Showing 123001 words to 126000 words out of 373688 words
Chapter 42 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
Baki da niyar saurare na shiyasa kina ganin kamar kishin Nasir na tare dake yasani zuwa gurin ki ko?
Ba haka na bane amma akwai wasu yan tambayoyi da zan maki ina bukatan amsa daga gareki in naji su daidai kinyi gaskiya.
Raiha ta dawo ta zauna tana kallon Nura ido da ido tace ina sauraren ki ko?
Hmm wai ma ta ina zan fara tambayan ki ne duk kin sani a caji wallahi.
Duk ta inda kika fara in na sani zan baki amsa insha Allahu.
Ok tau dan Allah kunkai kamar tsawon wani lokaci dashi Nasir din a tare dashi.
Ummm gaskiya mun kai kamar wata takwas muna tare inda a sannu ya fara koya min wasu abubuwa na rayuwa.
Kallon ta Nura tayi da kyau tace hmmm lalai ma amma ce min yayi tunda matar shi suka rabu bai kara neman wata ba bayan ni.
A,a karya yai maki don kafin ni akwai wasu da har yai galaba a kan su yanzun haka suna waje on behalf of him suna karuwanci a Spain.
Kai wai da gaske kike da zancen ki ni yar uwa wallahi ba karya a magana ta sai tsabar gaskiya kawai.
Ok ya taba zuwa dake tafiya ne ke dashi kubar garin nan zuwa wani waje?
Tace kwarai mun je lagos da sunan yatafi aiki ashe yakaini ne gurin yan commuty din su sugan ni idan zan yi sai ya dawo ya shirya tafiya na.
Mikewa tsaye Nura tayi tana fadin ikón Allah na ko yarda da zancen ki don duk inda muka tafi sai naji ana cewa she is ok,
Very pretty you will get a high level on dis pretty,
Sai da nai mashi magana ya daina kaini ana fada min hakana don ban son jin wanan kallaman daga bakin arna.
Murmushi Raiha tayi tace a can bai nuna maki true color din shi ba ne ko ?
Kamar yaya Nura ta tambaya.
Murmushin takaici Raiha tayi tare da fara fada mata duk yadda yayi da ita a garin Iko din.
Mikewa Nura takarayi tsaye tace umm ummm na yarda da zancen ki gaskiya don nima ya jawo wani abokin shi akan na tarda mu kwana tare dasu su biyu amma bai san ina jin lokacin da suke maganan haka ba sai na bijire mashi tun kafin dare nace period yazo min.
Mikewa Raiha tayi tace nasan koke can akayi shiyasa nasa a saka min ido a kan shi nai alkawarin duk yarinyar da yai niyar batawa sai na kwatota daga halaka hannun mugu azzalumi mayaudarin banza macuci kawai.
Nan suka zauna sukai ta hira akan yadda zasu dau mataki a kan shi don kada yaci gaba da abinda yakeyi.
Tun wanan ranan suka kulla kawance da junan su inda ta rako Raiha tana mata godiya.
****** ********* ******
Tun daga kofa yake kwala wa mariya kira har zuwa cikin gidan, maria wace ke duke tana wanke wanke taji kiran a bazata yai mata yawa.
Ta mike tana fadin gani nan babban Abba lafiya dai ko kira haka daga waje babu kakautawa.
Yace cikin hasala yanzu naga malam a kasuwan mu yake ce min wai yaran nan yanzu basu zuwa makaran ta ko yaushe.
Shi Abba ma sai ya makara kullun kafin yaxo in ma har yaje din yace yai magana yan uwan shi suka ce wai talla yake zuwa.
Tace tallafa tallan may wani kallo yai mata na ban yarda dake ba fa.
Tace ba gaskiya bane in zai yi talla ai ban dora mashi ban fada maka ba balle ma nasan ba yarda zakayi ba.
Shi dai kila yara sunyi mai yawa yanzu bai gane zuwan su da rashin zuwan su shiyasa ya fadi hakan.
Yanzu ina suke ya tambaye ta tare da tsureta da idanuwan shi tace sun tafi tin da karfe hudu suna can.
Yace ai zan tafi nagani ko suna makarantan ya mika mata ledan ce fanen da yayo ya dauki buta zuwa ban daki.
Nan ta samu tafa leken zaure ko Aliyu yana tafe saiko gashi ya sayar rataye da roban shi na talla a wuyan shi.
Da sauri ta tare shi ta karbi roba da kudi tai mashi magana kuskus a kune yaron ya juya da sauri yabar gidan.
