Showing 219001 words to 222000 words out of 373688 words

Chapter 74 - A LOKACIN MUKE BOOK BY ZAINAB .I. MAKAWA.txt

anty daga dawowan mutun baiko huta ba kina tambayan tsaraba.
To na hana ko zaki hana kuma ya bamu tsarabane yar gidan mugu.
Murmushi nayi nace ni a suwa?
Rufamin asiri na zauna da Fatima Bintu takafin kisa a canza min suna Binta munafuka.
Dariya tayi tace yanzun ko indai yayane baida wuya ajiku da dawowan shi nace yaushe kuma ai har ya fadi ko.
Murmushi mama tayi tace ni na,rasa wanan munafuncin da,sadauki ke kirawa ya ta.
Nace mama ni nasani barshi kawai inko don wanan ne ko gobe yayi shi sai nai mai munafunci.
Eyye wallahi maji wuyar yar ki yai kauri haka ashe yanzu yaya sadauki kik fada wa hakan ai kin fi kowa sanin halin shi dan kafan ki kawai ya taka amma kika ishi mutane da ihu,
Nace wallahi anty ban ma son na tuna don ba karamin wuya nasha ba a gidan nan.
Muna jin shi ya kara shigowa amma wanan karon ba dakin mu yazo ba cikin gida ya shiga gaida sauran iyayyen shi.
Duk da su diyan su basu zuwa gaida mama sai Sagir ne mai kokarin hakan cikin su don shi gaskiya daban yake a gidan sabodashi uztaszu ustazu ne haka.
Tare da Bashar suke ashe sai da suka shigo falon mu ne muka san da hakan,
Maryam da bata gan shi ba tafito da saurin ta gudu gudu tana fadin yaya sadauki ashe kana hanya bamu sani ba cikin murna da fatin cikin ta.
Ganin tare da Bashar suke yasa ta dan rage rawan kan da takeyi sai naga tawani noke cikin kunya ta dan boye bayan kujera tana fadin.
Yaya har fa wata biyu kayi da tafiya, gaskiya mu ka daina dadewa haka muna missing din ka sosai wallahi.
A hankali yace maryam nasan ai ba komai kikewa wanan tambayan ba sakon ki ne kuma ban sayo ba tunda ko murna baki min ba.
Tace wallahi yaya aiko nafi kowa murna tambayi maji kaji har party nai muna ranan ai nace ke dawa kukai party ?
Lalai ma Bintu sheri zaki kulla min don ki hanani samu wallahi na gane shiyasa yaya ke ce maki yar hana ruwa gudu.
To anty wai yau kuma lafiya naga kin wani boye bayan kujera kamar wata mara gaskiya kifito fili mana kowa ya gan ki .
Murmushi Bashar yayi nace sai cika bakin karya amma kina ganin yaya Bashar kin wani boye can bayan kujera to mun dai san komai mu dai ayi buki musha shagalin mu ko Anty Amirah?
Munafuka kawai wallahi yaya na yarda Bintu munafuka ce da gaske shegen saka idon tsiya gare ta kamar wata yar sandan ciki.
Wait, may naji wanan yarinyar na fadi ne wai kai mugu ashe ka zama dan akuya ne haka ban sani ba.
Dariya Bashar yai mashi yace akan may don ina son kaunata ko may kai wa ya hanaka fitar da naka sai wani kwanaye kwanaye kake wa kan ka abari ya huce dai shike kawo rabon wani.
Na kawo masi salad din sosai suka sha shi sai santi Bashar keyi yace kai mutumina kace min ka huta kawai.
Fuskan shi a daure yake bashi amsa a zazafe yana fadin wallahi zamu bata dakai idan kaja min matsala da raini Allah Bassh.
Wayan shi da aka kira ne ya katse masu challenges din junan su da,sukeyi.
Sai da ya ja dan tsuki yace ya akayi ne cikin daure fuska da mace yake wayan kuma tambayan shi take yau she zai dawo ne wai ?
Yace yau fa nazo gida shine kike tambayana yaushe zan dawo ko ganin mumm ban gama ba ki dai bari zan kiraki idan na fita.
Daga inda muke zaune sai naji wani dan abu kawai a raina ban dai san dalilin jin hakan ba.
Shiko yana kashe wayan yana dago kai inda nake zaune yana fadin ke zo kwashe kayan nan kada wanan mara kunyan ya cinye kwanonin gaba daya.
Fuska na yana a hade take ya fahinci ban cikin good mood a lokaci guda na koma haka to why ?
