Showing 174001 words to 177000 words out of 373688 words

Chapter 59 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

son yaran nan suyi aure hakana don haka ai zancen zuwa gidan yan matan su ai magana.
Hjy kubura tace har da dana ke nan Baba yace aishi ma yakamata yai aure shida ke fita waje ya dade kinga sai ya dauki abinshi su tafi can su karata can.
Yace zaiga kanin shi Sani suyi magana kan Rahama don asan abinyi nan dai duk aka aje magana za,a aika gidajen matan su.
Sai dai may Baba yana zuwa gurin dan uwan shi kan zancen auren sadauki da yar shi da kowa ya dade dasani sai cewa kanin nashi yayi gaskiya shi sai sunyi shawara da matar,shi da yarsu tukun.
Baba yace ikon Allah sani akan auren yaran da,suke duk abu daya shine zakace sai kayi shawara da mace tukun kabani amsa.
Yace eh don akwai dan mahawara tun kwanaki akan zancen saboda haka abari ya kara tuntubar uwar yarinyar yaji.
Haka Baba ya bar gidan jiki ba karfi don yana da ,wuya ba,a samu matsala ba ke nan amma dai sai yabar zancen a ranshi.
Ita ko hajiya saude da mijinta yazo kan zance sai cewa tayi ita gaskiya bada ita bata daukan yar ta, taba mashayi yarinyar da kurciyar ta taje can takama hadiyan bakincikin da namiji ga banza.
Yaje can ya samu wata irin shi yar shaye shaye su daidaita tsakani su, amma bata ganin maciji da rana ta tura hannunta ramin shi da dare.
Yar ta tazo ta haifi yara lalattatu a rasa yadda za,ayi dasu yace amma dai kin san wanan magana zai iya kawo matsala tsakanina da dan uwana .
Tace zumuncin shi yadade bai baci ba ai akwai diyan dangi da yawa yaje mana ya nemay su can ba yarta ce kawai yar dangi ba ai.
Sai yaja bakin shi yai shiru don bai iya tunkaran dan uwan shi da wanan zancen gaskiya.
Shi mai daurawa sadauki aurene yau kuma ace shi da kanshi ya hana yarshi sai yaya ke nan
Maji ko da,sukai waya da saudaki tasa shi gaba kan lalai sai ya hado lefe daga can bai so ba amma don bin umurni ta ya hado kayan shi tundaga kasar Spain da sukaje wasan.
Sai murna take cewa dan ta ya kusa zama kamilin mutum tunda zai aje iyali,
Duk da dai ba son hada zuria takeyi da yar hjy Saudae ba don kansu guda da umma kuma yaran basu da kunys ko kadan.

Bayan kaman Sati uku ya shigo gari nan matasa su kai dandazo gurin zuwa taron shi da,dawowa zakace wani gwauna ne zai zo.
Mukan muna school bamusan wainan da ake toya ba a gidan don bamu san zai dawo ba a ranan.
Sai after six lis muka dawo duk a gajiye muke a lokacin, nice gaba maryam tana baya ta tsaya ba mai Napep kudin shi.
Tun a kofan shiga falon mu na fahinci akwai namiji a ciki don takalman maza danagani daga waje.
Ban kawo shi bane tunda nasan baya kasan a lokacin da yar sallamana na shigo falon.
Ina saye da,buje da rigan les da,akai min feeted dinkin ya karbi jikina pink color da,farin zare akai mai yan flowers kanani ajikin shi har bakin lace din banyi kitso ba don ciwo da kaina keyi sai dai na,wanke na daure da ribon kawai.
Na shigo ina fadin wai mamana yau kan duk nagaji, wallah,,,,
Ganin sa kawai nayi zaune ya kara haske yai kyau dashi yana saye cikin wasu kayan maza ko ba,a fadi ba kan san sukai kudin su ga wani irin uban kamshi daya hade muna falo tun daga waje zai tare ka.
Haka kawai ganin shi yasa na makale magana ta sai gabana da naji ya fadi yaushe rabon dana dan matsala a gidan mu kusan wata shidda da yan kai ke nan,
Tun tafiyan shi don ko suna vedio call dasu Amirah bani zuwa kusa ni balle nagan shi.
A hankali nakai zaune saman masangalin kujeran dake daga kofan falon ina fadin sannu da dawowa yaya.
Cikin dan basarwa ya amsa min yace kuna lafiya,
A taikace na bashi amsa da kalau na mike zan shiga sai ga Maryam tana ganin shi tasaka wani irin uban ihu tai kanshi.
Yace ke ke kinfa girma yanzu kinga yadda kuka koma,wasu big ladies da ku kuwa,?
