Showing 198001 words to 201000 words out of 373688 words

Chapter 67 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

sosai.
Saidai duk da waya yake idonbshi yana kan kitson da Maryam take min kur dashi gashi dole muna facing din juna dashi.
Yana kashe wayan ya mayar da shi cikin aljihun shi inda ya ciro ta da farko.
Yace maji fa?
Yanzun ta shiga ciki nasan zatafito tunda taji muryan ka ai inji maryam din.
Maryam tace yaya wanan wayan taka tayi wallahi ni dai taban sha,awa Bintu gashi kaman wanda mukaga Kabir dinki dashi ranan.
Da sauri yace ke maryam ban son iskanci wallahi ki daina hadani da wanan tsohon mai zarin tsiya.
Na muguda baki cikin tsiwa nace nikan banga tsoho ba wallahi.
Ban san ko tako nawa yayi ba,sai gashi gabana ya danko gashin kaina da karfi sai da na,sake wani irin kara,da sauri mama tafito tana fani kai kai yayane kuma wai ?
May haka dan Allah kasheta zakayine ko may ?
Wallahi maji yarinyar nan ta raina ni wallahi kan wani tsohon mijin ta can take son ta zage ni, ta zage ka tace maka may?
Maryam sai dariyan keta takw min idanuwana,sun kawo kwalla ko don har cikin raina naji dankan da,yai min.
Kadai zama babban kwabo wallahi ka ishi yarinya da sherin mijin ta tsoho ne basai ka,samo mata saurayi ba kowa ya huta.
Allah dai ya,sauwa wake son wanan bakauyan haka ko dressing ba ta iya ba balle gyara irin na mata.
Kyalkyalkyal maryam ke min dariya Amira da,tafito daga kitchen don jin karana take cewa, a,a yayana aiko wallahi yanzu ba may cewa Bintu bata iya dressing ba gaskiya.
Kallonta yayi yaja tsoki ya juta gurin maji yana fadin maji zan dan shiga gurin su bashar na,dawo yanzu.
Sai ka dawo tace mashi tare da samun guri ta zauna tana man fada na daina shiga harkan shi kada ya halakani ga banza.
Nace cikin dan kuka ina,share hawaye da bayan hannu na mama,wallahi duk anty maryam ce taja min.
Ban san may yakaita danganta,wayan shi dana Kabir ba,shine yake cewa wai za,a hada shi da tsoho kazami.
Dariya abin yaba mama tace ni dai na rasa wanan kiyayyan na sadauki da Kabir wallahi Allahbya sauwaka.
Amira tace jinin su ne bai hadu ba yace min wallahi haushin shi yake ji.
Wai babba dashi yazo zaiwa yarinya wayo itako sai shegen son maza duk ta mutu akan tsoho.
Dariya suka sa nace tunda yana jin haushin shi ba,sai ya kashe shiba in ya isa.
Har lokacin ina jin zafin dankan da yai min don har kaina naji yana sarawa wani iri.
Tafe yake cikin motan shi sai dai a hankali yake tukawa don akwai motoci da yawa saman titin a lokacin.
Wani iri yaji kamar ina cikin motan na,sake wanan razananen kara da na sake lokacin da yaja min kai.
Yace natural hair ne haka gare ta ashe nibna,dauka ko kari take ko yaushe ai.
Wawiya can zata karata dashi gurin dan tsohon ta babu ma gyara kila a karshe.
Yana faka motan daga inda ya tsaya yafito yasa remote ya kulle motar nan ya taka a hankali zuwa gurin da office din Bashar yake don yasan yana nan yaga motar shi a fake can ne sa.
Bashar na zaune yana cika wasu takardu sadauki ya shigo office din .
Bashar ya dago yana cewa kadai samu fitowa ke nan yanzu din na dauka sai ka tsaya ka cinyewa tsohuwa dan tallenta ka fito ai.
Murmushi yayi yana kaiwa zaune yace don wa ake dafa tallen dama ba don mu ba.
Gaskiya ya kamata ace kayi aure haka wallahi man, don Maji ta huta da katon gwauro haka kullun yana lashe mata talle.
Sadauki yai murmushi tare da daukan wani takardan dake gaban shi yace aiko nai aure tallen maji ba zai huta dani ba.
Kana ma min zancen aure ga babban tazurai basuyi ba balle ni.
Da sauri cikin daga kai Bashar yace wa wai Imiranah kake nufi da Ahmad?
Yace su mana kai dan Allah rabu da wanan shashan yayan namu .
Cikin dare fuska sadauki yace ban son iskanci ba yayan nawa ne kuma sha sha.
Ce wallahi shi duk gari yanzu kowa yasan shi sai aukin bin yan yara masu tallah yana latsawa a kasuwa.
