Showing 366001 words to 369000 words out of 373688 words
Chapter 123 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
bane ai kinga dukiyar mutane ne nauyin shi ya hau kaina dole na kula masu da abinsu ko?
Nafisa ce tashigo gidan da alamun damuwa a fuskanta nan muka zauna da ita ana hira suko abinci suka wuce ci a dining.
Yana gamawa ya shiga ciki ya dan jima bai sauko ba yana sama koda zai fito ya sauya kaya jikin shi a lokacin.
Tun bai kai zaune ba ya soma magana yana cewa gaskya kauna ya kamata ace kifito da miji hakana kiyi aure na hada ku da Amira dama yan sa, a daya kuke kinga kowa sai ya huta abar Rukaiya har su karasa nasu karatun.
Cikin wani langabe kai tace ni yaya wama zai aure ni kawai ni na fitar ma da rai ga wani aure can
Da sauri nace haba anty ce astangafurullahi mana yaya zaki magana kamar ba musulma ba dake.
Tace to madam wakike gabin zai aureni a haka yadda nake duk masu zuwa gurina ba da sunan aure suke zuwa min ba sai dai da tasu bukata kawai.
Gaba dayan mu tausayi tabamu ga maganan ta don mun san cewa gaskiya ta fada maganan ta.
Amma kuma ai abin Allah ba a yanke kauna a gare shi nace anty gaskiya yaya ne ki natsu ki rage wasu halaiyar ki ko Allah zai tausaya maki.
Don kinga ai Allah miskaraziratin ne ba abinda ya gagari ubangiji sai kinyi mamakin irin mijin da Allah zai kawo maki idan kin natsu.
Kafin tabani amsa wayan ta yai kara jin sunan wace ta kira da Raye yasa na gane da Raiha take waya a lokacin.
Tambayan ta tayi tana ina tabata amsa da cewa gani nan gidan su madam ina shan sanyin A C.
Tabata amsa da gata nan tafe tana gamawa yake ce mata kinga ni maganan ki bawai ya karbu bane gareni fa kiyi tunane a kai ki gyara halaiyar ki Nafisa .
Mace fa dan guntun lokaci ke gareta tun anayi daku watarana masu neman naku gudu za, suyi su koma ga
wasu yan matasan
Ta amsa a marairaice da tau naji yaya insha Allahu zanyi kamar yadda kace amma zaka dinka min hijjabbai na fara sakawa ko?
Murmushi yayi yace gatanan yana nufin ni zata dinka maki ko guda nawa kike so kaunata.
Nidai kawai ki natsu ki daina wanan halin please.
Shigowan Raiha ne yasa muka daina zancen suka gaisa da shi ya mike zuwa babban falon shi na waje da yake taron baki a cikin sa yabar mu nan zaune a na cikin gida da waya a hannun shi yanayi.
Nan muka fara hira dash nake tambayan Nuriya suke ce min wai tabi wani saurayinta dan Ibo sun tafi lagos tare.
Banji dadi ba na kasa boye bacin raina nake cewa haba dai haba ace kuma mutum yana hurda da harda wanda ba musulmi ba kuma ai abin yayi muni gaskiya.
Raiha tace madam kawai dai Allah ya gafarta muna zamuce don dai gaskiya nima yanzu da hankali yafara zo min na gane hakan ba daidai bane.
Ni yanzu fatana kawai Allah ya kawo min miji wanda zai soni tsakani da Allah wallahi ko yaya yake zan zauna dashi na natsu bakiga yadda al, amarina har yasakawa iyayyena cutan hawan jini ba.
Tace to mazan ne yanzun sai a hankali wallahi na rasa wanda zaizo ma da tsigar so na gaskiya bada bukata ba.
Nafisa tace maganan da muka gama ke nan da yayana kafin ki shigo abinda na fada mai ke nan kema yanzu sai gashi kinzo dashi.
Tace wallahi muna son auren bawai bamu so bane to amma wazaka aura shine matsalan.
Istigifar bai bar komai ba ku koma ga Allah kwana biyu kuga ikon Allah wallahi bana jin dadin irin wanan rayuwan da kukeyi yanzu ya kamata ace kunyi wa kan ku fadan hakan.
Shi yasa nake son ki madam wallahi kece kawai zan iya cewa a yanzu kina tsayawa ki nusar da mutum hanyan alheri bayan kowa ido yakawo ya saka muna.
Ana jiran da garin Allah ya waye kai wani abin asha asakaka ga faifai a tallata ka.
