Showing 183001 words to 186000 words out of 373688 words
Chapter 62 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt
ya tashi ku kira likita yace a kirashi akwai abinda za,aimashi.
Daga haka ya fice dakin ni ina daga waje ban ma san yadda suka kwasa ba a cikin dakin.
An dan jima kadan Kabir yafito daga dakin nan na mike nazo ti mashi rakiya zuwa inda motar shi take.
Mun dan fara,tafiya,yana cewa,gaskiya jikin yai kyau don da,Alaman aikin anyi sa,a sosai gare shi.
Nace sai dai Baba ya ji jiki sosai wallahi ya dai samu gatane shine har yai saurin murmurewa haka.
Sunana naji yakira, murya a sanyaye yace Fatimatu don Allah may ke tsakanin ki da,wanan yayan naki na nan garin wanda ya shigo dazun ina ciki.
Nace wa ke nan don ban kula da,wanda ya shigo dakin ba ina can baya ni.
Yace wanan da,muka,taba gaisawa dashi acan gidan ku mana wani farin guy haka, mai dan tsawo kadan, mai karfi haka.
Nace,wai duk wanan kwatancen haka yaya sadauki ne mana dan mamana na,garin nan shi kadai ne danta namiji a duniya.
Kuma dan kwallo kila ma kana jin sunan shi don har kasan waje yake fita wasan kwallo sosai.
Nace ummumm wama suke kiran shi ne da,guy name din yan kwallo sai can na tuna nace U F sukekiranshi.
Yace au shine dama UF dan kwallon jahar nan tamu lalai ina jin sunan shi ko sosai wallahi a lailai guy din dollars sun zauna don yana kawo wuta sosai ga kasan nan anaji dashi.
Nace lalai ma ni ban damu da harkan kwallo ba balle nasan wani abu acikin sa sosai.
Sai tambayan da ya jefo min ta bazata na a kunnuwa na yana fadin to may ke tsakanin ki da shi Fatima.
Da,sauri na juyo tare da,dakatawa,da,tafiyan da nakeyi nai may tambayan hausawa tambaya cikin tambaya.
Nace washi yaya sadauki din yace sunan shi kuma ke nan ko nace eh UMAR FARUQ yake shine ma,anan UF din ai yace ok.
Nace sai ban fahinci tambayan da kai min ba nacewa may ke tsakani na dashi nace yayana ne mana, dakin mu guda dashi ai dan fa mamane na fada maka tun farko.
Yace nasani kin fada min, shima yaja ya tsaya wuri daya tare da fuskanta na da,kyau.
Fuskan shi ta nuna min damuwa acikin ta karara nace ba wani abu a tsakani da shi sai yan uwan taka kawai, amatsayin yaya yake gare ni.
Sai naga yai murmushi mai ma,ana da magana can ya nisa yace badon na fadi wani magana ai fushi dani ba dana fadi abinda nagani a zuciyar shi.
Nace kaga yana matukar jin haushi na ko wallahi haka yake mugu ne tun da nazo gidan su zama yani gaba da hattara da tsangwama.
Shi kullun yar kauye da munafuka yakw ce min don kawai yaga mama tana so na.
Fatima nace na,am sai yayai shiru can yadan harde hannayen shi gaban kirjin shi tare da kallo na ido da ido yace .
Wanan yayan naki sadauki yana son ki na hango kishin ki karara a kwayar idon shi wanda ba kowa ne zai fahinci hakan ba sai wanda ya kwantar da hankalin shi sosai zai gane hakan.
Wani kallo nai mashi na amma baka san komai ba nace, haba yaya kabir har may ya rufe maka ido yasa ka fada min wanan magana haka.
Mutumin da ko kashe ni yana iya yi don haushi da takaici na da yake ji zakace wai yana so na.
Ni may ma zanyi da wanan may bakar zuciyar kamar arnakun farko.
Wai tsaya ko don kaga ya taimakawa mahaifina ne yasa ka fadi wanan maganan?
Nasan ba,shi yai niyar hakan ba uwarshi ce ta sakashi yai taimaka muna don tasan yana taimakon mara shi a gari.
Yace to is OK tunda baki yarda ba amma watarana zakice nace nidai don Allah ki rike min amanan kanki don wallahi ina tsoro don zantafi zuciyana yana min kwankwanto ga abinda na gani.
Take naji raina ya baci nace ni wallahi yaya Kabir har ka bata min rai ko na rasa miji may zanyi da wanan mugun mara imani.
Dariya yayi yace shike nan tun da naji haka ga bakin ki da zaran an sallami baba zan turo da kaya a kawo wa mama kamar yadda nace don komai an hada kawowa kawai ya rage.
