Showing 189001 words to 192000 words out of 373688 words

Chapter 64 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

Advertisement

a hanya yace mummy bani son wanan yawan fitinan da kukeyi da Umma ko don hallin da baba yake ciki yanzu.
Kai Sadauki wallahi yaya ta faye abin haushine ita kullun sai ta mulki mutane tamayar damu da diyan mu abin banza.
Nikuma bazan yarda tayi zaune shirim tana zuba muna iko da mulki ba kaman ita ta aje mutane.
Hajiya maijidda suka samu suke mata abinda suka ga dama a gidan gaskiya ni ban daukan hakan.
Indai sheri ne ai ta matsa yanzu tunda kazo kaga Nafisa asibitin nan da sauri maji ma tace yaya akayi.
Tace may nene ba,agiba yan hisba suna neman su sun hada party na iskanci a gari, akai ta shedana da iya shege.
An kama yan uwanta su su gudu su masu party amma ce uwa tayi wai zata Abuja ne gurin Atika kaunan ta.
To ko shine ya jawo wa Alhaji wanan abin hjy Kubura tace shine ma da dan banzan ga na wurin Asiya Ahmad dayaje ya dauko rikici.
Dole Alhaji ya sayar da kayan shi har motar shi ya biya milayan biyar da wani abu.
Sun dauka ba,a sani bane kawai don mutum baison ya fadi a ce ga bakin shi akaji.
Amma ni Nasir dina yake fada min tun dashi ya boye muna bai son a sani amma ai sune suka jawo mashi hawan jinin ba wani ba.
Daga gaban mota sadauki yace to amma may yasa Baba bai fada min ba duk wanan zancen.
Tace ina zai fadi kasan shi da zurfin ciki ai in sun kashe shi ai an huta ko ?
Har suka isa gida ba wanda yai magana a cikin su sai dai kowa da abinda zuciyan shi ke saka mai.
Waahegari bai zauna ba sai shirin tafiya yakeyi na iyayyen shi, Imirana yace aikin banza ne wanan shi yaushe yake da kudin da zai fitar da Baba waje har da matan shi.
Sai ranan tafiya, ne suka tabbatar inda suka shirya sai kasa mai tsarki, ba tare sukai tafiyan dashi ba zai samay su daga baya amma komai da za,ayi a can ya hada su da abokin wasan shi dan kwallo dan kasan sadiya da yaya sagir suka tafi.
Tafiyan su da kwana biyu duk gidan babu dadi haka dai muke zaune amma sauran yaran sai harkokin su sukeyi.
Na dawo daga sayo muna kayan miya zan shigo gida ban san da mutum tafe ba sai cin kara nayi dashi.
Ina daga kai ya wani daga min gir irin na yan iska, har na zauda shi zan shige ya rike min hannu yana fadin.
Yau shigeya kobaki so sai na kwashi gara gare ki, gidan nan sai da in munafukan uwar ki ta dawo tayi abinda zatayi.
Dama na dade ina son in more wanan lafiyen jikin naki kafin wacan gara da zaki aura ya more.
Sai naji ya jawoni gaba daya yana kokarin daukana zuwa dakin shi nasa hakora na iya karfina na cije mai kunnen shi da sauri ya sake ni ya makure yakai min mari gashi ba wanda yafito daga cikin gida balle ya taimake ni.
Na samu wuyan hannun shi na kara kaimai cizo iya karfina yaji zafi ya dinga kai min nashi a bakina.
Naji zafi na sake sai nishi yake ban san lokacin da yanka wani irin ihu ba da karfi.
Yakara cakumoni na samu sa,a na murde mai gaban shi iya karfi na ya yanka wani irin ihu daidai lokacin, sadauki dake jin kamar ana danbe a waje daga dakin shi ya leko,
Zan gudu yakara finciko ni nakara kai mai wani cizo tare da kamawa da karfin Allah.
Daidai nan naji an kai mashi nashi a bakin shi sai da ya fadi ta baya zaune dirsha.
Yace dabba kawai sauna mara hankali da,wayo kai dabban wani gari ne karasa wanda zakaiwa haka sai Fatima da take zaman kaunan ka.
Tir da halinka halin dan akuya kawai kayi girman banza wallahi, ji ka raggo kawai ji yadda ta mayar dakai jina jina amma baka ji kunya ba kace sai ka danne ta da karfi.
Ya furzo miyan daga bakin shi duk jini ne kila ma hakkoran shi sun zube ne.
Ya juya inda nake tsaye ina kuka yace dauki kayan ki ki shiga gida ke kuma.