Sai muryan yaro ya ratso a kofan falon mu yana fadin wai Usman yana wa Fatima sallama a waje.
Maryam tace ga mr love lover din ki can ya iso nasan sun taso ke nan yazo ya damu mutane.
Na yunkura ina fadin babu ruwan ki anty ba dai ke yake damu ba ai, lah yanzu Bintu rashin kunyan naki har yakai haka a gaban su yaya zaki fice I love you ba kunya.
Sai ga mama tafito daga ciki tana fadin ke Fatima kin bar waya a daki sai faman ruri take ita kadai.
Na karbi wayan a hannun mama naga Usman ne nasan yakira ba,a dauka ba shine ya aiko yaron.
Hijjab din Amirah dake kusa na jawo na saka a jikina ina gyara wuyan hijjab din naji yace .
Ke bana ce ki kwashe kayan nan bane ina zaki haka kuma ?
Sai ga yaron ya dawo yace wai yace don Allah tazo yanzu yana sauri ne an kusa yin sallah.
Nace kace mai gani tafe yanzu don Allah.
Mikewa yayi kamar zasu fita shi bai fita daga kofan ba bai shigo ba ma,ana ya tare hanya ke nan ga Bashar daga waje tsaye yana jiran shi.
Na fito daga kitchen na gan shi a gurin tsaye a dan raunane nace zan wuce.
Tankar da dutse nake magana don ko motsi baiyi ba .
Ganin haka na dan jingina jikina gefe a bango ina kallon kafan shi dake cikin socks.
Waya na yai ruri na dauka nace gani tafe ai yanzu don Allah.
Bata hanya mana ta wuce ko kuma wani sallon muguntane haka kace kuma ga abinda tai maka yanzu.
A dan tsorace da jin muryan mama ya ja baya kadan nazo na wuce shi har hijjab dina yana gugan jikin shi.
Nan na fita na barsu na samu Usman zaune a motan shi ya saka kida na gaishe shi tare da tambayan shi yaya aiki?
Yai murmushi yace aiki Alhamdullahi daga can nake nace bari na biyo na gan ki kafin na isa gida don idan na shiga gida yau da wuya na fito kuma again.
Na dan dariya har hakora na suka fito nace anty na itama zata nada nata kambun ke nan ko?
Shima dariya yayi yace ai Nabila matsalace wallahi an samu wanda ya kai mata gulman ina neman ki, kuma tace min wai daga gidan nan aka fada mata.
Nace ai ko sai ka bari kada ku samu matsala da matar ka yace akan ta zan daina son abinda nake so sai dai ta san nayi.
Ban san sun fito ba sai da naji yace ikon Allah dama U F a gidan nan yake ne shine har na dan juya naga suna fitowa daga cikin gida.
Nace mai eh ai yayana ne a gurin maman shi nake zaune.
Kafin su karaso har ya fito daga motan shi naga ya nufe su yana dariya ya mika masu hannu.
Sai dai shi gogan barka kawai yace mai ya zagaya ya shiga mota hakan bai ma Usman dadi ba harni din ma dake tsaye ina kallon su.
Ban san gulman da yakaini daga ido na kalleshi ba sai ganin shi nayi ya sha mur fuskan shi tamau yai min alama da zaki fadi da ido kawai.
Ko da Usman ya dawo yake ce min ashe ko abinda ake fadi akan dan uwanki da gaske ne kuwa ?
Ance ba ruwan shimana amma ni sai naga ya wani basar dani ko don yagan ni da kaunar shine yakawo hakan.
Nace ai ba ruwan shi kila dai akwai abindaya bata mashi rai ne kawai yace Allah yasa ba don ni bane dai ?
Yana nan har gap da magariba mukai sallama ya wuce abin shi ni kuma na ahiga gida ina tunanen halin yan gidan mu har wa ya gane gidan su Usman yaje ya fada wa matar shi magana.
Suna barin gurin batare da ya kallo Bashar ba yace waye wanan guy din , Bashar ?
Wa wai wanda ke tare da Fatima yace shi mana a ina yake ne ?
Dan nan garin ne mana ni nasan shi da dadewa ina ganin kaman aikin banki yakeyi ne ai.
Sai dai guy din dan karyane tun dana san shi bai aje kan shi kusa ba akwai shi da karya sosai wallahi.
Zai iya kashe wa mace kudi sosai don ta so shi amma yana da aure don gaskiya na san na taba sanin yai aure a baya.
Tsuki yaja yace, wanan yarinyar ko ina take kwaso maza haka kamar ita kafai ce budur wa a gidan nan?
