Showing 333001 words to 336000 words out of 373688 words

Chapter 112 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

da sukai muna ya kalli idon Alhaji yace ba zai aura wa yar shi mashayi ba.
Kaje duniya tana da yawa ka samu irin ka yar shaye shaye ka aura shi yafi ma.
Shine yanzun don baida kunya zaice wai wani a tayar da zance to nima yanzun nace ban yarda ba duk abinda zaiyi yaje yayi amma wallahi baka auren Rahama.
Wa yanda sukaje suka bata ka garesu ai suna da diya yaje ya aura masu ita mana.
Wai ko akan zancen kake son tura Fatima gidane wai ?
Yace wallahi mama ban son Fatima ma tasan da wanan zancen shi yasa nace zan tura ta tafi ni kuma sai na tafi bashi ke nan ba.
Idan Fatima ta samu wanan labarin nasan akwai rikci sosai a tsakanin na da ita wallahi.
Bata ma komai amma baza,ayi ba na fada maka yace nima maji yanzu ba ida zan kai Rahama kuma don ta fita raina kwatakwata wallahi.
Don dai ka fadawa Fatima zancen tafiyan ne wallahi da ba inda zaku shi din may wai da har zaka gujeshi ?
Idan ma kun tafi ai dawowa zakuyi dole tunda ba inda zaku sai gida tun wuri zan ma Alhaji magana kada ma a soma zancen.
Nan dai sukai ta maganan yafito tare da mata sallama akan gobe zai kawo ni nai masu sallama kafin mu wuce.

****** ********* ******
Sai bayan la,asar ya shigo gidan yace kun shirya dai ko?
Nace mashi eh tafiya kawai ya rage muna gobe insha Allahu.
Yace kunyi magana da Iyya din ko ?
Nace eh tace tare zamu tafi da ita sai yai dan murmushi yace dama nasan bazata zauna ba ai.
Yace komai an shirya don na dan yi maki tsaraba sai dai basu da yawa sosai suna a cikin motan da zamu tafi dashi akwai kaya nanan na Baba ne sai wanda zaki kaiwa mama din.
Idan na kaiku na dawo Hamza zai samay ku can da motan da zakiyi amfani da ita har ku dawo.
Nace na gode yaya Allah ya kara daukaka ai mai yawa ke nan don kai baka kyauta kadan nasani.
Yace min karbi wanan ki saka a kayan ki idan kinje ki zauna da mama kuyi magana ki samu wanda ya dace kiba da aikin gidan su a fitar mata da plan yadda take so idan bai isa ba sai muyi waya a karo maku.
Ban san lokacin da nace yaya na ina son ka ba wallahi ban ma san bakin da zan maka godiyan hakan ba.
Yai murmushi ya kamoni zuwa jikin shi yana cewa wani godiya zakiyi min bayan yau ki barni nayi na ban kwana kwana biyar aiba wasa bane.
Nai dariya nace kai yaya kai baka da magana sai na wanan zancen kawai yace a,a toke in banda abiki ina dan kwallo inbayi wanan ba may zanyi tunda ina jin lafiya ajikina.
Nan dai ya zauna bai kara fita ba muna ta shiririta a gida sai zuwa yamma ne naji baba sani ya kirashi a waya.
Nai mamaki danaga ya mike zuwa dakin shi amma abin da da mahaifi nasan kila wani maganan siri ne zasuyi sai da,ya shige ne naga ya bar A T M din shi a falo na dauka nabi shi ina shiga dakin naji yana fadin.
Kada kaga laifin maji baba na fada maka tun jiya bazai yuyu ba taje Allah ya ,,,,
Sai gani ina nuna mai katin daya bari a falo din yace sorrya tare da mika min hannu na bashi na mika mai na juya nabar dakin.
Bai fito ba sai da magariba yafita zuwa maslaci yai sallah nima ina daki naji fitan shi .
Hakama da dare muna tare sai hira,akeyi yana waya yana fadin gobe insha Allahu tafiya zai yi zuwa waje.
Har dare yayi muka kwanta ranan kamar ba zamu sake haduwa ba again sai da ya gaji don kan shi ya barni.
Da safe bayan mun karya akafita muna da kayan mu zuwa waje aka loda su a cikin mota.
Kwalliya sosai mukayi daga ni har shi har su iya da zasu rakani ita da musa na.
Sai bayan nafito ne naga ashe da mota biyu zamuyi tafiyan danashi da hilux din shi sabuwa dal da ita.
