Showing 315001 words to 318000 words out of 373688 words

Chapter 106 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

da azahar muka bar garin sokoto zuwa sadauya mun sauka da dare inda akai muna screening motan da ke jiran mu muka shiga sai wani hotel nan muka kwana a jidda sai da safe muka wuce zuwa madina.
Ibada sosai mukeyi ba kama hannun yaro har su umma da mama sun bani mamaki sosai yadda naga suna ibadan su sai dai bawai sun bar halinsu bane ko acan.
Adduoina sun fi yawa ne akan Allah ya shirya min yaya sadauki da samun zuria masu albarka dam yan uwa musulmai da suka fada cikin irin wanan halin .
Sai dai a can ni da mummy muka zama kamar kawaye sai mama da muke tare da ita wani lokaci don mama bata da time din wasa ko kadan ko yaushe cikin ibada take .
Mun bar madina mun nufi makka a can mukai kwana goma muka fara shirin dawowan su gida mu anan zamuyi sallah two days after sallah zamu wuce chaina din.
Ana gobe zasu tafine ina makale da mama da mummy da wani iri shakuwa ya shiga tsakanin mu yanzun da ita.
A can nice mama take sakawa na zaba masu abubuwa ni da mummy wanda kusan sayayan na Amira ne da naji ance wai zatai aure bada dadewa ba.
Har gado nice yaya yasa a gaba na zabi gadaje har guda biyar masu kyau.
Da,safe mukai masu rakiya suka tafi muna tsaye muna kallon su ba yadda zan yi ban san lokacin da hawaye ya zubo min ba.
Muna motane yai dan murmushi tare da rungumoni zuwa jikin shi na langabe kaina ina share hawaye a hankali yace baki son rabuwa da mama ko?
Ban yi magana ba sai ajiyan zuciyar da nayi kawai muka kai masaukin mu wanka mukayi muka nufi masallaci gurin sallah sai dare sosai muka dan huta kwana biyu duk a cikin masallaci mukayi shi.
Ranan sallah na saka wani dogon rigan mai tsananin tsada da ya sayo min a wani katon shago na kayan mata.
Rigan da gani ta matan manya ce irin tasu sai wace ta isa take sayanta
Na yafa mayafin rigan take na koma kamar irin matan manyan larabawan da muke gani ko kuma matar wani kusa a kasan mu.
Ga zubbunan gold da na saka guda biyu a yatsuna wuyana kuma Diamond ne kiran Dubai sai takalma mai tudu da yar karamar jakan takalma dana rika a hannu na sai wani kamshin turaren larabawa ke tashi a jikina.
Yana falo zaune na fito a cikin shirina wani irin mugun kishina ne ya darsu a zuciyar shi.
Na karaso inda yake zaune shima kayan maza yasa na larabawa masu tsada na karaso inda yake zaune cikin wani takon da ban san inayin shi ba.
Wani kamshi ne ya daki hancin shi har ya saukan mai da kasala a lokaci daya.
Ya sake idon shi yana kallona har na karaso gare shi tare da,dan fadawa jikin shi ina cewa yayana barka da sallah.
Yace Fatima anya kuwa kece haka ko dai an canza min matane nace bari ka tabbatar da ni dince to na dan kai mai wani guntun cizo a kunnen shi ya dan saki wani dan kara yace muguwa.
Na mike ina dariya yace Fatima kinyi kyau kinyi kyau sosai wallahi ban san may yasa duk dogon rigar da zaki saka sai naga tai matukar karban ki kaman don ke aka dinkata ba ?
Gaskiya kafin mu bar garin nan sai na kara saya maki irin dogayen rigunan nan da yawa koda mun koma gida ki dinga min kwaliya haka dasu.
Nace kai haba yaya kaface da tsada ka,sayo su fa ai biyun nan ma sun isa haka please.
Yace Fatima shigan ki a cikin suturun alfarma shine mutunci na ga idon idon jama,a shigar ki shine zai nunawa duniya ni Umar ina sauke hakkina akan iyalina.
Ya jawoni da hannu daya na fada a jikin shi yace bakin san ko waye mijin ki ba ko bakin U F ba ko Fatima ?
Nai dariya tare da dan shafo fuskan shi da hannu daya yai murmushi nace niko nasan waye mijina don ni nasan kayana.
Yace to ki godewa Allah daya baki Umar a matsayin mijin auren ki uban diyan ki nan gaba kuma.