Dariya Bashar yayi yace kaida may kake nufi ne wai wanan tsaleliyar budurwa haka wa zai ganta ya barta ko don ma dai tana da kamun kai bata da rawan kai ai da yanzu kofan gidan ku ya cika da samari.
Da sauri yace wallahi da naci uban ta kuwa Allah.
Dariya sisai Bashar yake mashi yace oho dai indai mutum yace girman kaine ai gurin zurfin cikin tsiya sai asha mutum a banza.
Kafito fili kawai kabada kai bori ya hau ka tsaya kana wa mutane kwanaye kwanayen banza haka.
Wallahi Bassh kana son ja min raini Allah ni irin kane da zan bayar da kaina ga karamar yarinya haka nagane a gurin wanan yarinyar karamar yar kauye ban da tarin kauyanci.
Fatima ce yarinya U F ?
Ba yarinya bace tsohuwa ce ke nan ko ?
Sai ja tsuki tare da kawar da kan shi ga titi sai dai cikin zuciyar shi tunane yake yadda mazan yanzu basu jin kunyan hada halaka da yara kanana haka?
Wai to kai ban san yaya kake daukan kanka ba fa wanda ko 28 bai cika ba kana ta daukan kanka wani old man can.
A ganin ka ba ni kan ai nasan yanzu nakai yadda baka tsanmani don kagan ni ban girma ko ?
Dariya Bashar yai mashi yake ce mashi niko nafi kowa sanin yaya kake ai ka girmi duniya.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


DUK WACE TA TURA MIN NOVEL GA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YA SAKA MIN AKAN MAI SHI,,,,,



Fuskan ta a daure ta watso min harara tace shige ciki da wanan wasan banzan naku, simi simi nabi gefenta na shige cikin gida.
Binshi tayi da kallon mamaki shiko ko a jikin shi saima gyara hannun rigan shi yakeyi kawai.
Mama batai mashi magana ba sai kutawan da tayi ta shige ciki yace a fili i will dealing with you silly girl kawai.
Duk nabi na takura kaina sai jira nake mama tai min maganan amma shiru babu zancen haka yasa na sake gaba daya.
Rayuwa tana ci gaba yayin da takuran da sadauki ke min bai fasa ba don duk wani aikin shi nice zai saka komai wahalan aikin kuwa.
Zancen Maryam da Bashar har ya kawo gida yanzu don iyayyen shi sunzo gurin Baba.
Sadauki sai da ya dauki zafi sosai da Bashar har ya gaji ya sake don kan shi don Bashar din ya nuna mashi halin ko in kula ga yadda yake nuna mashi .
Halin zaman kishi na gidan su mama yana nan daram bai gushe ba don sai da suka samu mahaifiyan Bashar da cewa don may zata yarda ta hada zuria da wa yan nan mutane masu jinin tsiya fakirai masu gadon tsiya.
Inba yanzun ba da saudauki ya samu abakin may Hauwa,u take a gidan wace bata iya mayar da taro sisi zuciya ya mutu mata.
Amma dai yanzu ai Alhamdullahi ko don dama azziki ai gida biyu ne ko kai kayi ko danka yi ?
Mahaifiyar Bashar ce take tambayan su da hakan tace ai shi arzikin da yafi na iyayye dadi don zaka koma tankar basarake ne.
Baku jin ance bayan wuya sai dadi ba, dama cewa kukayi yarinyar bata da halin mutunci ne kila da sai na duba.
Amma Alhamdullahi, na zauna da yaran nasan halinsu don haka aure ne idan Allah yayi a tsakanin su nafi kowafarin cikin hada zuria da kamilan yara irin zurian maijidda a duniya.
Sai kuma suka fara cacan baki wai sun gane dama,kwadai ne kawai ya kai Bashar ga maryam don dan abinda yake samu ga,sadauki din.
Dama sun sani ai don haka ya raba shi da kowa nashi ya manne mashi kamar cingun.
Da,Bashar ya dawo ake fada mashi bai nuna bacin ranshi ba don yasan zasu iya hiya da hakan ma.
Amma yana barin gida direct kasuwa ya nufa gurin Baba ya fada mashi komai yace ai masu Umma iyaka dashi da uwanshi.
Ran Baba yai matukar baci sosai haka yasa shi dawowa gida a lokacin yai sa,a basu jima da dawowa daga gantalin su ba ke nan.
Ganin Baba gida ba lokacin dawowan shi ke nan ba yasa kowa mamakin ganin shi cikin wanan lokacin.