Kaifa dan iskane wallahi wanan kuma ai sheri ne nasan dai yana da shegen son mata amma ban san da wanan ba kan.
Yace aiku na gida baku sani kwanaki ma naji ana kudundumin yaiwa wata yarinya mai kai shikafa layin su ciki ko yaya case din ya kare.
Bashar yau dai da sheri ka tare ni ke nan dai don nazo gurin ka dana sani na zauna gida abina ko natafi stadium.
Wallahi ba sheri bane don ina ga Baba ma yasan da wanan case din ai .
Zai iya don kwanaki a gabana wallahi Fatima ta mare shi babu ko kunya wallahi.
Naso na lalatsata ai amma sai naga tana da gaskiya din taba tayi kasan bata da kunya itako ta kwashe shi da mari kayau.
Wata Fatima ke nan kuma?
Ya dan bata fuska yace wanan dayan sister tawa dake gurin maji mana da zama.
Au kace min pretty mana gaskiya mutumina yar8nyar nan ta hadu sosai wallahi ni dai tana min.
Dariya sadauki yayi mai kama da yake yace aiko dan tsohonta zaici ubanka wallahi.
Waye dan tsoho kuma babanta yace wanda zata aura dai wani guy ne mai mata biyu wai itace ta uku .
Zokaga shegiya yadda take rawan kai nace kici uban ki indai kince rawan kaine.
Kai kai amma gaskiya an kwabsa wallahi gurin nan .
Wai ma kai kana may har ka bari haka ya kasance ga ka har kabari akaba wani kuma can.
Wani kallon rainin hankali ya watso mashi gani sai ayi may kuma ?
Yace yar gida gida mai tuwona maina kawai musha buki mukan .
Kasan fa yarinyar wallahi matar manya ce sai ta samu gurima zakaga yadda zata baje sosai wallahi.
Kai don Allah ni bashi yakawoni ba wai how far ne akan kayan can da suka shigo.
Bashar yace baka son zancen ke nan dai mubarta anan kawai ko?
Yace zancen may kuma may zanyi da wanan mai zubin yan arab da ita.
Bashar yai wani dariyan keta yace kaidai sai naba Maji shawara tafara maka hayaki da rukiya wallahi.
Ya jawo wasu takardu daga drawer shi yana mikawa Sadauki yace duba nan ka gani kafin mu koma topic din mu don gaskiya ni iam serious wallahi.
Ko tayi miji ai ana iya tayar da zance don gida bai koshiba ba a kaiwa dawa.
Karanta takardan yake bai bashi amsa ba sai can ya dago kai yace ikon Allah so quick haka sun samu shiga da,wuri.
Yace yanzu haka ma munyi magana da SMG yace min kila zasu sa mukawo masu sabon sanfarin su din suna son su rabawa sarakuna shi.
Amma ko gaskiya in haka ya kasance da muyi sa,a sosai wallahi ko.
Nan dai suka kara dan tattaunawa akan business din su inda suka fito don dama suna da alkawrin zuwa wani guri da Bashar ya damu sadauki su tafi.
A hanya sadauki ya nisa yace amma gaskiya banji dadin labarin da ka bani ba na Imirana .
Yace kai kana ga zancen ne har yanzu yace ai wallahi duk ya zubar da mutuncin shi saikace ba Alhajin ku ya haisu ba.
Shifa Ahmad cewa akayi yana sanan kayan sata sai asato mota ko mashin ya saya .
Innalillahi da karfi sadauki ya furta tare da waigo inda Bashar yake zaune a gefen shi yace wallahi man .
Wai kai kana nufin duk wanan zancen baka san dasu bane ko yaya?
Yace ina zan sani tunda ba shiga gati nake ba yawo iyakata idan ina gari ina gida ko nan gurin ka,sai ko can site din da nake gina na kawai.
Lalai na yarda baka gari gama,wanan sister din naku kwanaki saida yan hizba suka kamasu wai ance sun hada party suna abin banzan ga da mata keyi tsakanin su.
Da karfi ya taka burki yace Nafisa ko?
Yace ita wallahi naji kunyan wanan abin sosai wallahi ance ai shaye shaye takeyi sosai yanzu kowa yasani ma agari.
Subbahanallahi ya,furta yace how comes abubuwa suke zo muna haka agidan mu kaman mu kadaine a gari.
Kadai Allah ya,sauwaka kawai amma ai abin ba dadi wallahi.
Can suk shiga kasan gari gurin ginan shi irin na mutanen dana daganin gurin mutum zai gane cewa tsohon gari ne gurin.