Yaya sadauki ne yashigo yana ce min sai ki shirya don muna da bakin da zasu duba gurin da za, a gina kamfanin shimkafa a garin nan
Gashi sunce min ba, a hotel zasu sauka ba anan gidan zasuyi masauki don haka sai ki samo wanda zasu yi aikin abinci idan kuma bayarwa zakiyi ai masu duka daya.
Kafin ma ya karasa zancen shi sai cewa Raiha tayi bagamu ba yaya aikin may mukeyi dabaza mu yi ba mu.
Baiyi magana ba don na lura hankalinshi bai kwanta da al, amarin Raiha din ba wanda shine bai fahince ta ba sauki kaine da ita sosai.
Amma shi yana ganin sune suke jefa yar uwarshi a cikin wanan mumunan harkan da sukeyi tare.
Bai san tafi su zama shedaniya ba don ita ta hure fitillar ta sosai ma fiye dasu.
Mun jima dasu muna tatauna abinda ya dace muyi da wanda zamu saya na bukatun mu.
Har sai bayan sallah magariba suka tafi mukai sallah suna cewa idan an shirya na kirasu.
Bayan yashigo gidane yake fada akan cewa may zaisa na yarje ma wa yan nan mashiririta suyi mai aikin abincin bakin shi yaushe ma suka zauna balle su san yadda ake girki su.
Nace haba yaya sai kace ba mata ba su gani kuma ga iyya a gurin ai zamu taimaka masu da wani abin.
Yace da sauri No no kada ki soma cewa zakiyi aikin komai kin dai san yadda condition din ki yake please kada ki fara ki taba komai idan ma bazasu iya ba sai a kira wasu suyi final nace ballema insha Allahu zasu iya duk abinda suka lissafo zasuyi din.
Bai kara magana ba haka muka bar zancen don yaga na aminta dasu sosai yasa ya kyale badon yaso ba.
Izuwa yanzu alherin da sadauki yaiwa iyayyena bazan iya lisfoshi ba don muna waje sun tafi sun sauke farali ga gyaran gida da abin sana, a da ya sayawa kowan su a sanadiya na iyayyena da yan uwana sun fita a cikin talauci yanzu wanda hakkurina da biyayyana ne yajawo muna wanan alherin haka.
H
Yan uwa dama yan garin mu sukan zo neman alheri a gurina wanda nakan yi masu shi gwargwadon halina.
Lokacin zuwan bakin shi yayi bayan sati ya zagayo yabani kudi masu yawa akan abubuwan bukatan su.
Ban masu kyata ba na ba kudi fiye da wanda za, a kashe sosai suma su karu daga ciki suka shiga kasuwa saywn abubuwan bukata duk da wasu muna dasu a gida.
Ranan har anty maryam da Rukaiya sai da suka zo da mummy tare akai aikin komai dasu na fita kunyan baki yadda ya dace sai da aka hada abinci kusan kala goma sha biyu nau,i daban daban suka kara gyara katon falon muna na baki an saka kamshi da komai a falon yadda ya dace ayi.
Bakin basu shigo gida ba sai misalin karfe uku na rana dirin motocin da mukajine yasa muka gane cewa gidan mu ya dauki manyan baki yau don har dasu jiya da alaman akwa wasu manyan kusa a cikin su ke nan.
Nan aka shiga fito da kayan ci dasha bayan wanda aka kai masu da farko wa drivobin su.
Gida ya rude da hayaniya sai kai da komo su Anty Nafisa sukeyi a gurin ana yaba aikin da sukayi.
Allah da ikon shi a wanan sanadin Allah ya hada su da masu son su a gurin sukai wa yayan su magana kan ya basu kannen shi din nan yace yabasu.
Wasa wasa magana ya zama babba don ita Nafisa ta hadu da wani ustazune manager din wani babban company dake garin Abuja.
Ita ko Raiha wani sojane babba wanda gwaunati ta turo shi as a security guard na kasa ya kyasa mata.
Amira da mama tace tazo ta taya mu aiki tace ita ba yar aikin kowa bane ba inda zata tafi nan mama ta ganta ta kyaleta.
Amma daga baya da taji sun ba da tukwaicin dubu dari biyar wa masu aiki sai kuma ta shiga fada tana ganin laifina
Wai dama ni yar bakin cikine shiyasa na gaiyato yan iska su cika min gida shiyasa ita bata tafi ba.
Karshe kuma sai ga zancen auren Nafisa da Raiha da taji Allah ya hadasu da wasu manya sai dai ba yara bane su.