Yace Fatima mijin ki mai tsada ne mai daraja kuma a idon jama,a sai dai a idon mutum biyu zuwa uku ne kawai yake mai rauni.
Dariya nayi nace idona dana mama ke nan na ukun ne ban sani ba yace na ukun shi ne baba.
Kai yaya kada kaiwa baba haka wallahi tun haihuwan ka har yau baba baida wani da dayake ji dashi kamar ka a duniyan nan.
Iyya fa ta fada min irin son da baba ke maka tun haihuwan ka har ya kai su Umma suna kishin ka tun kana karami har yanzu.
Murmushi yayi tare da jawoni jikin shi yana sinsina na kamar ya samu handkici mai kamshi yacs nasani Fatima nima nasani wallahi.
Iyya Rabi batai karya ba son da baba ke min yasa su imma suka sakani a gaba da horo tun ina karami ga mamanki da shegen hakkuri duk abinda akai min kona fada mata bata cewa komai sai dai tace min inyi hakkuri kawai.
Ya kara motsoni a jikin shi yace kin san may fatima nace ,a,a yayana yace watarana har nakan zargi su Umma a raina akan da hannun su a cikin lalacewa na a baya.
Sai dai zato zunubine koda ya zama gaskiya Astagafullah amma yadda suke gwada min bana jin dadi Fatima.
Sun hana diyan su hurda dani sun hana mutanen shiya ma hurda dani haka yasa na kasance ban da aboki sai bashar.
Bashar yai min kokari a rayuna na Fatima banda kamar bashar a duniyan nan kuma na san har gobe banda kaman shi wallahi.
Yace humma Fatima idan ina tuna wasu abubuwa bazan iya koda gaisawa da Umma da mama a duniyan nan.
Yace akwai lokacin da maji tai tafiya wallahi abinci hana min shi sukayi haka nake takawa da kafa har gidan su bashar a can zanci insha sai dare zan kamo hanya na dawo gida da kafa.
Wata rana ruwa ya hana naje gidan su bashar cin abinci na shiga gida ko zan samu wanda ta tausaya min cikin su ya bani ga abinci ina gani amma sukace min wai na Ahmed ne da Imirana.
Nadawo dakin mu da yuwa sai ga Bashar cikin ruwan nan ya aro mashin din makwabcin su bai ko iya tuki sosai ba yakawo min abinci shi naci har dare na kwanta.
Ga maji bata dawo ba aai ashe tayi yaji ne ta tafi gida ban sani ba lokacin tana goyon Amirah.
Kin san may nacece mai a,a lokacin duk jikina yai sa yi ga labarin da yake bani yace wallahi a lokacin ne na fara shaye shaye tun ina da fifteen year Fatima.
Idanuwana na runtse don jin abinda ya fadi nan yai ta bani labarin irin musguna mashi dasu Umma sukai tayi har mama ta dawo.
Yace ni mummy batai min komai ba wallahi don daidai da rana daya duk da nasan itama tana kishina kan wai baba yafi so na da diyanta amma tana boye zafin kishin ta akaina.
Don Allah Fatima duk zafin kishin ki a kaina kada ki mu,amula da masu sihiri bala,i ne da fadaqa halaka ga mai irin wanan halin daga karshe.
Kara shigewa jikin shi nayi nace kada Allah ya bani kwandalan zuwa gidan boka ko malam wanda zan illanta rayuwa wani bawan Allah.
Munje sallah idi muka dawo bamu sake fita don ansha ruwa ba azumi muna gida muna farautawa nunan mu rai.

****** ********* ******
Mun sauka a China inda na kara tsinkewa yaya ke nan irin abokan da nagan shi da su can har sun so sufi na saudiya ma don ko a can naga yadda yake hurda da yaran masu kudin kasan ga kyautan dana samu har tsoro abin ya bani.
Mun tafi wani katafaren hotel mai shigen tsawo da kyawo sosai kauyanci kan wallahi nayi shi sosai na lumshe idanuwa na daga inda muke zaune a bayan mota nace Alhamdullahi Ala Kulli Halin.
Yace jawoni yace may kikace Fatima nace godiya nake mikawa ga uban gijina da ya nufe ni da hakan .
Tsayawa bada labarin hotel din zai bata muna lokaci amma gaskiya nasha kallo Allah ya horewa mijin kowa yakaita kashen duniya tai kallon abin mamaki a can.
Munga karamawan ta ban girma a gurin abokan shi na can nikan sai faman godiya nake ga Allah da ya daukaka min rayuwana haka.
