Showing 246001 words to 249000 words out of 373688 words

Chapter 83 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

kullun zuciyar shi taki yarje mashi Fatima a matsayin mata a gare shi abokiyar rayuwa.
Babs ya dauki wayan tare da sallama yana cewa Umar sanda babuga sadauki.
Sai kaji irin alheri da taron da mutanen arzikin nan gidan su Fatima sukayiwa yan kai kaya ko?
Ai ni nasan ban taba dana sani akan ka sadauki bar wa yan nan wawayen iyayyen naka su Atika suna zaton auren wayayya shine zani ga aure.
Sai gashi su gidan nasu sarakan ko ruwa ba,a mutane sun sha ga wullakancin da sukai wa yan kai kayan sai kiran babu babu kaza a ciki sukeyi.
Nasan dakai da mahaifiyan ka dama mutanen arziki ne ba yau ba don komai naku a cikin nazari kukeyin shi.
Yace lafiya dai ka kirani yanzu ko?
Sadauki da ya rasa may zaice a lokacin don duk jikin shi yai sanyi sosai dajin yadda mahaifin shi yake a cikin farin ciki yace.
Dama kawai na kiraka ne mu gaisa naji lafiyan ka don bamu samu gaisawa ba jiya.
Nan dai mahaifin ya shiga sa mashi albarka tare da fatan gamawa da duniya lafiya.
Suna gama waya da mahaifin nashi ya kira mahaifiyar shi sun gaisa sai kuma shiru sai uwar ke fadin kaji dai ankai lefen ko kuma sunyiwa mutane halarci sosai a can.
Cikin murya mai nuna damuwa yace Maji ni may zance akan wanan magana tunda zabin kine.
Yanzun ma nakira Baba na fada mashi zancen nawa auren na zabina da nake so sai shima yake min magana akan wai ankai kayan lefen ko amma ni ban so akai kayan nan duka ba tunda ba wata bace can da suka san darajan kayan.
Sadauki wace irin banzan magana ce wanan kuma ko kayi shaye shayen naka ne kake son mayar da mutane kananan yara ?
Jin dadin da kayi ne yasa har kake son watsa wa mutane kasa a ido ko may.
A kan wata arniya can har idon ka ya rufe kake son yimin cin mutunci ko may ?
To wallahi kaji na fada maka, ko da wasa nakara jin zancen arniyar nan a bakin ka sai na bata maka rai fiye da yadda kake tunane.
Don haka idan an aura maka Fatima sai kai gunduwa gunduwa da ita ka zuba a buhu ka kawon gawan ta nan.
Sakaran banza mara tunane an maka gata shine kake son yiwa mutanr rashin mutuncin ka da ka saba ko ?
Haka ya kashe wayan ran shi a bace yasan dai yanzu baida wata mafita yadda mahaifan shi suka hau zancen sai anyi wanan auren dole.
Da kyat ya ja kafan shi zuwa bakin window dakin da yake zaune cikin wani katafaren hotel na kasan LasVegas.
Tun ranan kuma baida sauran wata walwala a tare dashi ga Amira ta ishe shi da kiran waya tana mashi kwarmato wai taga maji ta karbi keys din gidan shi a hannun Bashar zasu tafi da mummy su duba gidan.
Idon shi ya rufe da jin wanan bakin labarin suka soma canza launi, zuciyar shi ya dinga mashi wani radadi da zogi ya mike tsaye ya nufi fridge din falon shi nan ya bude ya dauko wani dan mitsitsin kwalba ya kafa a bakin shi.
Yana shaye abinda ke cikin kwalban ya wurgashi kasa gefen shi kwalban ya tarwatse.
Dafe kan shi yayi yana wani irin huci mai fitar da zafi daga bakin shi, yana fadin why maji why zakiyi min haka please?
May zanyi da wanan yarinyar da ko na yini daya bata iya daukan lalura balle na zama dindin din.
Kai ba shakka wannan yarinyar ta zama mashi kafen ka al,amarinta ya na matukar caza mashi kai.
Yasan idan baiyi da gaske ba zuciyar shi na iya kamuwa da wata lalura da zai ja mashi komawa baya ga harkokin shi.
Yana kwance ya saman dogon kujeran falon ya dinga karanto addu,an samu sauki a cikin mayen da yake.
Ya jawo dan filon kujeran dake gefen shi ya rungumay filon a kirjin shi tare da rintse idanuwan shi.
Yadda rayuwan shi zai kasance da zama da wanan yar kauyen yarinyar a gidan shi, wacce ko kwaliyan kirki bata iya ba kullun tana dunkule,a cikin hijjab.
A haka zazzabi mai zafi ya rufe shi, ga dubin damuwa da kadaici daya ishi zuciyar shi.
Duk da shi ba likita bane yasan gap yake da BP shi ya hau a lokacin.
Don irin yadda yake jin kan shi yana mashi sai matsanacin kasalan dake damun shi,.
Gaba daya sai ma yaji zaman garin ya ishi ra shi baki daya tankar ana hura mashi wuta.
Haka ya wuni kwance a dakin shi ko wasan motsa jiki ya kasa fita yayi sai shawara yakeyi kawai ya koma gida ai koma maye a gaban shi zaifi mai.