Nan kuma ta shiga zage zage kamar mahaukaciya wai ta yarda ni yar bakin cikine ta karshe sosai don ban son ta da arziki nafi bukatan komai sai a gani a gurina kawai.
****** ********* ******
Bukin anty Amira ya taso sosai ba kama hannun yaro don haka muke ta zirga zirga ba hutu don mu ke gudanar da komai akan bukin duk da gwatsale ni da takeyi tana nuna bata bukatan saka hannuna acikin al, amarinta sam.
Hakan bai sa na daina duk wani abinda nake da niyar yi ba don ba don itace nakeyi ba dama don Allah nakeyi da mijina da kuma mahaifan su.
Bata san ina da rana a gare ta ba sai da masu zuwa ganin dakin da za, a saka mata kaya sukaje suka dawo da labari mara dadi don ashe a family house za, a aje ta.
Kuma ga dakunan ba wasu dakuna bane maigirma a jere suke ita da uwargidan ta wace yar uwace ga mutumin da zata aura.
Da labarin yazo ba karamin tayar da hankalin ta tayi ba sosai nan ta tuburewa mutane akan Ibrahim ya cuce ta don cewa yayi gida zai kama mata haya don may yazu zaice a gidan su zai aje ta.
Sosai ta tayar da hankalinta akan bazatayi auren ba ta fasa hankalin mama yai matukar tashi gashi an gama komai akan shirin buki ga yan uwa na nesa har sun fara hallara a gurin bukin.
Kuka wiwi takeyi akan ita kan wallahi ta fasa sai dai akai wata ba ita ba don bazata wanan gidan da ake bada labarin shi ba babu tsari.
Mama kuma da yan uwa sun kafe kan lalai sai anyi auren nan sai dai ta mutu idan an kaita don bazata basu kunya ba.
Ganin matsalan yai yawa ga tashin hankali ga fuskan kowa idan ka duba ya sa na tashi daga inda nake zaune lokacin cikina yai girma sosai wata bakwai saura kwana goma nake.
Dakin da take na shiga na samay ta ta kifa kai ga filo ita kadai a cikin dakin tayi buji buji da ita kanta duk a hargitse dashi.
Zama nayi bakin gadon don bazan iya tsayi tsaye ba a yadda nake lokacin don karfi hali kawai nakeyi da kaina.
Duk da taji anshigo dakin bai sa ta dago daga yadda take a kwance ba cikin yanayin tashin hankali.
Cikin yar siriryar murya nace Anty Amira ki tashi muyi magana musan mafita akan wanan al, amarin don kuka ba shine mafita yanzu tunda kinga mama ta kafe akan sai anyi auren nan ba fashi.
Jin muryana yasa ta dago kai a cikin fushi tace Bintu for god sake ki barni naji da abinda ya damay ni please ke har wani taimako zaki iya yi min ?
Wani matsayi ke gare ki da har zaki dauka zaki iya taimaka min dashi a matsayinki ko don kawai kinga kina auren dan uwana kina juya shi yadda kike so to ni ba shi bane ko maji ki sani.
Murmushi nayi kawai nasan ban taba fari a gurin ta amma ni don Allah kawai nai niyar taimaka mata.
Nace a fili ba matsala anty ni don Allah nazo gurin ki don mu san mafita kawai idan kina da lokaci ki tashi muyi magana dake mu san abinyi tun ba, a kai maki kayan ki ba a wancan gidan yawan.
Wani kallo ta watso min kafin tace ina sauraren ki nace nagode naci gaba da fadin nasan bawai baki son Ibrahim bane a yadda nasan kun dade tare dashi kuna soyayya.
Kawai dai wanan matsalace ta gurin zama yasaki bacin rai irin haka sai nake gani idan yace zai canza maki gurin zama duk wanan matsalan zai iya wuce a tsakanin ku tunda soyayya ce ta hada ku ba kiyayya ba.
May kike fadi mutumin da ya kafe akan shi baida kudin da zai karasa ginan shi kuma baida wanda zai iya kama min hayan irin gidan da nake so a yanzu.
Nace insha Allahu anty idan don gurin zamane na rokeki Allah ki kwantar da hankalinki ayi wanan bukin cikin farinciki.
Yadda kowa yazo lafiya don farin ciki ya koma gida da farinciki a ranshi anty baku gaji yin kunya ba a rayuwan ku balle kuji kunya don Allah ni dai yanzu abinda nake so shine ki kwantar da hankalinki ki koma kamar babu abinda ya faru a baya don marasa da suyi kunya don yanzu kinga ido aka sakawa mama aga yaya zata kaya ana farin ciki zaki shiga gida mai kuntatawa.