Nace ni dai yaya Kabir da dai zakayi hakkuri har na kare karatuna da zaifi sauki wallahi.
Yace wa ni ance abari ya huce shi ke kawo rabon wani don haka akarashi a gidana na san na kama abina a hannu kafin ai min sakiyar da ba ruwa.
Yabude motan shi ya shiga har ya zauna sai kuma yafito yace wallahi ina ji kamar kada na wuce nabarki da wannan mayen dana hango nai dariya nace kai zuciya mai nashe nashe wallahi.
Ni ai wanan da kakw gani yafi karfin aure na don shi ba kalana bane ka bar wanan zancen kawai don Allah.
Yace to tunda kince hakana na gamsu yanzu sosai sai mun yi waya ke nan idan na isa gida nace Allah ya tsare idan kaje a gayar min da su Antyna da yaran.
Yace zasu ji insha Allahu yatayar da mota tare da yi min horn na daga mai hannu yafice daga harabar asibitin, saida naga security sun daga mai kofa fita daga get din na juya zuwa ciki.
****** ********* ******
Kwana biyu bayan haka aka sallami babana daga asibiti sai dai sunce bayan sati biyu ya dawo a kara duba lafiyan shi da aikin jikin shi.
A zatona zasu wuce gida amma sai Baba yace ba zai bari su koma ba ya tsaya gari har sati biyun ya cika gidan gwagona aka gyara mashi nan suka zauna da mama tabawa.
Komai sadauki yana masu duk da baya gari amma bashar abokin shi yana zuwa kai da kai yana duba lafiyan su.
Hakan yaiwa Maji dadi sosai da yadawo ranan ina jin tana mashi godiya sai cewa yayi haba Maji ai taimako kamar yiwa kaine abinda ka taimaki wani dashi shine rabonka.
Ban mata da yadda yarinyar nan itama ta taimaka maki ba da kike asibiti wanan ne kawai zamuyi mata mu saka mata da abinda tai muna muma.
Allah yai maka albarka, sadauki halinka na alheri ya bika duk inda kake Allah ubangiji yasa kafi haka a rayuwan ka.
Yaji dadin wanan adduan sosai don ya kasa boye farinciki sai cewa yayi Maji ina jin dadin adduan ki akaina ko yaushe tace ba dole na ba baba na .
Kaine farin cikin rayuwan mu ni da yan uwanka dama,wasu al,umma dake ci daga gareka.
Yace mata zai fita akwai inda yake son zuwa don akwai wani da suke son hada business dashi na mai.
Tace to Allah yaba da sa,a har yakai kofa zai fita take ce mai ai na manta za,afa kawo kayan lefen Fatima nan da kwana uku insha Allahu.
Don haka nake son kudi don nai shirye shiryen taron su.
Yace maji wanan ai maganan ku ne, ni dai bana son ki zauna ba kudi a hannun ki bani jin dadin irin haka.
Idan na fita zan ciro maki kudi, sai na kawo maki idan bai isa ba sai akara maku.
Har ya juya sai yake cewa amma maji wai sauri may wanan yarinyar takeyi, hakane da take son aure.
Wani kallo ta,watso mashi, tace shi aure ga yarinyar da takai sha biyar zuwa sama har wani abu ne yanzu.
Fita yayi kawai bai tsaya ba don yasan fadan zai kawo kan shi idan har baiyi hankali ba.
Ina wanki duk ina jin hiran su nace tunda kowa irin kane da bai tsoron Allah zauna har mutuwa ta riske ka ahaka.
Kamar yadda Kabir yace ranan laraba za,a kawo kayan lefena a gurin mama hakan ne kuwa,don ranan mama da,su Amirah basu huta ba sai aikin abincin masu kawo kaya sukeyi.
Maji ta,gaiyaci abokan arzikin ta daga ko ina a cikin gari kamar yadda akeyi.
Karfe hudu na yamma gida ya cika da abokan arzikin mama masu zuwa mata karan karban kayan lefen diyar ta.
Nayi kwalliya cikin wani swiss lace kore anyi min dinkin riga da siket Amira ta daura min dan kwali gashina ya zubo daga baya.
Sai dai ban fito ba ina dakin mu zaune don kunya daga cikin kawayen mama wasu ke fadin basu gane ni ba nan mama ta,tura Maryam data kirani nazo na gaida mutanen ta.
Maryam ta shigo cikin dakin ta samayni zaune nayi shiru tace Amarsu ta ango may ye haka kuma ranan farinciki kin zauna kinyi wani tagumi dake.
