Showing 177001 words to 180000 words out of 216282 words

Chapter 60 - KWANTAN BAUNA BOOK 2 COMPLETE BY Nanah Haleemah.doc

baya, shiyasa na tawo da duka iyalana dan su taya ni baka ha?uri da kuma neman yafiyar ka."
Asad yayi murmushi yace, "Dan Allah Hajiya a bar maganar nan ta riga ta wuce."
"A'a Asad bata wuce ba, an cutar dakai da yawa ko nace mun cutar dakai Asad. Nayi abubuwa a kan ganin bayan ka ni kaina ban san adadin su ba tun ba'a je ko ina ba na fara ganin sakayyar da Allah yayi maka akan Yahuza. Wallhi tun ranar da kazo duniya nake son ganin bayan ka Allah bai tab'a bani nasara ba. Ina had'a ka da kyawawan sunayen Allah kayi hak'uri ka yafe min abubuwan dukka da suka wuce" ta kalli y'ay'an ta tace, "Ku taya ni rok'on sa."

Babbar yayar su tace, "A madadin iyalan Hajiya muna neman afuwa abinda ya faru a baya ranka ya dad'e, abinda aka aikata wanda aka fad'a da wanda aka aikata ba a fad'a ba muna rok'on mai girma sarki da ya yafe mana mun yi alqwari in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba."

Asad yayi murmushi yace, "Dan Allah ku daina wannan maganar bana son ji, komai ya wuce ban rik'e kowa a raina ba." Hajiya tace, "Da gaske mai martaba sarkin mu ya yafe min?."
"Na yafe duk da daman ban rik'e ki ba Hajiya. Ina miki kallon mahaifiyata." Zata fara godiya yace, "Dan Allah kar kice komai, uwa kike a gare ni bazan jure ganin kina zubar da hawaye ba. Komai ya wuce dan Allah a daina kuka."

Ba musu ta goge idanun ta tana murmushi ya kalli y'an uwan nasa gabad'aya dukkan su fuskar su a sake yace, "Ina rok'on ku dukkan ku in akwai abinda ya faru a baya wanda ba'a ji dad'in saba a yafe. Sannan ina so duk inda akaga wani abu ba daidai ba a ciki da wajen masarautar nan ayi hanzarin sanar dani."

Dukkan su da farin ciki suka amsa kafin suyi sallama duk su tafi shi kuma ya tashi ya wuce saman sa Suhail yana bayan sa. A falon Suhail ya tsaya shima yana tsaye yace, "Ranka ya dad'e Hydar fa barazana ne ga rayuwar mai martaba bai kamata a sake dashi ba."

Asad ya sauke numfashi yace, "kar ka damu babu abinda zai faru."
"Haka muke fata, a kwana lafiya" ya fad'a yana juyawa ya sauka shi kuma ya wuce bedroom d'in sa. D'aki ya shiga sai ya tsaya a jikin mudubi yana kallon kansa kafin ya runtse idanun sa yana jin d'aci a zuciyar sa.

_ni kuma in ban zubar da cikin jikinta ba na amince ka kashe ni._ kalaman Hydar suka fad'o masa ya cire rawanin kansa ya kalli wayar sa ya d'auka da niyar kiran ta sai kuma ya ajjiye yaja k'aramin tsaki ta ko wanne b'angare haushin ta yake ji a zuciyar sa shiyasa yayi banza da ita bai sake waiwayon ta ba har yau. _Yana dakyau ka neme ta kodan abinda Hydar yace._ Zuciyar sa ta fad'a masa ya runtse idanun sa a bayyane yace, "In sha Allah babu abinda zai faru da ita, ina tare da ita a ko yaushe."

Fuskar Mama ta fad'o masa sai ya d'auki wayar sa ya kira Suhaima tana d'auka yace, "Mama."
Suhaima tace, "Har yanzu bacci take." Datse kiran yayi ya kama k'ugun sa sosai kansa yake masa ciwo har jiri yake ji yana d'aukar sa. "Hasbunallahu wani'imal wakil" ya furta a bayyane yana zama a gefen gadon ya dafe kansa lokacin da Jidda ta saka a kashe shi har ya kamata tana waya ya fad'o masa.