Dani dashi da iya da musa a mota daya sai wancan dayan motan dake da kaya naga mutum biyu muka gaisa dasu naiwa su maigadi sallama muka kama hanya.
Kafin mu isa gidan su mama ne na kira maryam ina fada mata zancen tafiyan don jiya zumudi ya hana nakirata.
Ainan ta hauni da masifa inda take shiga ba nan take fita ba sai dai hakkuri kawai nake bata.
A gidan su mama ma tayi nata korafin na samu ta hada min nata tsaraban su sabulu man shafa clean parket parket tace na rabawa mutane mukai mata godiya nafito na sallami sauran mutanen gida.
Mummy takawo turare mai kyau da,tsada tace nakaiwa babana turmi naba mama.
Nai godiya mukai sallama muka kama hanya mun dan sha kwanan kadan dagida ya jawo hand bag dina dana aje a gefena ya ciro kudu masu yawa ya zuba aciki wanda ban san ko nawa bane a lokacin.
Ya mikowa Iyya da musa yan dari bibiyu yace su rika acan ko saga abin saye su saye.
Tuki yake a hankali bai wani irin sharara gudun nan da ya taba yi da mu ba a baya daya taba zuwa ya dauko ni ba.
Nakalle shi naga yadda yake tuki a tsanake naji dadi araina ganin irin natsuwan da yake ciki a yanzu.
Gashi mutum mai cikakken halita ga iya kwaliya da tsabta ga kwarjin shi ya kara fitowa a fili sosai.
A hankali na lumshe idanuwana tare da mayar da kaina kan seat din motar ina sauke ajiyan zuciya.
Bai juyo ya kalle ni ba sai cewa yayi yaya akayi ne yan mata ?
Nadan bude idanuwana a hankali tare da dan sauke numfashi again nace babu komai.
Na dai kalli irin haduwan mijina ne da Allah ya mallaka min shi a matsayin uban yayana nan gaba.
Watarana insha Allahu idan zamu irin tafiyan ga killa a full family zamu tafi da yaran mu.
Shiru yayi sai dan murmushin da yayi kawai yace hummm a fili .
Can naji cikina yana murdawa zuciyana yana tashi take na tuna idan na shiga mota amai nakeyi dama.
Aiko nan dana amai yazo min da sauri na jawo leda a jakata na fara amai.
A rude yaya yace ko na tsaya ne wai cikin karfin hali nace mai mu tafi babu komai zai tsaya.
Sosai nai amman sai da Iyya ta miko min goro tace na saka a bakina sai naji aman ya dan tsaya min.
Sai dai jikina da yai dan nauyi a lokacin kaina yana sara min sosai kamar zai tsage min a lokacin.
Tafiya mukeyi ba wanda ya kara magana a cikin mu sai tunane nakeyi cikin al,amarin aure na dashi kawai.
Auren da daga farko kowa ke hango min zaman ukubar da zanyi a gidan shi wanda nima kaina nasan zaman ukubane kawai zanyi a lokacin.
Tunane nayi sosai irin yadda Allah da ikon shi yau gashi ya mayar da,sadauki wani kamilin mutum bawan Allah wanda kowa ke sha,awan zama irin shi a rayuwa.
Yau dubi irin abin arziki da ya labto min nakai wa iyayyena duka a gidan mu da yan uwana.
Aman ya kara yunkuro min na danyi kadan nakoma na kwanta saman kujera sai faman sannu yake min yace wai kodai mu koma ne a fasa tafiyan nan ?
Nace da sauri haba yaya kayi hakkuri please mu tafi ai zai tsaya min nakoma na kwanta naci gaba da tunane na danakeyi akan shi.
Gaskiya yau sadauki ya gwada min shi din na miji ne cikakke mafi darajan mutum da nake ji dashi a zuciyata da ruhina.
Nasihan mahaifiya ta ne lokacin da zamu rabu ya fado min a,raina yau gashi maganan ta dutse hasashen mama ya zama gaskiya ke nan.
Muryan shi ce ta katse ni da yake cewa idan kinje ne zaki zo da yarinyar da kikace din .
Da sauri na juyo ina kallon shi nace wa Sa,ade ?
Yace sunan ta ke nan ko ?
Nace to ai ban fadawa mama ba kafin na wuto kada ta ganni da yarinya haka kawai ga kuma musa already a guri na.
Yace ina ruwan maji may zasuyi mata tunda ba,a gida daya muke dasu ba.
Nace to sau naje naji yadda zamuyi da mama din akan magana zan buga na fada maka komai.