Nace kai anty maryam ni wallahi ina tunanen wanan kokarin na mamana ne kawai .
Tace ke taso su hajiya Larai na son ganin ki wai sunce basu san ki ba shine maji tace na kiraki ku gaisa.
Nai wani iri nace walkahi Anty maryam kunya nakw ji tajawo min gyale na dake gefe na fari ta dora min akai amma can bayan tuntun kaina ya tsaya.
Tare muka fito fallon dasu duk a kunyace nake idona yana kasa sai da nakai kasa na tsugun na a tsakiyan falon nace masu mama ina wunin ku?
Tubarkallah masha Allahu suke fadi hajiya maijidda wanan yar taki haka kamar ita tai kan ta dayar matan tace may ma sunan ta maryam na dariya na yadda duk na tsorace tace masu Fatima Bintu.
Sukace diyar ma,aikin Allah sai lokacin na daga kai na dan kalle su sake rudewa nayi da ganin su manyan mata ne hamshakai ban taba sanin mama tana da kawaye haka ba don banga tafaye fita,ba ita.
Naje gurin matar na zauna tace Allah yasa angon naki shima haka yake kamar ki zama nayi daidai kafar matan tace kaji arziki ba yarinyar da kunyanta yaushe za,a samu yara masu kunya haka wanan nan zamani aida yanzu muna nan dasu suna rawan kai.
Matar ta dan duko tana ce min kina karatu kuwa na ce eh tace a ina ?
Nace a hankali nan state university nake two hundred level.
Masha Allahu duk a kunyace nake zaune cikin su sai hiran duniya sukeyi.
Dayar matar take ce min jeki kin ji diyata don naga kinki sakin jikin ki namike cikin natsuwa nabar falon .
Ban karasa shiga ba naji wata na cewa kai amma hjy maijidda kin ban mamaki yaushe zaki bari wanan daman ya,wuce ki haka, aida kawai kin kamawa danki wanan zukekiyar yarinyar haka ga yarinya da kunya da sanin ya kamata.
Ban fi minti goma ba da shiga masu kawo kaya,suka iso da gudan su yan uwan shi ne mata su shidda suka shigo da,akwatina set biyu masu kyau da daukan ido.
Nan nake jin an shiga guda da yabon kaya basu dade ba suka ce zasu tafi aka bisu da kayan da aka hada masu drinks, kajin da aka soya, da su snacks.
Sai kudi tukwici dubu hamsin har mota aka kai masu nan aka dawo falo akabaje aka,shiga bude kayan ana yabawa.
Naji wata na fadin inji bata da ciwon kai dai ko da sauri maryam tace har biyu kuwa.
Kai tana da kishiya fa a,a,a yarinya kinko debo da zafi kamar wanan yar yarinyar ce za,ta shiga cikin mata biyu.
To Allah ya tsare ya kare ai sai ku tashi tsaye do dai kema gaki kina fama danaki a gida.
Zuwa yamma kowa ya watse gidan aka barmu iyamu hajiya kubura ce zance naji muryanta lokacin da aka kawo kayan har aka tafi tana falon tana yaba kyaun kayan .
Sai dare muka samu kan mu sai kuma a lokacin nafito ban kai minti biyar da zama ba yaya sadauki yashigo falon.
Ina cikin kwalliya na ban cire ba idon shi suka kai ga,akwatinan yazauna yana cewa har bakin naku zun tafi ke nan.
Amira tace su wuce sunzo wallahi kagama kayan da,suka kawo muna can.
Maryann tace kai yaya,wallahi kabir yai kokari sosai wallahi yana nuna yana matukar son Bintu ji wanan uban kaya haka haddadu dasu bari na,dauko maka kagani sai ta mike zuwa gurin kayan.
Yace ke ina wasa da kene ni mace ce da zan tsaya kallon wasu tarkacen banza can.
Da sauri nadago kai ina kallon shi don jin abinda yace, ya watso min harara tare da jan tsuki yace karamar yarinya sai shegen son aure haka.
Wanan tarkace kikewa rawan kan aure jekiyi ke kika sani indai wanan tsohon ne dana ga kina rawan kai akan shi.
Nace a hankali adaibar min abina ko yafi duniya tsufa ina son shi hakana .
Baki da kunya wallahi nike fadawa hakan na juya ina magana kasa kasa nikadai inda nake zaune.
Wai sadauki ban san wanan abinba yanzu shi Kabir din ne tsoho kuma koma dai may ye haka take son abinta sai kaje can kaji dashi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,
IDAN KIN TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA BA MU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAR MUNA AKAN KI,,,,,
Maji ne zaune falon Alhaji dake cin abincin da takawo mashi, abincin yai mashi dadi sosai kullun yana son cin girkin da maji da yaranta ke hada mashi idan itace da girki.