Saurin kawar da tunanin yayi ya tashi ya shiga wanka. Wankan ma da ruwan magani ya yishi bayan ya fito ya shafa mai da magani ya fesa turare mai magani ya saka kaya wanda aka turara su da magani. Hannun sa ya d'ora a cikin sa baya jin yunwa ko kad'an gashi shidan yasan tun daren jiya bai sake cin komai ba.

_Wallahi na tsane ka bana qaunar ganin mazinaci._ kalaman Rauda suka fad'o masa abinda yaji a zuciyar sa sai da ya datse labban sa da hakorin sa ya runtse ido yana sauke numfashi zuciyar sa na rawa. Bai san adadin lokacin da ya d'auka a haka ba sai da dare yayi sosai ya sauko kai tsaye b'angaren mai martaba ya shiga.

Kamar yadda yayi tunani yana zaune akan sallaya ganin hakan sai ya koma ya shiga d'akin da Aliyu yake kwance. A zaune ya same shi shima a kan gado idanun sa a waje ya yaga rigar jikin sa yayi tagumi ya zubawa waje d'aya ido kamar mai kallon wani abun.

Ganin Asad ya shigo ya saka Aliyu zabura yana kallon sa har ya k'araso inda yake ya zauna ya dafa kafad'arsa yace, "Allah ya baka lafiya Aliyu." Kai Aliyu ya fara girgizawa yana fad'in,? "Ba sunana Aliyu ba sunana Asad, ni sarki ne ina hawa doki ana zagawa dani, ina zuwa na bawa yara y'an islamiyya allo a lokacin bikin sauka. Ka daina cemin Aliyu zan iyawa yin komai akan hakan."

Asad ya runtse idanun sa ya buWe yana kallon Aliyu cikin tausayin halin da yake ciki ya zuba masa ido kawai baiyi magana ba. K'arar buWe k'ofa yaji hakan ya saka shi ya juya ganin mahaifinsa sai ya mik'e tsaye har ya k'arasa ya dafa kafaWarsa sa yace, "me ya fito da kai a daren nan?." Asad ya nuna Aliyu yace, "hankalina yak'i kwanciya."

Mai martaba ya kalli Aliyu yace, "zai samu lafiya da iznin Allah shiyasa na zab'i a barshi a nan yana karb'ar magani." Asad ya girgiza kansa yace, "Abba jikin Mama ma babu dad'i." Numfashi ya sauke yace, "dole ta samu gigita da rud'ani a wannan yanayin da ake ciki amma itama zata samu lafiya."

Mai martaba ya kalle shi yace, "Zuciyar ka a wanke take Asad kyakykyawar zuciyar da kake da ita Allah bazai bawa kowa damar cutar da kai ba." Asad yyi shiru ya sunkuyar da kansa mai martaba yace, "Ka koma kaje ka huta gobe akwai zaman da zaka gabatar domin gyara mulkin ka. Bana son a sake samun matsala a wancan karon ma kaine ka bada dama ka dinga karb'ar duk abinda babar ka tazo dashi. A wannan karon bazai faru ba." Kai ya girgiza kai kafin yayi masa sallama ya wuce ya koma yana ji kamar ana tura shi in yana tafiya sabida jiri.

*&&&*

? ? ?? "Duk abinda kuka aikata yazo kunnena Sadiya, duk yadda kuke da Rabi'a ta d'auki aminci ta baki tun kuna makarantar secondary a Kano kuke tare amma ki rasa abinda zaki saka mata sai da cuta, cutar ma kuma wai kisa Sadiya? Yaushe kika zama y'ar ta'adda ban sani ba?" Daddy ya fad'a da alamun bacin rai a tare dashi yana kallon Mum.

Mum tana kuka sosai tace, "Ambassador ka tsaya nayi maka bayanin abinda ya faru, banyi hakan da....." dakatar da ita yayi ta hanyar fad'in, "Rufe min baki domin baki da wani kalami da zaki fad'a min na amince. Sabida tsabar son zuciyar ki aminiyar ki kike k'ok'arin kashewa bayan kin rabata da d'an da ta haifa sabida wani banza burin ki na iska. Kin d'ora y'arki a tafarkin zina da aure a kanta take zmaan fasiqanci da Yayan mijinta kuma duk kina sane kikayi shiru sabida cikar burin ki."