Yace gurin mama ke nan yau zaku fara sauka ko?
Nace haka nake so muyi kwana uku sai mu dawo gurin baba mu karasa kwana biyun mu kafin mu dawo.
Haka muka karasa tafiyan ina jigibce sai faman sannu kawai suke tayi min dukan su.

****** ********* ******
Mun isa gida lafiya nan mutane ke bin motan da kallo suga gidan da za,a sauka sai kofan gidan mijin mamana muka tsaya.
Abin mamaki sai gashi yana ganin mu ya fara murna da fara,a hardashi ake shigo da kaya daga cikin gida.
Dakin mama muks shiga gaba dayan mu har yaya sadauki din da Iyya data rakoni.
Mama farin ciki ganin mu duk ya kashe ta ta rasa inda zata saka mu don ganin bazata ne tai muna a lokacin.
Mijin mama duk ya rude sai cewa yakeyi kai musa je wajen Isa mai shago kasamo maku ruwan sanyi.
Yaya ce No abarshi kawai ai da ruwa ma a motan sai bin gidan yaya yake da kallo yana tunanen yadda zan yi kwanaki acikin wanan irin gidan haka ?
Yadago ya kalleni yaga ni sai masha,ana nakeyi kawai ba abinda ya damay ni da komai bai jima ba yace zai koma don yai zai bar garin shima.
Namike na gyara mayafin jikina nabi shi a baya a kofan gidan muka tsaya dashi yake cewa tau ni zan tafi Fatima sai in Allah ya dawo damu ke nan ko nace to yaya Allah ya tsare na gode yace ki dai sha magani idan kuma kinga jikin zai matsa maki sai ki buga waya Bashar yazo yaje dake ko ?
Nace kai yanayin tafiyane kawai dana dade banyi ba kasan dama ina amai a mota ai.
Yace niko na sani nida kikaita ma amai a mota sai da nima naje gida naita shararawa har da ciwo sai da kika sani.
Nace kai yaya banda sheri yamiko min kudi yace kiba mijin mama wanan idan na wuce don tausayi wallahi mutumin yake bani.
Murmushi kawai nayi nace angode ni haushi yake bani ba tausayi ba abu tunda kurciya gashi yanzu har yafara farin gashi amma bai daina halin shiba na kurciya.
Suna wucewa na koma ciki kaina yana damuna da ciwo naki fada agaban shi kada hankalin shi ya daga yace mu koma.
Na dan kwanta sai barci ya dauke ni bamu ko gaisa da mama ba ban falka ba sai da akai kiran sallah azahar na tashi nai sallah na samu angyara dayan dakin.
Amna wanan karon mu a dakin mama zamu zaune mijintane zai zauna dayan dakin da musa.
An dafa abinci amma,banci ba nace hura zan sha shi aka,sayo iya ce ta dama min na dan sha jin zuciyana yana tashi na ture kwanon gefe daya.
Sai lokacin ne muka samu kebewa da Mamana tace ashe kuna tafe bamu da labari bamu shirya ma zuwan naku ba.
Banji dadin yadda mijin ki yazo bai sha ko ruwa ba ya koma hakana da yunwa.
Cikin dan murya nace haba mama ai ba komai koma an dafa bazaici ba nasani don ba komai yake ci bashi sai abinda yaso.
Tace wani irin tsaraba kukayo muna haka mai yawa yar baba nace wallahi mama ni sai ma yanzun da aka sauke nagani tsaraban yayane duka.
Nace sai su baba da in zan tafi za,a ware masu nasu muje masu dashi tace har can zaku isa ke nan nace ba dole ba mama.
Kada baba yace na fara gudun shi yanzu kuma don naga nayi aure.
Mama ta tabe baki tace aiba gudun shi kikeyi ba halin matar shine baida kyau kuje dadi dadi a kare da,tsiya kuma.
Nace nikan insha Allahu lafiya zamu rabu ai yanzu na riga na gano takon ta sai a zauna lafiya.
Ranan har dare muka raba da mama muna hira sai da dare ne nake fada mata sakon da yaya sadauki ya bayar akawo na gyaran gida.
Mama ta saki lalausar murmushi tace oh ikon Allah ni Amina yau ke da,wanan babban sa,an haka ?
Nikan banda abinda zan sakawa hajiya da zurianta sai addua da fatan gamawa da duniya lafiya nagode nagode bari wanan baudaden ya,shigo muji yadda za,ayi amma bazan nuna mashi kudin yana nan tare dake ba,sai dai naga yaya salisu asan abinyi dasu.