Tv daga bangon falon da ka shigo dashi zakai arba ya na aiki yakai tashan CNN yana kallon news da akeyi.
Ahmad ne ya shigo falon da wani takarda a hannun shi, yana cewa uban ga takardun an karbo sai ka saka hannu a mayar masu gobe.
Imirana kun dawo yaya kasuwan amma kaman baiji gaisuwan da maji take mashi ba alokacin.
Saida ya gama bin takardan ya dago yana fadin, bakaji ana maka sannu ne ka kyale ta.
Ya dan juya inda maji ke zaune ya watsa mata wani kallo mai kama da harara.
Duk a idon mahaifin shi Alhaji yace yanzu kai da girman ka kana namiji kake shiga harka irin ta mata.
Imirah yace may kuma nayi baba gaisuwa ce taimin kuma na ansa a rai na ai.
Yace to lalai ashe da sauran ka kuma ka bani kunya kai da yau idan na kwanta dama, kaine zaka zama min jigo a gidana.
Ashe hasashen na ba haka bane yanzu nasan ko bani Umar zai iya hada ku ya rike min don shi banga ya banbanta wata daga cikin gidan nan ba.
Ni dama baba ai nasan baka daukan mu yanzu da wani matsayi tunda mu bamu ,,,,
Cikin tsawa Alhaji yace ashe rashin kunyan naka Imirah har yakai haka ban sani ba ?
Yau ni kake kallo ina fadu kana fadi haka kai tsaye babu jin kunya.
Imrah baiyi magana ba ya juya yafita daga dakin rai a bace sai dakin uwar shi.
Maji tace Alhaji da baka biye mashi ba ai, don ni wanan halin na riga na saba dashi ko a gidan nan .
Babu wani yaron gidan nan dake kallona da daraja a matsayin uwa sai diyan hjy Kubura kawai.
Tace don haka don Allah ka daina fadan abinda da duk kaga sunyi min a gaban ka.
Don bazasu daina ba saboda kullun huduban shedan ake masu a kaina.
To Allah ya,sawaka amma gaskiya ba zan lamunci irin haka ba a gidana.
Sai muryan Umma sukaji tana fadin anki agaishe ki din ke waye da sai angaisheki.
Shi da ya mayar dake wata tsiya sai ya zauna yai tayi amma babu mai tirsasawa diya na akan wata mace can marasa asali da ta cika muna gida da diyan tsiya diyan taulali da suka zama ma mutane alkakan kafa.
Maji dai ta fito daga dakin maigidan da kayan abincin da,ta kwaso daga gurin shi.
Muna fuka kawai tun shigowan ki gidan nan kan Alhaji ya burge saboda bakin kilibibin ki wai ke ga,saliha.
Maji tace yaya Allah ya baki hakkuri indai akan zancen nan kike magana ko ni ba da son raina yai mashi fada ba.
Rufe min baki bakar munafuka sai kinyi annamincin ki kizo kinawa mutane wani marairaicewa.
Kin iya kitihin da zaki raba miji da matan shi da yaran shi .
To wallahi hawau kiji na fada maki kinyi kadan a gidan nan muddi kikace zaki shiga tsakanin diyana da uban su.
Ke har ina diyan naki dayake kirarin zasu rike mai gida bayan ran shi?
Ba dai wanan bakin mashayin dan naki ba da duniya tasan da zaman shi yana yawo cikin gari a wukance yara na kallon shi.
Masu abin fadi har ba iyaka saura wa yan nan muna fukan masu kirarin su kamilai ne a gida a waje ko tantiran yan iska.
Kuma kin sa Alhaji yaci zarafin imiran a gaban ki, kinji dadi to ki sani indai ni na haifi Imirah har abada ba zai gaishe ki ba bashi ba duk diyana a gidan nan.
Tsiyan banza duk wani a halina ma bazai taba yin mu,amula da kuba idan kuma kin insa sai ki sa Alhaji ya sa wuka yai ta yankan su don basu gaidake ba.
Haka zai sa nasan yaji zafin, basu gaida ke ba tun da ke dashi kuka daukan min nauyin cikin su na haife su.
Banzan bazara dake mai gayyan tsiya gida masu abin fadi tab ga tsuliya kawai.
Allah ya sauwa inji maji ta nufi dakin ta da kayan dake dauke a hannun ta.
Sadauki tagani tsaye a kofan ta ya dafa,