Ta wani shake murya tace kai yaya yanzune ma fa zan cika twity cif fa.
Itako Bintu she is just 18 da yan kai yanzu kaga mu yarane har yanzu don dai ka dade baka ganmu bane kawai.
Yace baki ganin tana ganin ta girma yanzu harda bani amsa any how.
Ni kaina na san amsar dana bashi bata dace ba amma yadda ya hade fuska shi ya dace dashi ai,
Maryam tace kasan aure zatayi shiyasa ta fara daga kai.
Yace aure kuma tare da kallon maji yace badai da wanan tsohon ba dana taba gani.
Kai yaya Kabir ne tsoho wallahi dai ba tsoho bane don dai tana da mata ne kawai
Yace da karfi cikin tabaya da what?
Mata bako guda ba fa ke nan maryam tace ai Bintu babbace itace ta uku a gidan.
Yace fir god sake Maji may zaku aurar wanan wajen don Allah kuma wai mai mata har biyu ita ta ukun su,
Nace tau bisimillahi matsala ya sauka na,shige abina ciki kan shi kawai ya girgiza yace ok lalai ma yarinya ta girma kan.
Har nashiga nai sallah kada lokaci ya karasa shigewa suna falo sai zuba suke shi dai bakajin bakin shi.
Nafito dauke da abinci a dan plate na koma can nesa dasu na zauna na fara ci a hankali.
Kamar kullun fuskan shi a daure yake ba dariya amma kuma wanan yaudararen dariyan tashi da baikai cikiba yana nan shi amsa da yake ba kannen shi kawai.
Inacin abinci na jin sunana da maryam ta kira yadani dago kai shima idanu ya,watso wanda tun ina yarinya nasan da wanan kallon wanda nake dauka kallon tsana.
Tace wai Bintu don Allah ba har part mukace zamuyi mashi ba amma maji ta hana mu.
Nace kunfi kusa anty maryam ba magana na bane wanan na mike zuwa cikin kitchen din dake attache da falon mu na aje plate na shige don lokacin magariba yayi shima naji muryan shi yana ce masu zai fita yai sallah ya dawo.
Bayan na idar na samu mama a falo nace mama dama antanadarwa yaya da abinci ne tace waya fadawa zai dawo yau.
Barshi kawai kinji tunda yazo nai mashi magana yace min wai yaci a government house can yafara sauka wai.
Nace ,a,a ashe abin nayi ne ke nan abu har gidan gwauna kuma tace bari kedai mutane sun dauki kwallo yanzu kamar wani bauta can.
Amira tace ku may kuka gani mudake gida mu mukasha kallo yau kinga yadda aka rako yayan mu kuwa a gidan nan.
Motoci mashin mashin kala kala mungan su yau wai duk yaya aka rako gidan nan.
Nan dai mukasha hira har muka lakace dare yayi bamu sani ba shikuma ba dawo gidan ba har lokacin.
Halinshine idan ya,dawo bai zuwa da,tsara ba sai bayan kwana biyu su iso garin.
Wanan karon ma hakanw ta faru don sai bayan kwana uku da,dawowan shi kayan shi suka iso.
A gaskiya mun sha,tsaraba sosai don bai nuna,min yan ubanci ba a nawa ganin Amma mama sai naji mama na mashi fada wai bata son haka don may kayan su Amirah yafi nawa kyau.
Amira tace Maji haba duk abinda yaya,yaiwa Bintu sai kice ya,nuna mata banbanci mana.
Maji tace ban son hakanane nafu idan zai saya maku abu ya saya maku iri daya koda kala zai banbanta.
Shi dai shiru yayi kawai baice komai ba yasan al,amarin maji da,wanan yarinyar sai Allah kawai.
Wai ma ko yaya akayi har maji tagane hakan da sauri amma ita,wawiyar sai wasan baki take tana godiya.
Gaba daya gidan an sheda sadauki ya dawo don har kudi sai da yabawa mutanen gidan.
Sai cikin dare ya shigo yace wa Amira ta kira mu tazo mu kwaso kaya a motan shi.
Tirka sa don set din akwatina ne har uku mukai ta,kwaso bamu iya daukan manyan dole shi ya kwaso sai da,muka huta muka shiga duba kayan.
Ni har tsoro kayan suka,bani abu sai kace diba akaitayi ba kudi akasa aka saya ba don yawan su.
Mun gama Amira ta nisa tace wai yaya munga kaya har bamu iya dubawa don yawan su.
Murmushi na kullun yayi yace sunyi maku ke nan dai ko da,sauri mukace sosai ma yace yana mikewa maji idan akwai abinda babu aciki sai a,saya anan.