Da,kwatancen da Bashar ke mashi suka isa gidan da suke son zuwa,
Daganin gidan basai anfadawa mutum ba gidan wani masani ne na alkur,ani maigirma don ga alluna nan na almajirai daga waje birjit dasu.
Nan suka,tura ai masu iso da,maigidan sai ga,yaron ya,dawo yace ance su shigo daga cikin zauren gidan.
Wani tsohone ya tsufa sosai yana zaune saman shimfida irin ta mutanen da can baya masu fada aji.
Bayan sun gaisa da tsohon ne Bashar ke cewa malam ka gan mu sai yau muka samu zuwa ko yace tau harkokin ku na mutanen yanzu yawa gare shi.
Nan dai suka kara gaisawa Bashar yace malam kaman yadda na,fara maka bayani ne akan al,amarin wanan abokin nawa dai.
Yau gashi nazo dashi malamin yai shiru can ya dan mike zaune tare da kallon su da kyau yace.
Karbi wanan yana mai mika mashi tasbahan hannun shi dayake ja, yace ka zabi guda ko wanine ma daga ciki.
Ya dauki wanda ke kusa da farko sai, tsohon yai dan murmushi yace ai abin yazo da sauki tunda naga baka da zari.
Don da,wanine na tsaka zai dauka yana ganin yafi mai killla yawa.
Ya dinga karatu mus,mus mus dabaki can yace umm,umm Allahu akabar to Allah ya sauwaka.
Su dai suna zaune suna kallon shi can yanisa yace Alhamdullahi Bashar don al,amarin abikin ka ba acewa komai don yanzu ma kuka fara insha Allahu,
Sai dai gaskiya akwai dan matsa dana gani yanzu dai tunda bashi yakawo ku ba harkankuce ta sana,a takawo ku bati muyi abindake nan.
Nan dai yai masu wasu bayanai yakuma basu yan abubuwa tun ana gaban shi yace su sha.
Sadauki da cukin kyankyami yake ya matsu subar gurin don shi bai son irin harkokin nan gaba daya a rayuwan shi.
Bashar ne ma ya matsa mashi kan lalai sai suzo don yanzu duniya ba,a shigan ta haka kai tsaye don A LOKACI MU KE.
Sukai mai godiya tare da mikewa zasu fita bayan sun bashi, dan abincin goro don yace bai karban komai nasu don abokin kakan Bashar din ne sosai.
Sadauki dake gaba ya dafa zauren na kasa zai fita sai tsohon yace ji mana idan kaje gida kacewa mahaifiyar ka kada ta manta da zancen baya da tai alkawari kai ka gurin da aka bukaci ta kai ka a baya.
Don idan bata maida hankali ba hannun agogo kullun zai dinga koma mata bayane.
Da mamaki sadauki ya kalli tsohon sai dan tsohon yai murmushi cikin kada kan shi yace abinda nace zaka fada mata ni dai bata sanni ba ban san ta ba.
Yace cikin mamaki toshike nan malam zan fada mata insha Allahu kaman yadda kace na fada mata yace Allah bada sa,a suka ce amin suka fita daga zauren.
Duk zukatan su fam yake da tunanen zancen tsohon saida suka fara hanyane Sadauki yace kai guy man din nan fa ya bani mamaki.
A ina ya san maji kuma may yake nufi da sakon shine wai?
Bashar yace nima naji mamaki amma sanin halin malam babba yasa ban damuwa nasan wani zance ne can ya hango akan ka kuma.
Baidai son ya fadine kawai kila tunda bashi yai aikin ba.

****** ********* ******
Maji ke da duty a gidan ranan duk da dai su girkin su bawai na duka gida bane gaba daya.
Wace dai take da girki ranan itace zata girka abincin part din ta dana maigidan kawai.
Ba ruwanta da sauran part din gidan kowa shi zai girka nashi da yaran shi.
Komai da ya dace a girka sungama da wuri kamar kulun sai ta wuce sashen maigidan don ta gyara mashi daki kaman yadda sukeyi kullun kafin ya dawo gida daga kasuwa.
Amirah ta tafi kitso a wani shago cikin unguwa maryam kuma ta shiga makwabta don ganin wata kawarta da tayi rashin lafiya.
Tare zamu tafi sai banda lafiya kaina da akaja min yana matukar damuna da ciwo hakan yasa tatafi ita kadai.
Ina kwance saman doguwan kujeran dake falon na rufe fuskana da littafina da na dauko don na karanta amma na kasa karantawa saboda kaina dake damuna da ciwo.
Sadauki ya shigo falon don ya ga mahaifiyar shi akan maganan da malam yai mashi.
Nan ya hangoni a kwance,kyakyawan suran jikina danabi kujera na kwanta rigingine yafito a fili.