Wani kallone takara watso min tare da cewa wanan shine dama maganan da zaki fada min din.
Nace eh anty don Allah tunda kuna son juna da Ibrahim kiyi hakkuri ki daure ayi wanan abin cikin rufin asiri insha Allahu bazaki zauna a wanan gidan ba.
Tsuki taja tare da marya da kanta a saman filo tace na zaci wani shawaran arziki kikazo min dashi har na bata lokacina a kanki haka.
Na dade a zaune ba tare da tajuyo gare ni ba ga wayan ta dake ta verviration taki dagawa.
Wanda nasan ba kowane ke kiranta ba a lokacin sai angwan ta wanda yake a cikin tashin hankalin kan cewan da tayi bazatayi auren ba ta fasa.
Nagaji da zama ina batun tashi anty maryam ta shigo dakin kallon mamaki tai min ganina da tayi a zaune ga maidakin ma kamar bata san ina zaune a gurin ba.
Tace ke kuma may kikeyi anan ina can ina neman ki mama tace wai wanan kayan kitchen din da aka fitar a mayar dasu a kwali tunda babu inda za, a saka su a gidan.
Tajuyo cikin zafin rai daga inda take a kwance idanuwan ta sunyi ja jajir dasu don kukan da tasha sosai.
Tace sai naga iban da akewa shirin auren da har ake maganan rage wasu kayan daki can akai badai ni ba.
Nikan da kyat na mike tsaye muka fita maryam tana mata dariyar mumuke muka fice.
A gajiye na bar gidan don dare yayi a lokacin yaya Sagir ne ya kaimu gida da kan shi don ban driving saboda matsalan cikin dake jikina.
Sai da nai wanka nafito falo na samu Iyya tana gyaran abin da zamu karya dashi tana kwaba abin da zatai muna sanasir dashi.
Ina zama ana kirana ga waya yaya sadauki ne wanda bai ma kasan yai tafiya a lokacin.
Mun gaisa yake tambayana ko mun dawo gida ko muna can gidan su mama har lokacin .
Nace mun dawo tun dazun har munyi wanka gani a falo ma zaune zan sha magani na kwanta.
Yace maji ta kirani tana fada min iskancin da wanan mara hankalin kewa mutane tun jiya wai ta fasa auren ko ?
Nace yaya bafa fasawa tayi ba kune dai baku fahince ta ba bawai bata son Ibrahim bane a, a gidan da za, a kaita ne bai bata ba don a cikin family house din su ne inda uwargidan shi take zaune.
Kaga kasan halin anty Amira da tsandan mutane bata son yawan hayani ita tafi son ta zauna koda yaushe silent bata son yawan hayaniya.
Ya karba kafin naci gaba da fadin don taita mugun hali ko?
Nace haba yaya ya kamata a taimakawa anty please bai kamata abar rayuwan ta a haka ba don Allah.
Yace ok yanzi so kike nima na biyewa haukan ta nace a fasa auren taita zaman gida ko?
Nace ba nufina ke nan ba yaya abinda nike nufi shine ka taimaka da baiwan da Allah yai ma na falala ka sama mata inda zata zauna don wanan auren nata yai karko kamar na kowa please ?
Ban fahince ki ba Fatima kima nifin nine zan bada gurin da Amira zata zauna da mijin ta ko may ?
Nace ai ba mijin ka zakaiwa ba yar uwar haihuwan ka zaka taimaka kamar yadda Allah ya taimake ka kaima ka sama mata gurin zama yadda take so.
Don yin haka kawai shine shedan dan uwata ya samu kuma mai taimako ne ga jinin shi don kaga ba Amira ba kawai wallahi har mama hankalinta a tashe yake akan wanan magana daurewa kawai mama keyi don ta bata karfin gwiwa amma ran mama baiyi dadi ba ace a wanan gidan za, a kai Amira gaskiya.
Yanzun dai na fahince ki yace nine zan aurar da ita kuma na bata gurin da zata zauna kamar na matsu da ita a gida ko ?
Nace wallahi yaya ba haka nake nufi ba ni nufi na shine kawai ka taimakawa rayuwan su tunda Allah ya hore ma abinda zaka iya yin haka din.
Idan kai haka ba karamin lada zaka samu ba har a gurin Allah don shine shedar zumunci yanzun fa kaine uwar mu kaine uban mu gaba dayan mu har kai.
Amira ba ko Nafisa ce da irin wanan matsala