Ina rungumay a jikin shi muka bar gurin haraban hotel din zuwa masaukin mu a tare muka zube agado dashi.
Na lumshe idanuwa na tare da ajiyan zuciya yace yaya akayi ne Fatiman yaya ?
Nace ni may ma zance yaya dariya naji yayi yace kice kina son U F dinki sosai Fatima .
Ki dinga gyara min kanki ina kallo ko yaushe gadona yazama ready ba sai na nema ba abani idan kin min haka kin gama min komai Fatima a rayuwana.
Murmushi nayi nace ai baka da matsalar haka din ko yanzu yaya .
Yace umm haka din ne amma ba sosai yadda nake so a raina na ba jinayi ya shiga zuge min zif din rigar dake jikina a hankali tare da fada min wasu kalamai da bazan iya fadin su ba anan.
Nace ko wanka ba zamuyi ba yau kuma yace wanda mukayi kafin mu fita may mukaci dashi kada fa ki manta honey moon dina nake yanzu.
Rugumashi nayi nace ai kayi abinka tin a gidan ka na sokoto sai dai ka dora inda ka tsaya kawai.
Yace hakan za,ayi ranan kan nafitar da duk wani kunyan shi a idanuwana na nuna mashi nifa ba yar kauyen da yake kirana da ita bace.
Rayuwa sosai na jin dadi mukayi da yaya a kasan China satin mu biyu a can ya sanya hannun jari a kamfanin yin karafuna da yake son yi a sokoto.
Mun dan kara kwanaki muka wuce har Hong Kong nasha mamaki sosai yadda yaya yasan kasashen duniya haka da mutane kuma cikin yan shekarun kwallon shi.
Daga karshe muka dira a Dubai a lokacin banda matsalan komai a raina ban da na tuhumar ko yaya yabai daina sha ba har yanzun .
Don wanan irin mutanen da naga yana hurda dasu haka dole ne idan mutum.baikai zuciyar shi nesa ba ya yi aikin sabawa Allah.
Amma sai naga shi akan ibada baida wasa ko kada ko wani kasa yana da time din sallah su ko baya gida zai bugo min waya yace lokacin sallah yayi na tashi nai sallah.
A kasan Dubai kan kamar a gida Nigeria muke don yan Nigeria dake kasan maza da mata gasu nan manya da yara kana gani.
Nan naga matan manyan kasan mu yadda suke hurda da matasa ko ina zai tafi tare muke zuwa yana nuna masu ni a matsayin matar shi.
Mutane da yawa suna cewa basu taba tsanmanin yai aure ba ma a rayuwan shi don basu ji ba ana fadin zancen auren shi akasa ba.
Akwai wata hjy wai shi take so ranan da ta ganmu mun fito gurin wani shakatawa sai da ta girgiza da ganin mu.
Nagane hakan a fuskanta tun da muka hadu gasu su uku hamshakai sai wani shakiyancin duniya sukeyi wai su karuwai.
Bayan mun rabu dasu ne naso na tambaye shi ko su waye su amma sai kawai na basar da zancen su.
Shi da kan shi naji taja tsaki yace rabu da mahaukaciya wai a haka sona takeyi bata san ni ba irin shashan matasan nan bane masu kwadayin tsofin mata ba.
Ni yanzu ko budurwa bata gabana balle wata tsuhuwar kwama can na banza.
Har Lindan shi sai da muka hadu da ita a Dubai wai tazo tare da mahaufin ta wani business nace tir da kafurci ta sa ni dan skirt dan mitsitsi iya cinyar ta kawai duk komai nata a fili.
Ita kanta Linda ranan da ta ganni sai da ta girgiza sosai don yadda taga nai mata kyau ga dress din jikina ya karbe ni nan tasan dole ne U F ya manta da wata Linda can.
Tasan lalai yanzu Fatima ta sace zuciyar U F din ta don babu ta inda za a kwata mu da ita gashi kuma addinin mu daya dashi gamu yan uwa kishi ya rufe ta taji kawai tasakawa ranta hakkuri ga tunanen zai dawo gare ta wata rana.
Daga ita har mahaifinta da muka hadu wanda yasab soyayyan su da yaya sai da suka bimu da wani irin kallo .
Mahaifin Linda yake tambayan wanan ce matar shi daya aura din linda tace ita ce dadd.
Yace so young pretty how are you tare da mika min hannun shi na girgiza kaina nace mashi dai yana lafiya tare da tambayan family din shi.