Ban san lokacin da nace kai haba sai kace riya wanan kaya haka aiko gidan sarki za,a kai sai haka.
Maryam tace, ke Bintu akwai abin dariya wallahi baki taba ganin lefe bane haka nace nikan sai yau gaskiya Allah dai yasawa aure albarka sukace amin gaba daya dakin
Muka kwasa sai cikin dakin muka mayar dasu can kuryan maji muka,kawo zannuwa muka rufe ba,wanda yasan anyi a gidan balle afara yadawa.
Shafa,i da,wuturi nayi nice farkon zuwa na kwanta zuciyata sai tunanen wanan irin kayan da yaya hado na laife nace a fili Allah ya kara shirya wa maji dan ta.
Na sauke wani ir8n ajiyan zuciya tare da cewa Allah gamu gare ka mai kudi yaji dadin shi gaskiya.
Wankan da nayi kafin nai sallah yasani jindadin kwanciya sai barci sai dai kuma zuwa dare ban san may ya,farkar dani ba.
Amma sai naji dirin mota an dawo da daren nan nace a,raina Allah dai yasa ba yaya bane a cikin daren nan.
Sai kawai na tsunci kaina da tashi na leka shi din ne yana rataye da corth din shi kawai sai na zarge shi.
Da sauri nai istigifar don zato zubi ne koda ya zama gaskiya da sauri na koma makwanci na.
Sai dai barci ya buwaye ni don haka na mike na fara gabatar da nafila har tsawon wani lokaci na koma na kwanta.
Sai barci da,safe ban shiga school ko maryam yau bazata dadeba can da,wuri zata dawo.
Sai na,dan kara,kwantawa sai zuwa goma nafito don na kama,ma Anty Amira aiki don zata fita yau.
Ina fitowa mukayi kicibis dashi kallo daya nai mashi na gane yasha daren jiya.
Ban kula shi ba don wani irin tsanan shi naji a,raina ya kare zuben min a idona ko lokacin mama tana ciki tana shiryawa haka ma Amira tana kitchen tana aiki.
Ke dauko min abin karyawana yace cikin wata murya na dan kalleshi nai saurin kara dauke idona.
Ya zauna yana wani lumshe idanuwan shi nasan abin bai sake shi ba har lokacin.
A hankali na,tako inda yake dauke da,kayan karyawan shi na duka saitin shi kamar zan aje kayan .
Cikin wata yar karamar murya nace mashi ka,saita kanka kafin mama ta,fahinci halinda kake ciki hankalinka ya tashi.
Don nasan kasha daren jiya kadai jin tsoron haduwan ka da Allah ka tausayawa mahaifiyar ka.
Na mike da,sauri na,barshi daidai ya mike yana gyara saita kan shi daidai don yai mamakin yadda duk yakamay amma wanan manyar yarinyar wai ta fahinci yasha jiya da dare.
Da kyat don mamaki ya iya saita kan shi sai ga uwar tafito kuwa tace a,a babana kana nane zaune ashe yace eh Maji yanzu nazo ahine ma wanan yar taki takawo min abin kari.
Fatima to nima kawo min na karya yau da Baba na tun dashi kun bashi.
Na amsa daga ciki nace mata gani tafe mama ita dai abinda akayi na kawo mata plantain ne da Irish da,kwai sai tea.
Na koma na dauko masu ruwan sanyi nabawa kowa nasa na juya nabar falon inajin su suna hira yana ce mata har yanzu yana da gajiya don bai samu hutu ba.
Nasan ya fadi hakane ya kawar da zargin wani abu a ranta nan take fada mashi cewa taji baban su yace zai kira baban su Sani yaji yadda za,ayi kan zancen auren shi.
Ban ji amsan daya bayar ba amma naji tace ai ina ga ba wani dadewa za,ayiba ayi bukin.
Bai dade ba yafito yabar gidan kada ya sake layi uwarshi ta gane shi tunda ga manyar yarinyar nan ma ta gane balle maji.
Da dare muna zaune Baba ya aiko kiran maji tafita zuwa amsa kiran shi andan jima kadan sai ganin ta mukayi tashigo rai a bace.
Idanuwan ta sunyi luhu, luhu sun kada sunyi jawur dasu duk muka bita da idanuwan mu muna kallon ta.
Amirace tace Maji may akayi kuma yaya sadauki ya dawo magana ya tashi ko.
Ta dago fuskanta ba yabo ba fallasa tace bashi bane Amirah na sauke ajiyan zuciya daga inda nake.
Tambayan ta suka matsayi nace anty kubar mama harta huce tukun koma may ye kuji daga baya.
Dalilin dayasa mukai shiru ke nan gaba daya a falon ba wani mai kwakwaran motsi sai tv dake ta aiki shi kadai.