Mum tace, "Wallahi ban san ba Asad bane, bata fad'a min ba, ban san zaman fasiqanci sukeyi da Aliyu ba ka yarda dani."
"Babu abinda zaki fad'a na yarda dashi, kin cutar dani kin kuma cutar da kanki da rayuwar yarki. Baxan lamunta ba wallahi bazan iya cigaba da zama da mata irin ki ba, daga asibitin nan kar ki sake ki koma min gidana kije can ku k'arata dake da y'ar taki da kuma d'an shegen da ta haifar miki da aure a kanta, wannan bak'in zunubin bazai zauna a gidana ba domin wata rana kar fushin Allah ya shafe ni."

Hankalin Mum ya sake tashi ta zube a k'asa tace, "Kar kayi min haka Daddy wallahi duk abinda ya faru bada son raina ba ka tsaya nayi maka bayani."
"Ni na tsaya na saurare ki? Har abada bazan tsaya ba domin ban san me kika k'unso kike so ki kashe ba nima dan tunda kikayi yun?urin kashe Rabi baki duba alaqar ku babu wanda zaki bari a duniya. Ga takardar sakin y'arki nan an bani sai kije da ita ku k'arata ko babu komai tahiri ya kafu a kanta wanda baza'a manta dashi ba a duniya. Mace ta farko da tayi zina da yayan mijinta y'ar kice, mace ta farko da taso kashe mijin ta sabida karta rabu da yayan mijin nata y'ar kice, mace ta farko da sarki guda shugaban al'amma ya fara sakin ta. Kar ki sake ki dawo min gida bazan iya zama da dake da kuma y'arki ba" ya fad'a yana cilla mata takardar hannun sa.

Har ya juya zai tafi yaga Eman na kuka sosai ya damk'o hannunta yace, "muje kar kema ta lalata min ke da bak'ar zuciyar ta!" Ya fad'a yana jan Hannun Eman suka bar wajan tana kuka sosai Mum tana kuka.

#FitattuBiyar
#Nanahaleema
[17/12, 10:45 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*085.*

? ? ?? Zubewa Mama tayi a k'asa tana kuka sosai mai tsuma zuciya Mai cike da tarin dana sani da nadamar duk abinda ta aikata domin gashi ya k'are a kanta da y'arta.
"Mum!." Da sauri Mum ta juya tana kallon Jidda jin muryar ta ta fita tana kallon ta itama ita take kallo.

Shafa cikin ta tayi ta sake kallon Mum tace, "Mum ina cikina?." Mum ta mik'e ta taso tazo kusa da ita ba tare da tunanin komai ba ta chakumi wuyan Jidda tana girgiza ta kafin ta cire hannu ta tsika mata mari tana fad'in, "Jidda kin cuce ni kin gama dani. Me na aikata miki kika zab'i kiyi min wannan hukuncin? Me nayi miki kike k'okarin saka zuciyata ta buga eh Jidda?."

Jidda ta sake fashewa da sabon kuka duk da ciwon da yake tare da ita tace, "Mum ba laifina bane laifin kine Mum, kece kika d'ora ni akan hanyar aikata duk abinda na aikata. Bana son barin gidan sarauta bana son a daina kirana matar sarki shiyasa na amince da Aliyu tun farkon kaini gidan matsayin matar Asad ba. Ban san wannan ranar zata zo ba da na kashe kaina kafin zuwan ta."

"Ko baki kashe kanki ba ni zan kashe ki Jidda. Na tsane ki wallahi bana son ganin ki dan kin aikata zunubin da ban tab'a ganin wanda ya aikata shi ido da ido ba sai kee!." Jidda ta tashi zaune dak'yar tana cize baki tace, "Da nace a kashe Aliyu da an kashe shi duk wannan bata zo ba, a lokacin in nace miki a kashe Aliyu Asad nake nufi domin munyi agreement da Aliyu akan bazan sake kiran sunan sa Aliyu ba sai dai Asad shi kuma Asad nace masa Aliyu. Mum duk laifin kine da baki d'ora ni akan cuta ba da yanzu ina tare da mijina Asad, ke kika koya min son kai, ke kika koya min kisa, ke kika koya min dukkan abinda na aikata a wajan ki na iya...." a haukace Mum tayo kanta ta fara dukan ta ta ko ina.