Yaji dadi yai murmushi yace sorry na manta addinin ku ya hana hakan nan ya shiga muna murnan aure ya dafa yaya yana cewa kinga shi nan ki rike mijin ki da kyau don mijin ki big man ne sosai yana cikin lokacin shi.
Dariya mukayi a tare har dan dimple dina ya dan lutsa kadan .
Linda taja tsuki tace ai dole ne UF ya rikice dadd a kan wanan karamar yarinyar ji yadda ya mayar da ita kamar wata queen can .
Ta juya tabar gurin ya ce don't mind her she is jealous of you taga kin fita komai baby ki rike mijin ki kinji yarinya.
Nai mashi godiya ya bani kyautan wasu irin mahaukatan kudi kamar bau san zafin su ba.
A mota hanyan mu na dawowa ne na ciro kudin ina bawa yaya yace na may ye fa nakine fa kece akabawa don haka kibar abinki gurin ki.
Tsaraba kan nasha shi gurin yaya don bai bari na kashe koda kwandala ba daga cikin kyautan da nake samu.
Mun baro kasan mun dawo gida Nigeria don hutuna da ya kare ba don yaya yaso yakare din ba don bai gama morewa ba can.
Sai da mukai kwana uku a Abuja san nan muka ahugo jirgi zuwa sokoto birnin shehu cikin jin dadi da walwala muka iso gidan mu.
Nai mamaki kwarai yadda muka samu yan uwa sun cika muna gida gurin taron mu.
Anty maryam na ganina lokacin cikin ta ya tsufa sosai ya kara girma tazama wata mama da ita.
Muka rugumay juna muna murna daganawan mu again ta sake ni tace wai ko Fatima don Alkah kece haka kodai yaya yakaiki cikin injin ne please.
Na dan shafo cikin ta nace masha Allah ubangiji ya raba lafiya ya bamu mai albarka.
Nan muka samu yan uwa sun cika falon sai faman sanu suke muna kowa kallon mamaki yake min don ganin yadda gaba daya na sauya na koma,wata yar larabawa dani abu ga dana,asalin buzaye.
Mun samu a girka abinci kala kala wanda nasan aikin maryam ce haka na.
Ban lura da Anty Amira a falon ba sai da naji yace mata haba sweet sister ba ko gaisuwa ne ?
Sai lokacin na dago na dubi inda yake kallo tana zaune ta yi irin zaman dacta saba yi ta dunkule saman kujera sai chatting takeyi abinta.
Ashe tun shigowan mu ta daga kai ta kalle mu taji wani abu ya tsaya mata arai irin yadda gaba daya taga na koma wata matar manya ko diyar manya can dani sai kamshi da annuri ke tashi gare ni.
Gani cikin wani irin dogon riga kore yaji duwatsu tun daga sama har kasan shi hannayen rigan shara shara na yafa mayafin rigan a kaina ina rataye da jakka ja da takalma mai duwatsu kamar na rigan.
Ga yan uwan su sai haba haba sukeyi dani mu kamar sunga wata basarkiya can daban.
Haushi ya kumay ta tace wai wanan Bintun kauyen ne yau ta murje ta zama haka da ita kai kai maji why please maji taja wani dogon tsuki tamike tana fadin ita zata tafi gida ke nan.
Nace a,a haba Anty Amira yanzun nan da shigowan mu hatta hausana ya sake ba sakwatancin nan sosai a cikin shi .
Tace a,wulakance wani abun kuma zan tsaya nai maki bayan naga kun sauka lafiya ko so kike na tsaye ina,fadanci a kanki kuma ?



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YABI MUNA HAKKIN MU AKAN KI,


Yana isa zuwa yamma ya bar garin ya wuce zuwa lagos inda zai tafi ghana daga can gurin business din shi.
Yana can ya bugo min washegari lokacin na tashi nai wanka ina shiryawa wayan shi yashigo na dauka tare da gaidashi yake tambayana jikin yayi sauki ko nace na samu lafiya sosai.
Dama ai idan na shiga mota ne kawai nai tafiya mai nisa nake jin haka.
Mundayi hira yana tambayana mutanen gida nace duk suna lafiya yace nagaida su nai mai Allah ya tsare yaba da sa,an tafiya muka kashe waya.
Sai dana shirya ne mama tashigo dakin tana ce min karyawa fa nace mata da,dai akwai dumamay tuwo ne shi nake son ci.
Tuwon aka dumamon


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login