Kafin maigidan ya fito ta boye roban da kudin da sauri a dakin kayan su ta kama aikin ta.
Yafito daga ban daki yana fadin yanzu zan tafi nagani idan suna can ko kuma wasa suke tsayawa yi a hannya.
Yafita tana ce mai a dawo lafiya bai amsa mata ba don a cike yake ran shi ya baci sosai.
Don shi bai wasa da hakkin iyalin shi a kan shi don haka yake matukar saka ido akan al,amarin yaran shi dama ita kan ta matar tashi.
Tun daga nesa ya hango su a zaune gaba dayan su don haka sai bai karasa kusa ba ya juya zuwa kasuwa ko zai dan kara samun wani abin tabawa a can.
Kafin ya dawo yaran sun rigashi dawowa gida Aliyu da yuwan taci ta ishe shi abinci yafara nema yaci sannan yai wanka zakace bai tafi ko ina ba .
Taja ma yaran kunne akan duk wanda yace Aliyu yana fita talla sai ta yankewa yaro kauna a gidan.
Bayan maigidan ya dawo ne yake tambayan yaran inda suke tsayawa basu zuwa makaranta da wuri yanzu.
Sai cewa sukayi suna zuwa andai canza masu ajine malam baiganin su yanzu.
Haka yasa yaja bakin shi yai shiru ya yarda da maganan su tunda ya gansu dazun a makaranta sabanin yadda malamin ya fada mai.
Haka Aliyu yaci gaba da zuwa tallan ruwan shi batare da mahaifin su ya fahinci komai ba tunda shi ba mai zaman gida bane ko yaushe.
Haka yaron ke kawo mata dan kudi itako tana bunkasa bankin ta dashi kullun tana farin ciki.
****** ********* ******
Tun ranan da akai wanan rikicin a gidan hankalin Bintu a tashe yake da mutanen gidan baki dayan su.
Ance babban gida babban magana ashe har da ita da take ganin ta kama kanta da kowa a gidan bata tsira ba ga matan gidan.
Don har da zaman ta gurin Maji ya tsone masu ido sai yanzu tagane nufin maji na bata magani tare da sauran diyan ta a baya.
Gashi yau Alhaji da kan shi yake fadin korafin da sauran matan shi sukayi a gidan kan zaman ta da Maji.
Wanda ba komai suke wa kishi ba sai basu kaunan suga ta karu da komai kankantan abu a gidan,
Wanan dalilin gitinan yasa damuwa ya dan fara yiwa Bintu yawa arai sai kafa kafa take da komai a gidan.
Tun da har mai gidan yai mata warning din shiga harkokin mutananen gidan shi da kan, shi.
Sai lokacin take mai jin zafin gwagonta hajiyan masa da tazo gidan mutane ta yar da ita kamar wata wacce bata da uba ko gata.
Da uwarta da uban da ransu a duniya amma yau ta zama,marainiyar karfi da yaji a duniya.
Ba don Maji mace ce mai halin alheri ba da bata san iya inda al,amarinta zai tsaya,ba a,rayuwa.
Amma gashi Allah ya hada ta da mace tagari wace tasan ciwon kanta tasan zafin ta a rayuwa.
Ta rike ta amana tankar itace ta haife ta ko kuma ince wata yar uwarta ta jini can daban.
Yanzu Bintu ko falon maji bata son zama da yawa ko yause tana cikin dakin su a kumshe.
Idan kuma aiki tafito yi zata yishi gudu gudu ta gaba ta kara komawa tashige daki wai ita tana taka tsatsan da kanta.
A haka zancen tafiyan sadauki zuwa kwallon farko da zai fara fita ya buga yazo masu.
Maji bata zauna ba sai faman karban taimako take akan dan nata akan shaye shaye da kuma na tsarin jikin shi.
A cikin hakane maji tace wa yaranta su shirya sukaiwa kakan in su ziyara kafin yatafi don kada sai yatafi su samu labari baza suji dadi ba.
Sadauki bai so wanan tafiyan ba amma ba yadda zaiyi ya zama dole yabi umurnin iyayen shi.
Sai faman shiri suke amma Maji bataji duriyar Bintu ba don ko falo bata fito ba don ba,a shiga makaranta ranan.
Da kanta tashiga dakin na yaran tun zuwan Bintu gidan ko yaushe zaka samu dakin tsab dashi ba wani datti a cikin shi kaman baya can da dakin yake motsutsu kowa na kyashin gyarawa .
Kwance ta samay ta ta kifa kanta a saman filon da ta ke akai.