Nurses ne suka shigo a guje aka kwace Mum amma tuni Jidda ta suma itama Mum d'in baya tayi ya zube a k'asa suka d'auke ta aka shiga bata nata taimakon haka Jiddan ba.

*&&&*

Washe gari ta kama ranar litinin an gabatar da zaman fada mai aji wanda Asad ya gabatar da zafafan hukuncin da ya yanke wanda zai sake farfad'o da martabar masarautar sa. Duk wani abu da ake yi ba daidai ba an dakatar dashi an sake d'ora masarautar akan tafarkin addinin musulunci da kuma kyawawan ayyuka masu kyau da tsari.

Ranar kowa sai da Asad ya burge shi domin yadda yake maganar ma abin burgewa ne balle kuma hukuncin da ya yanke akan komai ya tsara komai yadda ya kamata.

Bayan an tashi daga zaman fada asibitin da Mama take kwance ya wuce ana tafiya ana jiniya mota hud'u a gaba sannan wacce yake ciki sai hud'u a baya ana gudu akan titi.
Duk a k'ofar d'akin suka tsayaa shida Suhail ne kawai suka shiga ciki tunda ya hango Maman sai kuma gaban sa ya fad'i ganin ta dai tana nan yarda ya barta jiya.

Suhaima ya kalla yaga ta rame lokaci d'aya tayi duhu idanunta ya fad'a ya kalle ta yace, "Suhaima meyasa bakya jin magana?." Ta rausayar dakai dan ta gaji da yin kuka tace, "na kasa bacci ne." Ya furzar da iska a bakin sa yace, "Mama bata farka ba?." Kai ta d'aga alamun eh ya girgiza kansa ya kalli Suhail kamar yasan me yake nufi sai ya tashi ya fita jim kad'an sai gashi da Dr sun shigo.

Dr Yasir ne ya gyara tsayuwa yace, "Barka da zuwa ranka ya Dade." Asad bai amsa ba yace, "ya jikin Mama?." Ya sake saukar da murya cikin girmamawa yace, "Ranka ya dad'e jinin Mama ne ya hau sosai, sannan zuciyar Mama tana bugawa da sauri har muna expecting heart attack ya kama Mama but bamu yi confirming ba. Akwai firgici sosai a tare da Mama dalilin da ya saka har yanzu jinin ta baiyi daidai ba har yanzu zuciyar Mama a firgice take."

Asad ya sauke numfashi ya kalle shi sannan ya kalli Suhaima Dr ma ya kalli Suhaima yace, "Allah ya k'ara maka lafiya itama Suhaima akwai firgici a tare da ita shine ya haifar mata da zazzaSi amma tak'i zama ayi mata treatment." Asad ya kalle ta ya kalli Dr din sai ya kalli Suhail gnin kallon sai yace, "Ayi mata yanzu Dr duk abinda ya kamata ayi. Sannan zuwa yaushe Mama zata farka?."

Dr yace, "in sha Allah zuwa gobe zata farfad'o, muna so bp d'in nata ne yayi k'asa kafin allurar ta sake ta." Suhail yace, "Ayi duk abinda ya kamata Dr."
"In sha Allah ranka ya dad'e." Asad addu'a ya yiwa Mama sosai kafin a kawo gado a kwantar da Suhaima a kai a saka mata ruwa a gaban sa bacci ya d'auke ta.

Security aka k'aro mace mai uniform aka ajjiye ta da kula da Mama aka saka maza biyu a bakin k'ofa ya bada umarnin ko waye yazo kar a barshi ya shigo suka amsa da girmamawa sannan suka fito suka koma gida.

*&&&*

? ? ?? Yadda waziri yake kuka sai ka d'auka k'aramin yaro ne har majina ce take zuba daga hancin sa matar sa na tsaye a kansa itama cikin kuka da tashin hankali tana fad'in, "Na rantse da Allah sai ka fad'a min matsafan da ka bawa y'ay'ana suka tsafe akan son mulkin ka na banza da wofi. Wallahi bazan bar maganar nan ba zan kaita gaba wajan human right domin su kwatar min hakkina."