Na duka na dauki ledan da na sayo kayan miya duk sun watse a kasa da takalmana da suke warwatse a gurin nai cikin gida da kuka na barsu nan suna fadawa juna magana.
Yana ce wallahi ba dan kwallo kake ba sai naga bayanka a garin nan yace Bisimillah shege ka fasa in baka ga nawa ba ni zanga naka ai.
Sai lokacin naga yan gidan duk sun fito waje ashe suna tsaye cirko cirko cikin tashin han kali.
Ina shiga gida na zube kasa gaban Anty Amirah ina wani irin kuka mai tsuma rai da ban tausayi.
Tana kukatake tambayana bai maki komai ba dai ko na girgiza kai cikin kuka nake fada mata ,a,a yaya sadauki ya ceceni gurin shi.
Maryam tafita ta dinga kantara mashi zagi da,ashar kamar ranta zai fita sai da sadauki yazo yace ta shiga gida hakanan.
Wayan shi ya fitar ya kira Bashar yazo ya samay shi a cikin damuwa ya yasamu abokin nashi.
Yana fito ya samay shi bakin kofan gida su dama Bashar yafita da motan shi shiyasa Imirana bai gane yana gidan ba a lokacin.
Yaya akayi man?
Ya kara cewa wai may ke faruwa ne naganka haka a ya mutse?
Yace hajiyan ka tana garine Bashar yace eh yace zan kwashi yaran nan nakaisu gurin ta har su baba su dawo.
Anyi wani abune ?
Yabashi amsa da anyi a takaice.
Ina fito da kayana falo ina fafin wallahi Anty Amirah ban kwana a gidan nan garin mu zan tafi sai gashi ya dago labule ya shigo falon .
Fuska a daure yace ke Amirah maryam ku hada kayan ku dake kuzo na kai gidan hajiyan Bashar don gobe zanyi tafiya bazan barku a gidan nan ba.
Yan gidan na kallo muka fito da kayan mu mun kashe komai na,wuta a part din namu tare da rufo kofa muka fita daga gidan.
Daga cikin diyan mama Asiya ta buga ma mutanen saudiya waya ta fada masu halin da ake ciki a gidan.
Anso boye wa maji amma sai hjy kubura ta tsinci ana maganan itace ta fada mata abindake faruwa da mu.
Hankalinta yai matukar tashi sosai ranan bata iya barci ba, don gani take kila yakai gare ni boye mata akayi kawai.
Gashi tayi kiran layin mu duk bata samay mu ba har sadauki din bata samu ba.
Ita ko Umma fada takama yi wai don anga bata gida za,a kullawa dan ta sheri haka.
May Imirana zai yi da wanan kwailar yarinyar mara fasali sai fari, duk tsiyan da aka kwaso don anga Allah ya azurta ta da yara shine ake mata hassada a gidan.
Sai ga kanin Imiranan ya bugo mata waya yana kuka yace gaskiya Umma abinda yaya yaki baida kyau fyde wa ya tashi yiwa Bintu yau saida yaya sadauki yacece ta kuma yace sai ya kashe yaya sadauki ya fadi a gaban kowa.
Nan ta hau yaron da fada tace har dashi ke nan za,a kullawa dan uwan shi sheri a gidan.
Yace wallahi Umma ba sheri bane a gaban mu akayi baki yadda akai mai jina jina ba wallahi zaban kunya.
Kashe wayan tayi don bata iya sauraren takaici gashi a gaban hjy kubura suke wayan.
Nan tahau banbami cewa dama ankawo sune don an hada baki a tozarta mata da acan bayan ta.
Hjy Kubura tace ai ba wanda yasaki zuwa ko kin manta fada dakikayi kan sai kin zo dakin zauna gida da yara ai da duk haka baifaru ba.
Amma kun kwaso jiki kunbar yaran can maynene ba zai faru ba tunda basu da tarbiya.
Nan wani sabon fitina ya fara kamar ba a kasan saudiya suke ba saboda bakin kishin su.

Muna gidan maman Bashar matar bata da matsala itama tana da yan mata guda biyu sai wata yar karamar yarinya jikan ta.
Bamu da matsalar komai a gidan don tana bamu kulawa yadda ya dace uwa tabawa diyan ta.
Gasu da addini duk da sun girma basubar zuwa isalamiya ba daukan hadda da sauran litattafai.
Zazzabi nayi na kwana biyu da wahalan da nasha Bashar da maman shi suka kaini asibiti sai da nasha allurai na mike.
Hankalin mu a kwance muke komai a gidan babu tsangwama kuma su kadaine a gidan.
Zamu zauna da uwar muyi hira da ita cikin sake jiki babu ruwan ta.