Sai wayan mama yai kara ta dauka da alaman lalashin ta ake ga,wayan kuma kamar muryan Baba ne.
Mama na aje wayan sai kawai tasaka,wani irin kuka mai ban tausayi tana cewa ita dai gidan zata bari gaba daya ma kowa ya huta.
Da sauri na mike na isa gareta na ce mama don Allah don Annabi koma maynene kiyi hakkuri kibarwa Allah.
Ban kai ga fadin wani abu ba,sai ga yaya sadauki ya fado dakin ganin yanayi uwar yasa shi saurin karasawa gare ta yana tambaya cikin tashin hankali.
Su Amira sai faman kuka sukeyi suma hankali duk a tashe nima kukan ne yazo min lokaci guda.
Kara tambayan ta yayi tare da bata hakkuri kafin ta dan sarara kukan nata sai kuma dakin yai tsit.
Tace babana ban taba zaton Alhaji sani da kan shi zai iya muna wanan cin mutuncin ba a matsayin shi na mahaifi gare ka.
Amma sai gashi tau ya,wanke ido yana fadawa Alhaji maganan banza a kanka.
Yace bazai ba mashayi yar shi ba kaje ka samo maahayiya yar uwar ka ka,aura shi yar bata auren mashayi.
Cikin wani murya naji yaya yai magana yace maji shine abin tashin hankali ni haka ma,yafi min nono fari wallahi.
Dama don naga kina sone yasa kawai na yarda amma ni ban ga abin bata rai ba kowa ya rike nashi.
Ba aba ban ta ba ganin Alhaji na kuka da hawayen shi ba sai yau din nan akan yadda Sani ya rufe ido ya fada mai magana akanka.
Kuma yace daga nan gidan aka kai maganan gidan shi don haka ba zai yarda ka lalata mashi ya ba.
Furza iska yayi ya mike tsaye yace don Allah maji ki kwantar da hankaliki Allah yabani wata,wace tafita ba,shike nan ba.
Amira tace wallahi ko shike nan maji kinga ma,shi bai damu ba.
Maji tace Amira baku ganewa ne shima ke nan jini kuya hana yar shi wa zai bashi yar shi a garin nan.
Maryam tace gari da yawa ai maye baicin kan sa maji in sun hana yarsu sai may Allah zai bashi wace tafita da yarda Allah kuwa.
Ga mata gari da yawa birjit in wani yakika da kwana wani da yini zai nemaka.
Shiru mukayi kowa da abinda yake tunane a ranshi har yagaji da zama yafita nasan shima abin yaci mashi rai sosai.
Da safe sai gani mukayi su umma su biyu wai zasu uguwa mudai san can gidan zasu sukara bata zancen.
Haka ko akayi don gaba daya sun kara jagula al,amarin baki daya kare baici.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


A LOKACIN MU KE,,,,,,,


Maria duk zirga zirgan da akeyi asibiti, hankalinta a tashe yake gashi ta bude kudin bankinta asusu da take tarawa wanda sadauki ke kawo mata baikai ko dubu ashirin ba dama wanda take tarawa agida.
Kafin wani lokaci labari har ya zaga, gari ko ina yan sanda suna neman Sisko ya,gudu ya,boye gidan abokin shi can wani uguwa.
Amma haka bai sa an fasa bincike ba don a gano shi don har hukuman human right tasan da zancen a hannun ta yake yanzu.
Mahaifin Aliyu bawan Allah kamilin mutum abin tausayi sai kuka yake kawai yayi a fili yayi a zuciyar shi.
Ya rasa ina zai saka kan shi ya samu kudin da za,a ceto rayuwan yaron shi Aliyu.
Haka yasa wani matashi dake jinyan dan uwan shi a dakin yaji tausayin bawan Allah sosai.
Shine yakai sanarwa a gidan redio da kafafen yada rabarai na cikin gari don a tallafawa wanan dan karamin yaron dake shan wahala.
Shine har Allah ya taimake su labarin yakai ga idon matashin dan kwallon da suke dashi a gari watau U F umar faruk Abubakar yaji sanar wan.
A lokaci guda yaje ya biya kudin aikin tare da,bada kudin magani da wanda yaron zaici abinci har da iyayyen shi.
Mahaifin ya rasa bakin da zaiwa wanan matashin godiya sai dai yafara jero mashi addu,oi masu ma,ana acikin rayuwan dan adam kawai.
Tare da fatan samun nasara a,rayuwan shi ga,duk abinda ya tun kara na alheri.
Sisai yaji dadin adduan wannan bawan Allah sai yake gani ai, kawai kamar an zare mai wani dutse mai nauyi a jikin


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login