Don har yanzun da kikaganshi nan ga girma yazo amma bai fasa halin shi ba ni kadai nasan irin kuncin rayuwan da nake ciki a gidan nan ke dai.
Shiya sa tunda kika fada min zancen mijin ki ban sake rufe idona a gidan nan nayi barci ba gayawa Allah nake matsalan mu.
Nai murmushi nace da alama kuwa yanzu mama Allah ya karba muna rokon ki.
Don yanzu gaskiya ko yanayi ba irin nada can baya ba kamar farko sai dai kila aboye idan yanayi din.
Mama tace Allah dai yasa ya bari kwatakwata a rayuwan shi.
Yau gashi wanan hadin na hajiya da kike gani kamar son kai tayi maki ya zama aure mafi daraja da ko wace uwa ke mafalkin samun shi a rayuwa.
Dukar da kaina nayi don jin nauyi maganan da tayi tace ga sako da ake aiko muna dashi ta hannun mahaifin ki duk da nasan ba duka yake kawo muna ba.
Nace kai haba mama yaya baba zai rage maki sakon ki kuma tace ai bashi ba wanan munafukar matar tashi dai itace zata rage su.
Cikin natsuwa nace mama tabawa zata iyashi mama don bs imani ne da ita ba wallahi.
Haka muka kwana muna hira harda Iyya da,ta kwanta waje da,farko har barci ya dauke ta nasan tai hakane tabamu guri mu zanta ni da mamana.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BA KI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA PLEASE DON HAKKA CIN AMANA NE MUN BARKI GA ALLAH,,,

Zamana a gidan su mama yasa na dan kara walwalewa na dan samu sauki sai dai har yanzun ba dama naci wani abu a ciki.
Don da zaran naci yanzun zan shiga na mai ke nan sai kunu kawai zan dan sha ya zauna min a cikina.
Ana cikin haka yaya saudauki ya dawo daga tafiya da tarin abin arziki don kusan watan shi biyu ke nan a can gurin tafiyan da yayi.
Sai da yaje gida ya,shirya ya tafi inda muke a lokacin ya dawo ya samu matar yaya Imiran ta haihu ta samu diya mace.
Muna zaune a falo mama gaba dayan mu mama da Iyya suna hira ni kuma ina dunkule saman kujera na nade kaina har kafa a cikin hijjabina.
Anty Amira da,wayan ta a hannu tana chatting sai Sa,ade da ta kurawa tv ido tana jallo don ita kallo baya isan ta.
Da,sallama ya shigo falon gaba dayan mu muka mai da hankalin mu a kan shi.
Duk da dare ne mutum zai iya ganin canjin da ya samu a tare dashi sosai a lokacin daya haka.
Zama yayi suka gaisa da kowa dake cikin falon tare da mashi yaya hanya suna mai fatan alheri.
Sa,ade ta mike har gurin da yake tana gaida shi yace a a wa nake gani haka kamar yar kauye don yanzu sunana a kanta ya koma kuma.
Daga inda mama take zaune take cewa ,a,a kabar kira min yarinyata da yar kauye don yanzun ta waye kai ma nake jira kadawo kakai muna ita makaranta gata sai zama gida ba karatu.
Yariko hannunta yana cewa mama wanan bakauyan zata iya karatu ne a haka ?
Kaita a gani mana inji mama ta bashi amsa tare da cewa kai yaya akayi ka iya ba koyo kayi ba kaima.
Ita dai Sa,ade sai murmushi takeyi kawai don bata sake jiki dashi ba har lokacin duk yana dan mata wasa jefi jefi.
Gurin da nake zaune ya kalla yace madam yaya kuke wai har yanzun dai jikin ne haka ?
Ya mike zuwa inda nake zaune bai damu da akwai mutane a falon ba ya zauna a bakin kujeran da nake a kwance tare da dan shafo fuskana a hankali.
Wani irin mugun zafine yaji jikina dashi yace kai maji haka jikin nata yake da zafi ko yaushe?
Su ka dan kallo mu tare da saurin kawar da idanuwan su don ganin irin zaman da mukayi dashi a lokacin.
Mama tace aima jikin yai sauki yanzu gata har tana dan fitowa falo yanzu aida ko yaushe tana daki a dunkule.
An ko koma asibiti da ita kuwa ya tambaya ?
Yau sati daya ke nan da aka kara mata ruwa da magani ai abin yazo mata


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login