Showing 27001 words to 30000 words out of 259198 words
Chapter 10 - Rudin Kuruciya Book Complete Original By Ayshercool.txt
order na 10k ɗin nan kuyi ankon su"
Shewa suka ɗauka a gurin, Taslim tace "omo What do you mean? Mu ɗin kuma fa"
Sadik yace "in dai zaku sa se ayi order da ku"
Meena tace "mw ze hana? A siya damu"
"Shikenan duk wanda ze je partyn, a saka order da shi, zan sa a bugo riguna polo, amma kowa siyan riga ze dan ubanku"
Dariya su kai, Nas yace "nasan iya wuya ba tafi 5k ba, na saiwa mata goma riguna, amma fa se zafafa wanda suka cika mata, wadda idan ta saka kayan nan za'a ga kaya"
Taslim ta buga wani uban ihu tace "yeee ina cikin wanda za'a saiwa riga ko ba'a so, dan na kai mace wallahi"
Nas yace "ba ƙarya muma mun seda ai"
Shewarsu suka cigaba da yi, suna ihu, suna cigaba da tsara rashin jin da za suyi a gurin party.
Knocking ɗin ƙofar ajin akayi, Sannan aka shigo.
Director ne ya shigo, shida wasu 'yan bautar ƙasa, maza uku mata biyu, sedai matan kiristoci ne, dan kansu ya sha ƙarin gashi.
Tsit sukayi suka gayara zamansu, Director yace "my dearest And beloved student, can't you greet?"
Seda yai Maganar, sannan suka gaishe su gaba ɗaya.
Nan ya gabatar musu da 'yan bautar ƙasar nan, a matsayin sababbin malamai.
Nan suka gabatar da kansu ɗaya bayan ɗaya ga 'yan ajin, bayan sun gama gabatar da kan nasu ne, Director da kansa ya dinga gabatar musu da ɗaliban da kansa, kowanne ya gabatar da shi da matsayin mahaifinsa.
Seda suka kammala yai musu jawabin da ze musu, akan su bawa malaman haɗin kai, dan samun ilimin da ya dace.
Meena ce cikin harshen turanci da iyayi, ta wakilci 'yan ajin ta yi musu barka da zuwa, da tabattar musu da za su basu Dukkan haɗin kan da suke buƙata, dan gudanar da aikinsu.
Wani fari daga cikinsu wanda ya gabatar da kansa a matsayin Nura daga Kogi state, shima cikin harshen turanci ya wakilci 'yan uwansa, yai musu godiya da irin karɓar da a kai musu.
Daga nan kuma suka bi Director suka fita suka nufi wani ajin.
Suna fita Meena tai murmushi tace "Subhanallah"
Taslim tace "ke lafiyarki kuwa?"
Meena tai murmushi tace "Taslim kinga abunda na gani kuwa?"
"Me kika gani?"
"Wallahi I fall for that guy"
"Wane guy kuma?"
Taslim tai maganar tana kallon Meena.
"That fair and tall Man, Nura looking very beautiful and energetic, wallahi yai min"
"Ke bana son iskancin banza fa"
"Ke wallahi ba ƙarya nake ba, before nafi ganin kyan corper Nazir, Amma yanzu naga abunda zuciyata ke so wallahi"
Taslim tace "Nifa daɗina da ke 'yar bala'i ce ke, ki rage leƙe leƙe wallahi"
"Ba wani leƙe leƙe ƙyaleni kawai"
Nasir kuwa cigaba da batun bikin yayan Sadik sukayi.
Yau Farhan ba ta zo gurin sa ba, dan haka da kansa ya kuma tafiya nemanta, sedai ya tarar ta kifa kanta akan benci, kamar me bacci.
Ƙarasawa yai a hankali, ya ɗagota da ga kwanciyar da tayi.
Hakan ya firgita ta sosai, ta shiga rarraba ido amma ba tace komai ba, yace "Am sorry na miki laifi, na firgita ki gashi na taɓa ki ko?"
Ba ta masa ba, ya samu guri ya zauna daf da ita yace "Honey meke damunki ne? Naga idonki yai ja"
Ji tai kamar Sadik ya taɓo mata inda yake mata ƙaiƙayi, tana da damuwa But she has no one to discuss with, she's developing some changes in her breast, suna mata zafi wasu lokutan, sedai ta kasa ganewa, is it the normal stage of puberty, ko kuma wata matsala ce daban, dan tana jin ana wayar da kai akan breast cancer, dan recently anyi taro a makarantar, na wayarwa da mata kai, akan ciwon sanƙaran mama, amma ita ta kasa gane a wani hali take? Gashi ba yadda za'ai taiwa Ummanta zancen, gashi ba wanda za ta iya gayawa damuwarta, a yanzu haka duk da ta na kwana guri ɗaya da Ummanta ta tashi, amma Babu wanda take da kusanci da shi a yanzu kamar Sadik, sedai shima ɗin Maganar tayi matuƙar nauyin da ba zata iya tambayarsa ba.