****** ********* ******
Sosai mama ta mayar da hankalin ta gurin gyaran mu a cikin hikima irin ta manyan mata.
Ta hayan gyaran jiki da kuma magunguna na hausa da zasu karawa mace, ni,ima a jikin ta.
Lokaci guda duk da damuwar da nake ciki da tashin hankalin wanan kaddararen auren.
Amma haka bai hana ni canzawa ba nai matukar kyau, tankar ni nai kaina a lokacin.
Cikin dare ya iso garin muna folo a zaune gaba dayan mu har mama dake ta waya da kawarta kan wasu kaya da take son a hado mata.
Da murna suka tare shi duk da dare ne amma hasken fila ya haska kowan mu.
Saudaya ya daga kai, ya kalleni inda nai mashi sannu da zuwa kaman yadda kowa yai mashi sannu din.
Cikin dan sakin fuska kadan mama tace kai kana hanyane ashe bamu sani ba?
Yadan kai zaune a kasale yake cewa wallahi tafiyan dai gatanan kaman ba shiri nayi ta nima maji.
Maryam tace Allah yasa ka dawo ke nan har a gama buki yaya don idan baka nan ba zamu ji dadi ba.
Maji ta kwantar da murya cikin tsigan lalashi tana fadin haba ya dawo ke nan mana ina kuma zai koma ai gara ayi komai dashi yana garin don jama,an arzikin shi.
Amira ta saki wani irin tsaki tana cewa kai maryam ke wallahi baki da kunya sai kace kanki ne farau din aure.
Maji tace basu bane farau saidai su yanzun ne zasuyi dole suyi dauki kuwa.
Sai kuma Amira tai fushi wai da ita maji keyi don ita bata tashi aure ba yanzu a matsayin ta na babba cikin mu.
Ta mike cikin fushi zata shige tana cewa, Allah dai yasa ni ban iya kutsawa aso ni ba balle na kawo wanda bsi sona.
Maji tace cikin takaici wawiya kawai mara hankali shekaru yakai bata sani ba sai hauka.
Sadauki da idanuwan shi suke mai a lumshe yana sauraren kowa sai dan murmusawa yayi yace,
Maji ba dake take ba ai da maryam mai shegen rawan kan tsiya take magana ai.
Zaka ci abinci ne inji mama data ga dan nata cikin alaman damuwa yake.
Yace ban jin cin komai yanzu maji dan dama dama dai ko tea na dan walwale hajina dashi kawai.
Maji tace Fatima hado ma yayan ku tea mai kauri ya sha don yafi mai zama haka nan.
Na mike don dama a takure nake zaune a gurin na shiga kitchen don hado tea din.
A fakaice ya bini da satan dan kallo duk abinda yakeyi akan idon mama amma tai tankar bata gan shi ba.
Nafito da tea din hade da jug din ruwa cikin dan karamin tire dan madaidaici nakawo mashi gaban shi.
Na samu ya rike goshinshi dake damun shi da halbawa da hannun shi daya.
Nace cikin dakewa ga tea din yaya, ya bude idanuwan shi da kyat yai min alama da na aje a gaban shi.
Sai da ya ciro magani daga aljihun shi ya bare tare da hadewa tukun ya fara dan kurban tea din a hankali don zafin shi.
Baja jin dadi ne naga kasha magani mana mama take tambayan shi da hakan ?
Da kyat yasha cokali kamar shidda ya aje cibin tare da mayar da jikin shi saman kujera ya kwanta da bayan shi a hankali.
Muryan maji yaji don a lokacin na koma cikin dakin mu, maji tace mashi.
Ka sa damuwa a zuciyar ka ko dubi yadda duk ka lalace lokaci guda, kana ganin zan cutawa rayuwan ka ne ko may sadauki?
Ya dago kai tare da bude idanuwan shi yace namay kuma maji ?
Tace akan auren da kake gani ina son tirsasa makayi ba da son ran ka ba mana.
Yace maji ni fa banda zabin daya wuce naki a rayuwana akan may zan tayar da hankalina ga abinda kike shirin yi min gata.
Mama taji dadin kalamin shi sosai a ran ta har fuskanta ya dan baiyyana murmushi kadan.
Nan ta shiga mashi nasihohi akan hakkin aure tare da saka mashi albarka kwando kwando na mata biyayyan da yayi tana mashi fatan alheri.
Sosai ya dan ji sasauci a zuciyan shi dan kasancewan da sukayi da mahaifiyar ta shi na dan lokaci, abinda ya dade baiga hakan ba a tare dashi tsakanin su.
Ni dai tun wanan lokacin ban kara bi takan komai ba don ko kallon inda yake banayi balle nasha harara.
Hakan yana matukar bata mashi ran shi sosai yakance a ran wai wanan abar ce zata zauna da mutum har ta farauta mashi ran shi yaji dadi a haka?
Mace komai bata iya ba ban da dunkulewa a cikin hijjabi kulun kaman munafuka ko muguwa.
Wama yasani ko maganan Amira gaskiy ne asrice maji sukayi don suci arzikin su.
Don shi baiga abinda maji tagani gacwanan yarinyar ba har take kokarin yi mashi baki a kanta inba hasken fata ba kawai.
Gashi baida yadda ya iya dole yasawa zuciyar shi hakkuri da wanan auren kaddaran don ya dadawa mahaifan shi rai kawai tunda suna so amma shi kan yasan an tsere mashi gurin matar gwadawa tsara kan.