Kuka sosai yake yi zuciyar sa tana bugawa yayi tari yana dukan k'irjin sa kana ya d'ago jajayen idanun sa ya kalle ta muryar sa har rawa take yace, "Yanzu ni kike kalla kike sanar dani na kai y'ay'ana anyi tsafi dasu?." Ta kalle shi tace, "Na fad'a, ai nasan zaka iya ne akan son mulkin ka babu abinda baza ka iya aikatawa ba. Ko ka saka a dawo min da y'ay'ana ko na kai ka k'ara" ta fad'a tana fashewa da sabon kuka ta zube a wajan.

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, kaicona ni Yahuza kaico da masu hali irin nawa na son duniya da k'ok'arin ganin bayan wani.? Yanzu me gari ya waya a gare ni? Na rasa y'ay'ana har guda biyu akan abinda ba addini ba" ya fad'a yana kulle fuskar sa yana kuka mai tsuma zuciya.

"Ban amince da wannan jawabin naka ba, wallahi Allah sai an karbar min hakkina sai an saka min abinda akayi min nida y'ay'ana, bazan amince ba wallahil azim sai bazan bar maganar nan ba kaji na rantse, jira nake a share makoki in kai maganar gaban hukuma" tana fad'a ta tashi ta fita bai iya kallon ta ba ya cigaba da kuka sosai.

Bai daina kuka ba dan kukan daga zuciyar sa yake zuwa shiyasa hawayen idanun sa suka ki tsayawa kuka yake sosai kana kallon sa kasan yana cikin rad'ad'in zuciya da tashin hankali. Ya jima a haka kansa yana sarawa yana yi masa ciwo ya kwanta yana kallon sama.

"Assalamu alaikum, ranka ya dad'e anyi baki daga Kano" wani dogari ya fad'a daga bakin k'ofa. Bai iya d'agowa ya kalle shi ba da hannu yayi masa alama da yaje ya juya ya tafi ya jima kafin ya tashi ya shiga band'aki ya wanke fuskar sa ya fito. Sai da yazo gab da mutanen da suka zo masa gaisuwa jiri sai ya kwashe shi nan take ya zube a wajan a sume.

*&&&*

? ? ? ? ? Falo na musamman suke a zaune Asad ya kalli mahaifin sa murya a sanyaye yace, "Abba ina neman alfarma." Mai martaba ya ajjiye abinda yake hannun sa ya kalle shi yace, "Ina jinka."
"Ranka ya dad'e alfarma nake nema a madadin Mama, ina rok'on mahaifina da ya yafe mata kuskuren da ta aikata a baya, tana jin jiki yanzu daga can nake har yanzu bata san a inda take ba."

Mai martaba yayi murmushi yace, "Asad babu kai a cikin maganar dake tsakanina da mahaifiyar ka, ina so tayi nadamar dukkan abinda ta aikata da wanda take son aikatawar wannan abun ya faru. Ina so tayi nadamar abubuwa da yawa ta wanke zuciyar ta dukka halayen ta marasa kyau ta ajjiye su a gefe."

Asad yayi shiru har Abba yakai k'arshe kafin yace, "A duba dai Abba."
"Ai kad'an ta fara gani Asad abinda ta aikata ko hakkin matar ka Rauda bazai barta ba balle hakkin sauran mutane. Ni sai ka tuna min ma batun matar taka jibi juma'a za'ayi bikin dawowar ta gidan na shugaba guda bazai yu ya zauna a gidan nan babu mata ba."

Asad yayi shiru baice komai ba Mai martaba yace, "Munyi magana da mahaifinta d'azu sun san da batun dawowar ta jibin an gama gyara b'angaren da zata zauna komai an tanadar mata ita akwai ake jira ta dawo dan cikar martabar ka." Asad ya girgiza kai alamun gamsuwa kafin yace, "Allah ya taimake ka ba'a ce komai akan Maman ba."

Yayi y'ar dariya yace, "wato hankalin ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login