A hankali maji takira sunan ta,da Fatima abinda ya dan sata firgita ke nan don bata san da shigowan Maji dakin ba a lokacin.
Cikin dan firgita ta amsa da na,am mama tare da saurin kokarin mikewa zaune daga kwanciyan da take.
Zama maji tayi daga gefen ta tare da dan kura mata ido tana cewa waiko lafiyan ki kalau kuwa Fatima?
May ke damuwanki ne duk kwanakin nan kin koma,shiru kina kuma nisanta kanki da kowan mu?
Dan murmushi Bintu ta kirkiro a fuskanta tana cewa ba komai mama kaina ne ke dan ciwo shine nadan kwanta.
Tun yaushe kanki ke maki ciwo baki fada min ba fatima baki sha magani ba yaya zaki ji sauki.
Shiru Bintu tayi tana fadin dama gashi zamuyi tafiya zuwa garin mu gobe tunda safe gashi kuma baki da lafiya.
Don haka dole na barki nan har mu dawo don ba,a daukan ciwo akai kauye.
Da sauri Bintu ta daga kai ta kalli Maji, sai kuma ta dukar da kanta don bata iya jure kallonta ido da ido haka.
Maji da ta fahinci may Bintu take nufi sai tace kada ki damu ba,a nan zanbarki ba gurin hajiya kubura zan barki don kwana biyu zamuyi mu dawo insha Allahu.ko kuma guda yadda dai tafiyan namu ya kasance don wanan mai tafiyan.
Bintu ta kara kallon Maji alaman ranta baizo hakan ba take cewa mama da abarni ko anan din zan iya zama ai.
A,a haba Fatima yaya zanbarki karaman yarinya dake a daki ke kadai kuma gashi ko lafiya,bai isheki ba ma.
Kada ki dmu nasan zata rike ki da kyau har mu dawo daga tafiyan, kamar Bintu tace taji sauki zata tafi amma kuma sai take cewa tau mama.
Maji tamike tana cewa don haka saiki shirya kayanki wanda zaki dauka tun yau ki koma can.
Bintu tanaji tana gani Maji da kanta ta dauki dan jakar kayan ta zuwa dakin hajiya kubura.
Nan suka dan zauna suka taba hira a tsakanin inda tai mata sallama dacewa gobe asubanci zasuyi zuwa tafiyan su.
Hakan akayi don koda gari ya waye har sun tafi ko don can ne kauyen Niger state iyayyen ta suka koma da zama don noma.
Bintu bata farka,ba don maganin da tasha mai sa barci sai zuwa takwas na safe lokacin har hajiya kubura ta shirya zuwa gurin aiki tana cikin uniform din ta.
Dakin da Bintu take ta leka tasamay ta zaune tana lazumi ta idar da sallah a lokacin.
Kin tashi Binta ya jikin naki Bintu ta amsa a sanyaye da Alhamdullahi ga breakfast din ki a falo idan kinyi wanka sai kici ni zan fita sai na,dawo.
Sai kindawo mummy ta bata amsa tare da kokarin mikewa da ga saman abin sallah da take zaune akai.
Zuwa rana kadan ta dan samu sauki nan ta mike tafara gyaran part din sai da taima ko ina tsab a part din sai bedroom din mummy ne kawai da ke a kulle bata gyara ba.
Tana gamawa tashiga tai wanka bayan tafito ne ta dan zauna sai kuma tai tunanen kada su dawo da yaran ta basu samu abinci ba.
Kitchen din ta shiga inda ta samay shi sabanin na Maji don wanan komai na zamani ne a cikin sa.
Ga kayan abinci na kala kala babu abinda babu cikin sa komai gashi kamar ba saye akeyi ba.
Ta yanke shawaran tai masu tuwo don taga kullun yaran ta na zuwo rokon tuwo a gurin maji don ita bata da time din tukawa ko yaushe busy take.
Nan ba bata lokaci ta girka tiemwon shinkafa da miyan agushi da manja tai amfani da naman da tagani a fridge din.
Gashi ranan girkintane ta kwashe a wani kula da bai saurin sanyi takara hada masu pepper surp din kayan cikin rago da drinks din hannu na kayan fruit din data gani a kitchen din.
Takara gyara gurin ya koma tsab takoma daki ta kwanta sai yamma mummy tadawo da yaran ta inda tun a,wajen part din ta soma ganin canjin yanayin shiyan nata.
Tana shiga dakin gaba daya taga duk ya canza mata sai ta tuna da lokacin da take amarya a gidan komai nata tsab yake a lokacin.