Farin kafa na da yake fari sol dashi ya dan baiyyana a fili sunyi fari sol gasu lub lub dasu tankar wace bani taka kasa.
Sadauki yai saurin kawar da kan shi dan ganin irin yanayin da nake a kwance cikin yar doguwar rigata mai dogon hannu da,sharp.
A hankali ya tako zuwa inda nake kwance din ya dan rage tsawon shi ta hanyan dukowa ga kirjina ya dan ban karo gaba.
A hankali yasa hannun shi ya cire min littafin dana kare fuskana dashi,
Da sauri na bude idanuwana da suke min a lumshe don ganin waye ya cire min littafi haka a fuskana don part din shiru yake a lokacin.
Daga cikin tsakiyar kaina da hancina naji kamshin turaren shi amma banzaci cewa shine a gabana ba.
Nai saurin bude idanuwana da suke a lumshe alokacin shi nagani tsaye kerere a kaina .
Haka yasa nai saurin yunkurin tashi zaune a lokacin tare da jifan shi da wani fitinanen kallo na tsana.
Yace ke ina mutanen part din suka shigane wai ?
Wani guntu tsuki naja da ban yi niyar ja ba don cike nake dashi a lokacin saboda ciwon kan daya haddasa min.
Ke ni kika ja,wa tsuki ashe baki da kunya haka ban sani ba?
Nace cikin turo baki da kokarin tashi tsaye ni halan nai maka tsikine ?
Yakai hannun shi ga dan bakina iya karfin ya murde shi da karfin tsiya, ban san lokacin da nasa kuka ba da karfi ina cewa.
Ya sadauki nimay ne maka katsane ni haka kaja min ciwon kai yanzu kuma kazo ka murde min baki.
Na karashe fadi cikin wani irin kuka nace in gidan kune baka son ganina sai in bari nima fa diyace kamar kowa.
Na juya zuwa cikin dakin da kuka na sai muka hafe da Maji dake shigowa falon, hannun ta dauke da kayan su jik dinta, da hapic na wanke bathroom.
Tsaya tayi cikin mamaki takaleshi ta kalleni cin son jin may yafaru bayan futan ta .
Sai kukana take ji a cikin dakin daga inda take tsaye, tana mai wani irin kallon tuhuma.
Tace may kai mata sadauki?
Cikin ko in kula ya nufi saman kujera ya zaune, yace shagwaba take ji kawai dai.
Kai may kaimata nace?
Tambaya kawai nayi ina kuke sai tai min rashin kunya nikuma na murde mata baki.
Kana ko da hankali sadauki?
Shin yarinyar nan tobashiyar kace ko kuwa wai?
To bari kaji wanan kukan da ka sata ko ka bata hakkuri koo na rama mata abinda kai mata.
Wa zan ba hakkuri Maji?
Tace Fatiman.
Yace cikin mikewa kai haba maji don Allah ki bari kada ta kara raina ni mana.
Kai har wani raini kake gudu bayan wanda kajawa kan ka?
Ya mike kawai yabar dakin don shima kukan da yake ji yafara shiga zuciyar shi a lokacin.





ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


I DAN KIN TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA MU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAR MUNA A KAN KI


Bayan mun dawo gida sokoto babu abinda mama keyi sai lalashi na tana kokarin taga na saki jikina sosai.
Amma na,kasa sakin jiki saboda shakuwa ba karamin abune ba ga dan adam.
Na kasa cire Kabir a raina gaba daya ko yaushe zaka ganni nayi zaune nai shiru ni kadai ko idan ana hira ni na zauna naita tunane ni kadai.
Yau ma zaune nake saman dogon kujeran falon sai hira suke a tsakanin su akan Ahmad dan wurin mama Asiya.
A zahiri kallon su da sauraren su nakeyi amma zuciya na tai nisa da inda suke zaune.
Sai da naji murya mama cikin fada tana magana ko shi sai da Maryam ta dan taboni na,zabura firgigit dani.
Yaya Sadauki na gani tsaye cikin kaya bakake sai kwalan rigan ke da jan kwalla daga saman shi, kamshi na tashi daga jikin shi.
Kallon mamaki yake min irin yadda na koma a lokaci daya na koma Bintu shiru shiru dani ban magana kamar ba nice ba.
A hankali ya tako zuwa inda nake zaune saman kujera na takure kaina guri daya ina makure kamar mai jintsoro.
Zama yayi daga gefen kujeran da nake zaune na dago ido in kallon shi a cikin mamaki don, bai taba zama haka a kusa dani ba.
Yace, Fatima har yanzu baki sake jikin ki ba ko kin fi son ki tayarwa maman ki da hankalinta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login