Ta ko wani bangare na gidan kowa sai shirin buki yakeyi banda mummy da babu nata ko daya a cikin bukin don ita yaran ta kanana ne kwarai agidan.
Sai dai kusan tare suke harkan bukin bangare mama da ita don ta saka kanta tsunbul a ciki inda su umma ke fadin wai kwadai ne kawai ya kaita ciki don taga gurin ci.
In bashi ba ai su ma yaran su ai diyan mijinta ne may sa zatafi bada karfi a dayan shiyan kawai.
Ta bangare na ni kan ba wani abinda na shiryawa aure sai harkan bukin Anty maryam kawai nake yi kamar nima ba amarya bace,
In dan anyi min magana nakance ni ba wani bukin da zanyi sai dai dan dama dama walima indan zan samuyi.
Su mummy sun tafi sun gyara gidajen mu yadda ya dace duk da ba wasu abu za akaiba mai yawa saboda ko wani ango yasaka kayan komai a nashi gidan.
Baba yai fadan haka yace don may zasuyi mashi haka da su bari shima yai wa diyan shi nashi bajinta da ko wani abu kewa yar shi idan zatayi aure.
Kayan aiki ne aka kai muna irin na amfanin mata ko shi ba wasu masu yawa ba don sauran abubuwa irin su gas, su tv, fridge, toaster da yan kayan kitchen electronics akwaisu a kitchen din.
Yan zuwa jai kaya suka dawo suna fadawa mama abinda ya faru a gidajen mi mama tace a daikai nata da ta saya muna hakk8n mune ta sauke muna ai.
Saura kwana hudu buki ya shigo cikin gidan duk gidan a lokacin cike yake da baki yan zuwa buki yan uwan hauhuwan maji da ga garin su sunzo.
Dakin ta ya samay ta da wata yarta ta dagin su mama take ce mai bayan sun gaisa dama ina son na gan ka don gobe ko jibi nake son akai Fatima gurin iyayyen ta don su ma suyi nasu bukin a can tunda ita yar fari ga mahaufin ta.
Shiru yayi bai dago kai ba tace don haka sai naji naka shawaran akan tafiyan nata don ban san ko kana da wani shiri ba ?
Yadago idon shi da suka canza launi yace maji ni wani shiri nake dashi duk abinda kuka tsara ai daidai ne.
Ta kara cewa ina son ka basu mota da sauran kayan da zasu bukata a can akai masu don zirga zirga da amfanin su.
Baiyi magana ba nan ma shiru yayi yana tunane wa maji ke son na tura wanan bakin kauyen ya kwana can gari ba wuta ba wani abin more rayuwa can.
Ranan da za ai kamu gidan mu ya cika makil da mutane yan uwa da abokan arziki ta ko ina na bangaren dakunan gidan.
Mata mu hudu ne maza ukku, sai dai a lokacin na bata tsarin abin don duk yadda akayi dani na fito zuwa gurin kamun naki futowa nashige bandaki na kulle kaina ciki.
Mama tace a kyaleni tunda bani son fitowa agan ni ai hakan ba ibada bane ga mutane yan gulma da basu sanni ba sun cika gurin don son ganin kwam.
Sai da naji ba kowa a shiyan duk sun watse sun tafi gurin kamu nafito na zauna a bakin gadon mu nai tagumi ni kadai a dakin.
Sai ganin mama nayi tashigo dakin abinda ya dan sani firgita ke nan zan tashi tace koma ki zauna abinki na fahinci baki son ai maki kamu a garin nan sai a gaban iyayyen ki ko?
Don haka kada ki damu gobe insha Allahu za,a tafi dake can zamu washe gari muyi maki naki a gidan mahaifan ki.
Kuma kinyi gaskiya don wanan halin naki yasa nake kara kaunanki Fatima a raina don baki dauki karyan duniya ba ke a ran ki.
Muna nan zaune tare da mama a daki har mutane suka fara shigowa tana kara yi min nasiha akan duk rayuwan da zamuyi na daure nayi hakkuri watarana sai labari insha Allahu.
Ganin mutane sun fara shigowa yasa ta barni ta koma dakin ta sai lokacin ne na dan sake jikina nan na fara shirin tafiya don tace da safe zamu tafi garin mu.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA YA KARANTA ALLAH NAGANIN KI ZAI KARABAN MIN BASHINA GOBE GARE KI,,,,