Ba irin yanzu ba da,bata da lokacin tsayawa gyara komai kamar yadda ya dace mace tana gida tayi.
Yaran suna shiga daki suka fara ihun da murnan ganin yadda komai nasu ya canza a lokaci guda.
Dan karamin sune yafara maganan abinci Bintu dake fitowa daga dakin da take ciki take cewa Anwar zo ga abinci can kazo kaci taja hannin yaron inda ta tsaya daga kofa tanawa mummy sannu da dawowa.
Mummy tace Bintu ke da baki da lafiya kika sha wanan aiki haka sannu da fama nagode.
Tana fitowa taga Anwar a hannun ta take cewa kaikuma may yafaru Bintu tace wai abinci zaici.
Uwar tace kaida andawo kace zakaci abinci har yaushe muka dawo na girka maku abinci.
Bintu tace a sanyaye mummy ai na yi girki tun dazun ma nagama bari na debo mai.
Da mamaki uwar tace kinyi girki Bintu bayan wanan uban aikin da kikasha haka.
Murmushi Bintu tayi ta juya rike da hannun yaron ta debo mashi abinci ta zauna tafara bashi.
Saiga Mummy tafito daga daki idon ta ya sauka akan plate din da yaron ke cin abinci take taga mai Bintu ta girka masu.
Wani irin dafi ne ya kumay ta tace kai amma wanan yarinyar Allah yai maki albarka.
Nan tashiga kitchen ta samu komai tsab kamar ko ina mamakine ya kama yadda karamar yarinya kamar Bintu tai irin aiki haka mai yawa ita kadai.
Gashi kuma,ba lafiya ne take dashi ba ajikin ta take taji kwadayin zama da yarinyar ya kamata don irin haka take son yaron ta dashi.
Ba,wani abinda aka taba mata ko aka lalata hatta sharan da tayi bata zubar ba ta tara a wani roba har mummy din tazo tagani idan babu abinda take so daga ciki dai a zubar dashi.
Haka mummy ta dinga jin dadin zama da Bintu kamar kada uwar rikon ta tadawo take ji.
Suko matan gidan ai nan gulma ya fara tashi akan zaman Bintu gurin Hajiya kubura na kwana biyu kafin maji ta dawo don ance babban gida ba,a raina dan magana kadan,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,
A LOKACIN MU KE,,,,
Washe gari da safe sadauki yana dakin Maji saman dogon kujera ya dan nade hannayen shi a saman kirjin shi idanuwan shi duk suna a lumshe, zakace barcin safe yau yake a falon mahaifiyar tashi.
Duk zirga, zirgan da sisters din shi keyi yana jin su sai dai idanuwan shi a,rufe suke still zakace barci yakeyi.
Maji ta,shigo dakin daga part din maigidan take, tana ganin Sadauki a falo tun da farar safiya haka sai taja tai turus tana kallon shi cikin mamaki.
Ba tare da ya sauke hannun shi dake saman fuskan shi ba, ya ke cewa Maji barka da asuba, jin haka,ya,sata sauke ajiyan zuciya takarasa gare shi cikin yanayin mamaki.
Yau kuma a,nan kazo ka,kwanta muna da,safe haka ko har yanzun kana kewar namu ne.
Murmushi kawai yayi wanda har yakai ga sauke hannun shi da ya kare fuskan shi dashi da,farko.
Maji bana son Baba ya fita bamu gaisa da,shi ba shiyasa na zo nan nake jiran ya,shirya sai na shiga gurin shi mu gaisa.
Maji ta,karaso cikin dakin tana fadin a to tin dai jiya naji ya fara tambayan ka idan ka wuce yanzu za,a jiku dashi,
Yace cikin kara kwantar da kan shi bama za,a jimu ba insha Allahu maji,
Maryam ce ta katse su da fadin Maji tun dazun nake jira kizo sauran madaran da ya,rage shine Bintu ta dauka wai tana hadawa yaya tea dashi .
Kai maryam baki da hakkuri wallahi jiyane fa kayan tean namu ya kare shine har kin fara raki haka.
Sai a lokacin ya daga idanuwan shi da,sukai ja yake cewa No ni kubar shi bazan sha tea ba,sauran tuwo nake son ci ni.
Yana kokarin tura hannun shi cikin aljihun wandon shi ya ciro kudi masu yawa yace wa marya karbi jeki sayo maku kayan tea ku karya kafin na,fita.
Tana mika hannu zata karba ne, Maji ke fadi kai haba Sadauki na fada maka ka daina wanan kashin kudin haka.
A hankali ya mike zaune da kyau yana fadin