Showing 90001 words to 93000 words out of 373688 words

Chapter 31 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

iskan matasan zamanin nan.
Sai kuma aka fara rawa da da,zagaye duk wanda aka jefa a bu ya fada a kan shi dole ya fito yai rawa ko a ci mai shi taran kudi.
Irin wanan jifan ne koda aka jefo sai abin yafada akan jikin Raiha wace ke can ta juya tana magana da kawar ta.
Jin an sa ihu yasata juyawa don ganin may akewa ihu haka,sai jin kyalen rawan tayi a kan ta inda,zasuyi rawa da,wani sauri dan dogo fari dashi.
Dole badon Raiha ta so ba ta mike tafita filin don bata da kudin biyan tara har dubu biyar idan bazakai rawan show ba.
Fitowan ta yasa mutane da,dama gurin suka,san da,zuwan ta a,filin, inda aka sa masu kidan tausi watau cool music,
Rawa na ban mamaki sukayi da saurayin a filin inda,suka bada show yaron ya,dinga juyata yadda ake rawan kidan na ai nahi.
Wanan abin ne ya haska Raiha,a idon mutane don dama Raiha yarinya ce mai kiran mata duk wani abinda ake so gajikin mace ta mallake shi ko.
Wani matashi wanda tun fara,event din ya kafa hular shi a gaban goshi kamar baya kallon abinda ke faruwa a gurin ya mayar da hankalin shi a kan raiha,sosai.
Yarinyar ta,tafi da imanin shi don haka ya yanke shawara a,ran shi cewa dole ne ya nemay ta don ya gana da ita,yadda yake so.

****** ********* ******
Yanzu abubuwan sun dan yi sanyi wa Maji akan Sadauki don tun ranan da tai mafada sai ta dan samu sauki daga gare shi.
Don haka shawaran hajiyan masa yai mata rana a gurin ta sosai maimakon fada na fitan arziki ga yaron yanzu nasiha da ban baki yafi komai sauki ga yaron yau.
Don yanzu sam ba ruwan shi da kowa gidan kwata kwata yafita batun yaran su amma fa idan ka,shiga shirgin shi duk da haka bai ragawa mutum.
Safiya ce matan gidan kowa sai harkan gaban ta takeyi ba,ruwan wata da wata a gidan kowa tasa tafisshe ta haka zaman su yake.
Sallaman Bintu ya,dakatar da Maji daga aikin da takeyi daga cikin uwar dakin ta.
Tafito suna gaisawa da maji a cikin mutunci da ladabi da tsintsiya a hannun ta Bintu sai take mika mata ledan da,gwagon ta, ta bata ta kawo wa maji din.
Tare kuma da karban tsintsiyar dake hannun Maji Bintu ta karba duk da Maji ta so hanata amma yadda ta marairaice yasa Maji mika mata tsintsiyan sharan.
Nan ta kara yabawa da hankali da tarbiyan yarinyar tana dama ace nice da haihuwar wanan yarinyar ma hankali da sanin ya kamata haka.
Tas ranan Bintu taiwa dakin tare da kawar da komatsan dake a fili ta,shige mata dasu daga ciki don yanzu dama duk Maji ta sukurkuce bata da,wani kuzari a jikin ta saboda dafin bakin cikin dan ta ya fara tabata sosai.
Bayan Bintu ta gama da gyara waje ta kofan part din Maji ne ta shigo dakin tana,saye da dan hijjab din ta mairuwan cingan .
Tana cewa Mama na rarage ni zan tafi gida kada gwago taga na dade ban dawo ba.
Nagode Fatima Bintu Allah yai maki albarka Allah ya albarkaci ruwan ki, Bintu ta amsa cikin yar muryan ta, da Ameen mama nagode.
Ta fita daga gidan matan gidan sai binta da kallo suke da take aikin suna mamaki don dai su sun san yaran su basu iya wanan aiki da yar karamar yarinya tayi haka.
Duk wanda ya,shigo ya,samu yadda Bintu ta gyarawa Maji guri sai yai maga suce kai Maji amma yau kan kun sha aiki sosai maji waban gyaran guri haka.
Tace wa Ameera bani fa nayi shi ba yar gidan hajiyar masa ce ta gyara min shi haka ta shigo ta samu ina shara sai ta karba shine tai min wanan aikin haka,
Yarinya yar albarka da ita da mutunci ga sanin ya kamata a yar karamar yarinya da ita haka.
Amira tace ni dai yarinyar tana bani shawa wallahi don tasan girmama na gaban ta sosai.