Gaba dayan su ya kirasu basuyi tsanmanin zancen bane sai da Baba ya tambaye su da cewa Atika ke da Asiya ina kuka tafi ne yau ?
Wana ta dubi waccan suka fara a tsakanin su sai umma ce yar gadara tace asibiti muka shi gaida Hanse yace abisa umurnin wa kuka tafi?
Yace bama wanan ba don na riga na barku ga Allah kan fitan da kuke yi bada izini na ba a gidan nan.
May ya kaiku gidan marigayi salisu mai engine ?
Da mamaki mama ta dago tana kallon su sai hjy kubura ce tace gidan Alhaji salisu mai engine ai gidan su Bashar din da zai auri mayam ke nan mana.
Yace eh can din?
Shiru sukayi sai Umma tace da muka je ance maka munyi wani abin ne acan.
Yace mai zaihana kuyi tunda shi ya kaiku yace da farko da Sani ya fada min kuka soke zancen auren sadauki da Rahama ban yarda ba sai yau din nan nayar da da hakan don kaidin ku ya wuce yadda nake tsamanin ku.
Na dauka duk wani "da da ya fito daga tsatsona kamar kuma dan kune a gidan nan kuma.
Ya girgiza kai yace ashe nayi kuskuren yin wanan tunanen a kanku don ku din nan ba abokan zaman alheri bane a gareni tun da har kuka, iya wanke kafan ku kuka tafi soke auren yar yaruwan ku.
Salati suka saka suna fadin yaushe akai haka su sheri a ka kulla masu kawai daga sun tafi, gaida mahaifiyan shi kawai.
Yace to yanzun dai Bashar ya samayni ya roke ni nai maku kashedi akan gidan su da uwarshi don haka duk wacce ta kara shiga harkan shi duk abinda yai mata ita tajawa kan ta tunda daini bada izzina na kuke fita ba gidan nan.
Abin bakin ciki da rashin sanin ciwon kai ace kun fi son yaran nan suyi ta zama a gida suna shashanci kamar yadda diyan ku sakeyi suna bata min suna a gari.
Abinda Nafisa keyi a garin nan waye zai aure ta a haka da ita watsatsa yau itace wancan party gobe itace gidan mashaya gata kuma gata wai a kungiyan yan madigo a gari.
Da sauri Umma tace kan yar ka yar gwal kada ka kulkawa diyata sheri don da baifi daba a duniya.
Yace sheri kan Atika aike kika kulawa kanki ke da baki kaunan dan wani da karuwa kina ganin Allah zaibar naki yadda kike so ne ke ?
Ran Umma ya baci kan bankada asirin Nafisa da ya yi a gaban kishiyoyin ta nan ta hau sababi tana borin kunya.
Yace magana daya ya rage gareku yanzu shine daga mazan har matan duk kowa ta fito da miji tai aure su bar min gida na hakana na huta da fitina haka.
Ya girgiza kai cikin takaici jin borin kunyan da Umma ke tayi wai bai kaunan ta ita da diyan ta agidan dabakin shi yake kulla masu Sheri don ya gyara zuciyar masoyan shi.
Shidai yafita bayan yai masu warning da gargadi mai karfi kan duk wace ta kara fita bada izinin shi ba har yaji sai tabar mashi gidan shi.
Maji ta dawo dakin ta cike da mamakin wanan irin bakin jinin da mutanen nan suke gwada mata haka.
Nan take fadawa yaran abinda su Umma sukajeyi gidan su Bashar daga inda nake nace ai sun kai karshen gulma indai gidan su Bashar ne Inna ce ko Bashar din ai suna daidai da su.
Waya mama ta dauka takira Inna na ta kwashe duk yadda akayi ta fada mata mama tace Allah ya kyauta nabar su ga Allah.
Buki za,ayi a family house din su Baba haka yasa yanzu su mama basu zama a gida sosai don suna zuwa can gidan gurin aikin bukin da za,ayi.
Shima yaya sadauki baya zama a gida sosai don ina ga,akwai wani aiki da yasha mashi gaban shi don sai dare yake dawowa gida.
Yauma da dare ya shigo har lokacin su mama basu dawo gidan ba suna can cikin gari.
Daganin shi a gajiye yake sai dai kuma alama ya nuna min yana cikin halin shi don ya dan sha a lokacin.
Maryam waya take da,wata kawarta Amira tana kallon wani season film a tv bayan an gaisa dashi kowa ya juya gur8n harkokin shi.
Ni dake


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login