A LOKACIN MUKE,,,,


Amaryam kan ta tare gidan angon ta Atiku maria haka ta kwana a cikin bakinciki ranan don tashin hankali.
Washegari da safe ko kafin ta gama barcin ta data saba tafito ta samu har amarya ta fito ta gyara gida ta dora ruwan zafi a wuta.
Ganin maria ta fito lokacin tana tsaye tana tara kwanon da tukanen maria, da yaran ta suka bata tun safen jiya har yau.
Bingidan maria tayi da kallon yadda ya sha gyara ko ina, ina kwana ?
Amarya Sadiya tace mata, cikin haushi ta amsa mata tace lafia kawai,
Ta wuce zuwa bayi ta kewaya tafito tafara alwala duk abinda amarya keyi tana binta da ido.
Bazata gwada wa amarya sadiya shekaru ba itma dai sadiya din zasu zo sa,a daya da maria din.
Kafin duk yaran maria su tashi har sadiya ta dama kunu, ko sai ga maigidan ya shigo wanda tun fitan shi masalaci suna can suna zikiri bai dawo gida ba sai yanzu da gari yadan haska.
Yana shigowa ya samu sadiya ta zuba kokon da ta dama ga sabbin robobin da tazo dasu gidan.
Inda taimashi sannu da dawowa ta dauka takai katon roba mai kunu kofan Maria ta girke masu ta dauki nata da mijin ta tashiga dashi dakin ta.
Sai gata tafito da sabon bucket a hannun ta ta deban mashi ruwan wanka takai mashi bayi.
Zata fito ne ta samu maria ta idar da sallah tafito waje tace mata ga kokon ku nan a kofa na aje maku sai ruwan wanka dana sa su fito su fara wanka kada su makara zuwa makaran ta .
Wani kallon banza maria ta watsa mata tace da baki gidan wake basu ruwan wanka dama kada ki kawo min sallo da iyawa don gidan kika shigo.
Kuma ki koma ki dauki munafukin kokon da kika aje don mu baza musha abin sihiri ba wayasan inda kika fito da tarkacen tsiyan ki da zaki wa mutane sihiri kice wai kin dama.
Haba yar uwa gumbane fa akayo muna shi wanda zamu amfana dashi kwana biyu a gidan nan.
Munafuka mun san irin ku wazaki cuta sai dai shi daya daukowa kan shi, bata karasa ba Atiku yafito daga dakin amaryan nashi.
Yace ke Maria wallahi ki shiga taitayin ki idan kikace zaki tirka min tsiya agidan walle na lahira nafin ki jin dadi.
Ke ga kina iskancin ki nakawo ijjiya na saka maki ba fa fin karfina na kin yi ba.
Raga maki dai nakayi don wa yanga yaran dakin ka gani ko suma yaran ba tausayin na kikayi ba da kina tasaya masu da baki kaisu mahalaka ba ke illata masu rayuwan su.
Duk wace tace tashin hankali da diban albarka zata aza min agida bani daukon shashan ci yanzo don zama da mace ba dole na ba.
Aliyu kai, Aliyu ina kake na ?
Sai ga yaron ya fito


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login