Har maigidan sai da yaiwa Maji magana dacewa yau shiyan nan naki yai min kyau ga kamshi na tashi sosai.
Murmushi maji tayi tana cewa ya ta yar albarka tazo tai min wannan aikin yar gidan hajiyar masa na makwabtar mu
A,a tayi kokari su wayan nan katar banzan may sukeyi ne da,bazasu iya gyara guri ba,sai wata tazo ta gyara masu.
Maji tace halin yaran nan ai sai su don ko sunyi basuyin yadda wanan karamar yatinyar tayi.
Tun wanan rana kwana bibiyu sai Bintu ta shigo gidan gurin maji ta dan yi mata aikin da ya kamata tai mata sai ta koma gida.
Sannu sannu har Bintu tafara fahintar cewa Maji tana fuskantar matsala a gurin mutanen gidan don basu kaunarta sam.
Ga fitinar dan ta da koyaushe ya shigo gidan tana jin yadda yake uwar ke fama da shi akan wasu matsalolin da bata fahinci aini cin yawan laifin da yakeyi ba ako da yaushe don maman nashi bata fitowa fili tafadi sai dai taganji tana cewa.
Baba kaiwa Allah ka rufa min asiri ka,daina halin nan naka don girman Allah.
Sai ya kan katse uwar da wani irin magana a gala baice da cewa ni mama mai nayi ne wai kullun ace wai mutum yai laifi.
Sai yafita a kasalance yabar dakin zuwa waje maji kan bishi da kallo har yabar dakin ta sauke ajiyan zuciya tace Allah ya kyauta.
Yawan ganin da Sadauki yakewa Bintu a gurin mama bai sa ya,sake da ita ba asalima dai shi yarinyar haushin ta yake matukar ji a,ran shi sosai.
Don tafaye yin abu kamar muna fuka idan ta ganshi ta kama dan noke noke ke nan kamar taga dodo ko mugu bata jimawa zata bar dakin ta ce ita zata wuce duk yadda maji tayi ta tsaya bata yarda ta tsaya idan yana nan part din.
Gwago tana son zuwa kauye don uzuri na tafiya ya taso mata zuwa gida shine taga bazata iya barin Bintu gida ita kadai ba.
Don haka tazo da kanta gurin maji tana neman arzikin Bintu ta zauna a gurin su har ta dawa daga gida.
Don babu damar ta tafu da ita a na cikin makaranta a lokacin ana karatu ne ba hutu akeyi ba.
Da yar ledae kayan ta tazo gidan aka sauketa daki daya dasu Amira da maryam.
Tunda gwago ta, tafi a takure Bintu take gidan su Amira din koda kowa yana falo Bintu tana daki ita bata fita zuwa ko ina ko kallo bata fitowa tayi a falon kamar yadda kowa keyi.
Yau da ya dawo daga wasan ball ya samu maji a kwance bata jin dadi don haka tana ganin shi tasan cewa abinci ne ya kawo shi don haka daga inda take kwance ta kwalawa Bintu kira tazo.
Mamakin jin tana kiran wani bakon suna daga ciki Umar keyi sai dai halin shi bai barin ya tambaya ko bakuwa,ce uwar tayi mai suna hakan.
Bintu tafuto tana saye da dan farin hijjab din ta a jiki don dabiar tane bata zama jiki ba hijjab ko kadan.
Mama gani inji Bintu duk da jin muryan ta da jin muryan ta da yayi ta shigo da sallama bai sa ya dago kan shi ba daga abinda yake a,wayan shi ba.
Bintu don Allah kawo wa yayan ku abincin shi kin ji,
Tau mama tace tare da juyawa zuwa dauko mai abincin dan lokaci kadan sai gata da ture ta ta dauko kayan abincin har ruwa duk a cikin ture din.
Kujeran da yake zaune akai hankalin shi a,waya ta nufa, ya dora kafan shi daya saman daya.
Ya mayar da bayan shi a makarin kujeran da yake sama zaune yana ta faman la tsan wayan shi.
Bintu ta karaso gaban shi ta dire mai turen abincin a gaban shi ta juya da,sauri zata bar falon,
Muryan shi taji kamar mai jin barci bayan ta juya yana cewa,
"Ke, yace da dan karfi abinda yasa Bintu ta,tsaya guri guda cak ke nan bata daga kafa ba kuma bata juyo ba.
Kizo ki zuba,mana zaki ajewa mutum abinci hakana kamar wata yar kauye can dalllah,
Da hanzari Bintu ta juya don bin Umurnin shi ta duka tare da jawo plate tafara zubawa a plate din dake cikin ture din.