Sadauki ko ya samu jikin Baba yai sauki sosai don har yafita yai dawafi duk da da sauran jikin shi.
Sai dai yasan cewa Umma tana hake dashi don irin yadda take mashi tunda ya iso kasan.
Bai kula taba don maji taja shi a gefe tunnisowar shi take tambayan shi abinda ya faru.
Hakalin ta ya kara tashi sai dai da taji cewa ai yaranta yanzu suna can uguwar arkilla gurin mahaifiyar Bashar hankalin ta ya kwanta.
Kwana shi uku tare dasu ya tafi garin Riyahd ya barsu gurin wasu yan team din kwallo.
Nan ma ya,bugawa wasa inda ya samo riyar masu yawan gaske don yan kan har taya shi sukayi akan yadawo kasan su da wasa amma yace masu kasan shi ma suna bukatan shi.
Ya dawo suna shirin tafiya ya ba su kudi kowa tayi tsaraba wa yan uwa da yaran ta.
Umma tai matukar rudewa da irin kudin daya basu a can hankalinta ya tashi tasan in bata zake damtse ba sai wanan yaron ya zarce tunanen ta.
Maji ta samu kudi ta sayo muna kaya masu kyau da,tsada zannuwan gado masu kyau da sauran tarkacen daya dace a sayo.
Sai kuma Umna abin ya tsone masu ido wai yabawa uwar shi kudi yafi nasu ya nuna masu banbancin cewa ita ce ta haife shi ke nan.
Maji dai tana gyaran kayan ta sai murmushi tayi kawai batacewa mama Asiya uwa ka iya komai ba.
Don umma ta zugata itace ta fito fili tana maganan cikin hasala da bacin rai.
Sai dai duk iya shegen su basu yarda suyi a gaban Alhaji don yanzu zaici masu mutunci ne.
Satin su biyu da kwana hudu suka iso sokoto zakace ba jinya sukatafi ba da bauta don duk suyi kyau abinsu.
Ga zancen tafiyan su ya bi yan uwa da abokan arziki kowa ya san da cewa dan kishiyan su ne da suke kira mashayin gidan su yakai su saudiya umar da jiyan mijin su.
Saidai kan kowa na ciki na ciki jira ake a dawo gida a zazzage balain da aka kullo.
Kafin su dawo mun shigo mun gyara ko ina na part din mu muka koma gidan su Bashar muna jira su dawo gobe.
Mahaifiyar su bashar tasa ai muna gyara jiki kitso har kumshi saida ta sa akai muna, siffa mai kyau mun koma kamar wasu amare da mu.
Sai bayan sun dawo har sun huta yaya sadauki yaje ya,kwaso mu har mahaifiyan Bashar din ta rakomu gida.
Mun samu gida ya rude da murnan dawowan iyayyen su ko wani daki sai hayaniya akeyi.
Gaba dayan mu muka fada jikin mama cikin murna da farin cikin ganin ta a lokacin.
Maman su Bashar sai kallon mutake cikin sha,awa nan mana ta fara mata godiya, kan karamcin da tayi mata na rike mu a gidan ta.
Tace haba ai ba komai yaro ai duk na kowane dama absan haka tun farko da can suka zauna harku dawo.
Yaya sadauki da Bashar na zaune sai kallon mu sukeyi duk nabi na takura da zaman su a gurin.
Na mike tare da fara daukan jakkunan kayan mu da muja dawo dasu yanzu zuwa cikin daki.
Maji tace Fatima bazaki bari har ki huta ba nai dan murmushi nace mama bari na shiga dasu kawai.
Ina shiga maman Bashae tace ai Fatiman nan taki akwai kokari wallahi ko can haka nake fama da ita gurin aiki.
Mama tace ta riga ta saba bata son zama da kazanta ko kadan .
Ashe aure zatayi bada dadewa ba jiya nake jin suna mata sheri wai angon ta yazo yaga wanan kwalliyan nta sai nake tambya suke fada min an kusa bukin ta har an kawo kayan lefen ta.
Hakane hjy nice ban aika maki ba.
To Allah ya sanya alheri ai mijinta yai sa,a ya samu yatinyar kirki ta san ya kamata sosai.
Kai wanan yarinyar dai shu,umace kowa sai kaji yana yabonta ko akan may oho.
Bai zaci maganan zucin shi yafito fili ba sai jiyayi Bashar na fadin kaine kake ganin ta shu,uma amma ai Fatima mutunce wallahi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,,


IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA, BA MU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAN MUNA,,,,,


Bayan dawowan su maji daga saudiya da yan kwanaki jin ba wanda ya tayar da zancen abinda akai min agidan,
Maji ta kawar da kaiwaici a idon ta inda ta samu Imirah ya dawo daga kasuwa ke nan zai shigo gida take ce mai,
Imirana ji mana sai ya dan waigo yai tsaye kerere yana kallon ta cikin rashin mutunci.
