asamay ki cikin jimamay ba cikin kishi ba haka kamar ba wace tai rashi haka ba.
Ku tashi mutafi mu gausuwa mukazo maku ba tsiya yakawo mu ba nan.
Mun fita muna jin su suna zage zage nace a raina ai in sakwatawa kuke kun hadu da mama da hjya kubura a raina.
Bamu dadeba su baba sukace mu fito nan maji ke fadawa mahaifiyar shi cewa za a aiko da kayan lefen da yai min.
Ko yanzu don anzo gaisuwane yasa ba,a zo dashi ba.
Matan sukace haba haba habadai da zafi haka.
Sai mahaifiyar shi tace wanan ai kyautane tsakanin ta dashi tun yana da rai don haka mun yafe mata ba namu bane rabontane daga gare shi.
Allah ya bata miji nagari idan antashi auren ta a fada muna kada zumunci ya yanke.
Uwargidan Kabir da zamu tafi tayi kuka sosai muka rike juna tana min addua tace zata dinga bugo min waya.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,
.
YA ALLAH DUK WACE TA TURA MIN NOVEL GA,WANDA BAI BIYA BA ALLAH KAI MIN BAKAR ISA AKAN MAISHI YA ALLAH DAMU DA WANDA DUK YA KARANTA A SANADIN TA,,,,


A yammacin da aka,sallamo sadauki baba ya tara duk ilahirin iyalin shi a falon shi yana masu magana a cikin takaici da bakin ciki.
Ku san Nafisa ce ta karshen shigowa falon tana saye cikin wani dogon riga da yai matukar matse mata jikin ta sosai.
Baba ya bita da kallo na tsana da yakaici yace cikin bacin rai ke ina hijjab dinki zaki shigowa mutane kusan tsirara haka.
Tace cikin wani bakon murya mai baiyyana wani sabon al,amari a gareta,
Baba,,, nifa ba tsi, tsira rarra nake ba don a saye nake da, da da riga a jikina.
Ido ya kura mata cikin nazarin ta yace Nafisa kanki daya kuwa yau din nan?
Warassss nake Baba may ka gani kafin yai magana Umma take cewa daga barci take fa take wanan ita shegen haka.
Yace maza jiki sako hijjab dinki na baki minti uku ki dawo nan mara mutunci kawai.
Ya juya gurin Umma yana fadin Atika ina son idan ina magana da yara na ki daina saka bakin ki daga yau.
Ki bari idan na sako sunan ki a ciki ki saka bakin ki, idan kuma kinga kamar fadi nayi kawai to kici gaba da hakan.
Yanzu saboda mugun halinki na


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login