Sai da Bintu ta shake plate din fam sannan take cewa nazuba tana shirin mikewa.
Ke Uban wa zai ci wanan abinci haka kamar jaki ko an fada maki cewa kowa irin ki dan kauye ne.
Kai Babana inji Maji wanan wani irin hali ne maka yarinya ta,dafa,ta kawo maka kuma cine kawai naka har kake kokarin kiran ta,da,sunan dabba.
Ke wuce ki shige abinki kinji Bintu kar ki tsaya,sauraren shi da zancen banzan shi.
Da hanzari Bintu ta juya zuwa cikin uwae dakin mama inda dakin su yake da,su Amira gaban ta yana faduwa irin yadda yai magana ya bata tsoro sosai.
Tun ranan bata son taji koda muryan shi don tsoro yake ba bintu din idan ta gan shi.
Da wani dare yashigo gidan sai wani lumshe idanuwan shi yake anyisa,a Bintu ma tana falon do Amira ta takura mata tafito suyi kallon wani hausa film sabon fitowa.
Bayan ya,samu guri ya zau a suka,shiga gaishe shi daya bayan day suna mashi sannu da,zuwa,
Ya zauna tare da mayar da hankali shi ga mahaifiyar su da ke zauns daga gefe saman salaya tana jan casbi ta a hannkali suka gaisa dashi daga gurin da take zaune ,
Sai dan wa lokaci ya dan nisa yanacewa Maji abinda yasa ta,dawo da hankalinya ke nan gurin dan nata don tasan magana yake son yi da ita.
Yace dama nazo maki da wani magana ne akan al,amarn da ya,shafe ni.
May kuma ya faru ne babana Maji dama ina son fada maki ne na,samu wani contarac akan zancdn ball din da nake yi wasu club suna son dauka na zuwa yi masu wasa.
Cikin sauri Maji tace ban amince ba kaji na,fada maka kada ka,fara ka,tayar da,zancen nan har wani yaji ko mahaufin ku a gidan sai nai matukar bata maka rai wallahi kaji na fada maka gaskiya.
Kallon mamaki yakewa mahaifiyar nashi don tabashi mamaki don shi a,zaton shi yai tsanmanin zatai farin ciki dajin wannan labarin tunda kullun gori take mashi akan wasan ball din da zaman banza bai zuwa shago kamar sauran yan uwan shi na, nagidan da,suke taya mahaifin su sana,a.
Shiru yayi tare da,dukar da kan shi guri guda bai daga ba har tsawon wani lokaci .
Tsam Bintu ta mike zuwa ciki don tsoro takeji naganin fushin wanan jarumin kada ya hada fushin shi dasu.
Maji amma,wanan abin fa alheri ne sosai idan har anyi nasara akai don Allah ki bari naje.
Bazaka banace na fada maka,gaskiyan magana ta ke nan har cikin raina .
Nan ma da kake a gaban mu yaya muka kare dakai balle can inda babu kowa naka.
Shiru yayi sai ya mike zuwa fita Maji tace abinci fa yace makoshi kawai yasa kai yafita daga dakin.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


A gurin da suke zaune suna magana suke jin hayaniya daga cikin gida, shiru sukayi suna saurarawa.
Labulen dakin tane ya,daga ko sallama babu ya fado masu dakin duk jikin shi yai futu, futu da kasa ga wandon shi kamar yai fitsari a ciki.
Kara shigowa yayi daga cikin dakin ya fadi kasan ties din falon jagwab dashi sai kuma ya fara nasarin barci.
Innalillahi Baba na may ke faruwa ne haka, may ya samay ka, may akai maka, wa yai maka wanan abin haka.
Sai ta,sake wani irin kuka cikin wani murya mai ban tausayi da tsuma zuciyan mai sauraren ta.
Innallilahi wa,inna alaihim rajium Baba kada dai ace da gaske shaye shaye kake yi haka.
Cikin kuka take magana da tashin hankali, mai masa kin ga yaron nan yau yadda ya koma ikon Allah.
Allah kataimake ni ya Allah wanan yaron yau may zangani haka da idona.
Nashiga uku na lalace a rayuwata Sadauki may ka koma haka yaushe ne kafara wannan bakar rayuwan haka.
Takara daga murya tana cewa Baba na badai shaye shaye kakeyi ba cikin gigicewa take maganan.
MAJI bafa,,, abinda ya,samay ni just ,,,, relax ,, relax Maji,,, kawai,kawai dai ,,,, dan joy neeee,,,,,
Sai ya mayar da kan shi kasa yaci gaba,da barcin shi, nashiga uku mai masa yau dan nan ya, jawo min magana babba a cikin kishiyoyi da al,umma.