Yace ina jin ki,
Ganin babu mutunci yanzu a tare dashi yasa maji cewa ,yanzu Imirah baka ji kunyan abinda kayiwa yarinyar nan ba da bamu nan?
Amatsayinka na babba a gida anbar maka amanan yaran nan shi ne kuma kaida kanka kai kokarin keta mata haddinta?
Fuska a daure yace dama don wanan maganan kika tsayar dani ?
Saurayi nake ita kuma nudurwace zan iya shigar da kai na akanta ko hakan kuma illa ne.
Murmushin takaici maji tayi tace amma tir da halinka na dan akuya, halin maha,inta.
Idan zina abin yine jeka ka nemi yar uwar yin zinanka can kuyi tayi amma ba yar mutane da aka bani amana ba.
Murmushi yayi yace Maji kada kiga laifina yar taki ce da shegen kyau wanan aiba komai bane,
Allah ya shirye ka,Allah kuma ya tsare amma ni dai Hauwa,u ina maka kashedi akan diyan mutane a gidan na wallahi muddin ka kara yi mata wani abin tashin hankali again zan ba mutun mamaki don shiru ,shiru ba tsoro bane kuma in mutum bai jiba ya gwada ya gani.
Sai muryan Umma daga bayan su akaji tace tau isassarsa masu gida wallahi duk sherin ki baki na kakan ki ba.
A hir din ki akan diyana ina fada maki Hauwa,u ki sakan min maran diya don bani nasa danki yayi tambada ba abaya.
Haka,kawai don yar kauyen diyarki zaku saka min yaro gaba dasheri don kawai a bata mai suna.
To wallahi ta Allah ba taku ba kuma karya kukeyi nagaba yayi gaba nabaya sai labari.
Kuma kijawa karuwan diyar ki kunne da take kokarin cusa kanta gare shi tayi kwantai a kauye ankawo ta gari ana neman mashinshini a cafke.
Murmushin takaici maji tayi tace kaice yaya a matsayin ki na uwa kuma diya mace kin san zafi da munin irin abinda Imirana ya tashi aikatawa yarinyar nan amma idon ya rufe da kin gaskiya.
Babu komai ai Allah ba azzalumin kowa bane yana sama yana gani duk bayin shi.
Ta juya inda Imiran ya fara tafiya tace wallahi kaji na fada maka duk ka sake kokarin ketawa yarinyar na hadin ta sai kayi mamakina a gidan nan.
Tashige cikin part din mu duk muna jin yadda suka kwashe da Umma da dan ta maji tace kai Allah dai yasa kin kusa aure ma kowa ya huta, ki bar wanan gidan namu mai tarin fitina cikin shi.
Muryan Baba ne daga waje yake fada kamar haka amma dai ke kan anyi uwar banza wallahi.
Yanzu ashe abinda yaron nan yaiwa yarinyar nan ke nan bansani ba shine har kike fada don kunya bai ishi idon ki ba ke,
Ida da yarkice wani katon gardi haka yai niyar illantawa haka zaki fadi an mashi kazafi ne ba gaskiya bane hakan
Dama ai nasan hakace zai kasance muddin kaji ba ka tsaya kai bincike irin yadda ya dace,
Tunda da matar so dinka ake fitina to ku sani ni diyana basu da gadon iskanci masuyi dai kowa yasan su don haka sherin mutum yabishi can cikin kayan shi .
Haka Umma ta tare ta hana Alhaji ya,tsaya yai fada akan wanan zancen don idan ya matsa zagine da tonon asiri zai dawo akan sadauki da,uwar shi .
Wanda yanzu daga uwar har dan tausayi sukw bashi sosai don duk abinda zasu gujewa gudun magana agidan suna kokarin yin shi don kimar su ta riga ta zube ,
Su Umma da mama an samu gurin zagi da gori da habaici koda akan da tsinke ne.
Shiyasa yakan kawo ido yasa,wa Umma inda ita ko tana ganin kamar tafi karfin kowane a gida sai yadda tayi da kowa agidan baki daya.
Hjy kubura ce kawai bata samu ta mallake yadda ranta ke so ba amma ko ita din ba laifi don bata iya kifar mata da,gwaunati a gurin mijin su ba.
Amma wanan munafukan Hauwa,u zamani amarcin ta Alkah daine yanufi takai wanan lokacin a gidan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login