Baba da nasan wanan rayuwan zakayi a duniya da na barar da cikin ka na huta da ganin wanan bakar ranan da nagani yau a,rayuwa na.
Haba haji ki daina fadin hak don Allah yanzun dai musan abin yi kafin abin yai mashi illa haka.
Mai masa ai gara ace ya mutu da na zauna ina ganin shi a gabana haka.
Umm,umm hajiya don girman Allah ki daina fadan haka wa dan ki Ai babu abinda ya gagari Allah ko?
Kuka mai tsuma rai Maji takara sakawa cikin tashin hankali tana fadin da daya ke nan tilo namiji da Allah ya bani mai masa yau ga abinda ya zama min a duniya.
Ba u komai Allah ya shirya muna shi dashi da ma sauran diyan musulmai masu wanan halin.
Daga waje kofa tsakar gida kuma kishiyoyin maji a tsatsaye suna fadin ikon Allah yaukan mun ga abin mamaki a cikin gidan mu wanan bakar masifan ya,fado muna.
Hmmm lalau akwai magana da,sake don dole a,dauki mataki ga hakan kafin a lalata muna yaran mu.
Dayar kuma sai cewa tayi kai gurin bakar jaraba har an kwaso muna jikokin yan maye a gida yau ga abinda bakar jaraba ya jawo a gidan nan.
Ace wai cikin gidan nan yadda muke da mutunci a cikin shiya an samu dan maye irin haka.
Allah kai muna tsari da wanan bakar masifan ka kare muna yaran mu dama karshen so ke nan ga yaron da ba,a kwabo ai.
Haba dai ai wanan ba daga nan ba inji amaryan su kowa dai yabi nashi da addua amma ai ita Maji ba itace ta turashi zama haka ba kudai kowa ya iya kan sa don wanan masifan ta shafi kowan mi a gidan nan, ba ita kadai ba.
Ke don Allah ni ban son munafumcin banza ina ko ke bai bari ba indai sadauki ne a gidan nan.
Haka sukai ta cacan bakin su daga kofan dakin Maji da suke daga ciki suna jin cacan bakin su.
Mai masa kinji abinda nake fada maki ta fadi cikin kuka da tashin hankali.
Ai basu kamar Allah ba don ba wanda ya wuce jerabawan ubangi daga cikin su.
Ke dai kibi dan ki da adduan neman ashiryuwan daga Allah dan yanzu ke ce da matsala basu ba.
Kara jajircewa ki koma haikan gurin ubangiji tare da nemar taimako, kina bashi koda baya so ki bashi ya shanye a gaban ki ba bayan ki ba.
Insha Allahu nima zanyi kokari naga na taimaka da dan abinda zan iya gurin al,amarin.
Don kinga shi aikin shedan shiga rai ke gare shi sai mutum yai kamar zai bari sai kuma shedan ya rude ka ka koma.
Don haka yanzu ki yawaita jan shi a jiki ki kada ki biyewa maganan mutane kina nuna mai kyama ko hattara ,a,a ki jawo danki zuwa jikin ki don ki san damuwar shi.
Shigowan Bintu dauke da dan wani kwanon glass na tangaran da cibi a cikin sa yasa sukai shiru baki dayan su.
Su Amira duk suna tsa tsaye cirko cirko sai faman kuka sukeyi da tashin hankali.
Gurin da yake kwankwance sharkaf dashi ta nufa inda ta durkusa tare da dora kan shi a cinyar ta suko duk ido suka saka mata.
Amira na ganin haka ta fahinci may Bintu ke shirin yi masa don haka itama ta karaso tare da karban kwanon daga hannun Bintu.
Haka maryam itama ta guso inda suke da taimakon su ta samu ta bude mai baki da kyat suka dura mai manja da girshirin da ta hada har kusan cibi uku,
Sai ya fara wani irin tari ya bude idon shi da kyat tare da dan kara yunkurawa sai kuma bintu ta mayar da bakin shi da karfi ta rufe gam sai ko yai wani zabura tace ku danne min shi dan Allah.
Maji dake gefe tana kallon su ta kara sakewa da wani sabon kuka sosai cikin tashin hankali.
Yan mintina kadan saiko wani irin amai ya taso mai nan ya fara sharara amai kamar zai amaye kayan cikin shi a lokacin.
Amai sosai Umar yayi a lokacin sai kuma ya koma barci dan gefen su kadan.
Bintu ce ta kwashe amai


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login