"Lafiya naga kin yi shiru kina kallona? What's wrong ki gayamin please"
Ajiyar zuciya tayi, cikin sassanyar muryarta tace "bakomai fa"
Ya kwaikwayeta yace "ban yadda ba gaskiya"
Hakan ya bata dariya da seda tai murmushi, yace "oya gayamin ina jinki"
"Dagaske nake bakomai, bacci nake ji ne"
'ba kya bacci sosai ne a gida?"
"Eh ina yin karatu da daddare"
"Wow that's very good ai, amma ki dinga rangwantawa kanki kinji Hubby na, bikin yaya na ya kusa, za'ayi events da aka shirya a gidan mu, amma akwai party da zan organising, so akwai kalar outpit ɗin da za'a saka, ayi order dake zaki saka?"
"A'a baza'a barni ba a gidanmu"
"Ok ba damuwa, nasan dama ba lallai a barki b, but I just decided to tell you ne, amma dai ko sau ɗaya zaki zo ko?"
"Eh Insha Allah"
"Yawwa my wife"
Sunkuyar da kai tayi ƙasa, dama yasan hakan ne ze faru, dan wannan kalaman nasa nauyi suke mata.
"Farhan" ya kira sunan ta.
"Na'am" ta amsa.
"Next week zan karɓo exams card ɗina, na kusa Barin makarantar nan Insha Allah"
Ai da sauri ta ɗago ta kalli Sadik tace "dan Allah dagaske ka ke?"
"Am serious, zanyi Waec ne in kammala karatuna akan lokaci"
Take jikin Farhan yai wani irin sanyi, ta kasa cewa uffan se dai damuwa ta bayyana ƙarara ta mamaye fuskarta.
"Farhan" ya kira sunanta.
A sanyaye ta kalle shi, yace "kin san meyasa nai haka? Duk cikin planing ɗina ne na in mallake ki, dan Allah Farhan kar ki kalli hakan da wata fuska daban, i really love you wlh, duk saboda nake wannan fighting ɗin, kimin addu'a samun nasara, bari in tafi aji kar Wannan jarababben mutumin yazo yai min masifa"
Ya tashi ya kalleta yace "I love You baby" ya kashe mata ido ɗaya ya juya ya fita.
Ai yana fita ta bawa hawayen da take ta kokawa da su damar zubowa, ta kifa kanta kawai ta fara kuka ƙasa ƙasa.
"Yanzu idan Prince ya dena zuwa Makarantar nan ya za tayi, a duk ranar da ba ta ganshi ba, tana shiga mummunar damuwa, se gashi ze bar makarantar gaba ɗaya, nan hawaye suka cigaba da zarya a kuncinta, ta sa hanky tana gogewa, tun a lokacin taji ta fara kewar masoyin nata, take ta manta da damuwar ta ta farko dake damunta.
Shi kansa Sadik tunda ya gaya mata yaga damuwa a fuskarsa, ya shiga damuwa shima, take yaji wani irin tausayinta ya kamashi sosai, shikansa ya san zeyi missing ɗinta, sedai barinsa makarantar ba yana nufin ya bar Farhan ba, akwai yiwuwar ya fara neman Hanyar cinma burinsa, na aurar wadda yake so a Wannan shekarun.
"Idan ka aureta Yanzu tata rayuwar fa? Karatun ta fa?" Wata zuciyar ta tambayeshi.
'ta ƙarasa a gidana' ya bawa kansa amsa.
Da gudu ta sheƙo ta kan varrender, tana ƙoƙarin ƙarasawa ajinsu "Lilly! Lilly" tsayawa Lilly tayi tana kallon Sir Nazir dake ta ƙwala mata kira kamar mafarauci.
"Why are you running like this? Where is your jacket?"
Ta kalli jikinta daga ita se inner shirt, da skirt ɗin ta iya gwiwa, ta cire jacket ɗin ta ajiye a aji, ta kalleshi tace "tana aji"
"Meyasa kike yawo a haka? Baki san kin fara girma ba, kuma kina gudu a cikin yara haka? Ga hijjabin ki ƙarami, Why are you exhibiting childish behavior, don't you know you are at your Adolescents period, you have to maintain your body?"
A ranta tace "ji ɗan iska, seka gayamin a Adolescents period nake, ai nima na sani"
Ta tura baki cike da sangarta.
Yace "idan na kuma ganin kin kuma cire jacket ɗinki kina gudu haka, sena zane ki, wuce ki ban guri"
Tafiya tayi tana yatsuna fuska.
Tana zuwa Ajinsu tace "hmm ƙawayen amana kun san abunda ya faru kuwa?"
Haseena tace "ya za'ai mu sani se kin faɗa"
Lilly tace "mhmm wannan sir Nazir ɗin ne na taho da gudu ya wani tsaida ni, wai meyasa nake yawo ba jacket nake gudu, wai ban san na fara girma bane na shiga Adolescents period, kuji min ɗan air mutum"
Shewa suka yi Haseena tace "Ya ƙyasa ne yaseen, shine ya gaza shiruu seda ya tanka, ya tsaida ke ne kawai dan kawai ya sake kalla sosai"
Ihu suka saka gaba ɗaya, tai wani juya tai girgiza tace "gani ba taɓawa ba asarar ido, nan gani nam bari ɗumamen mayya, kuma wallahi yawo ba jacket yanzu na fara, ke ni fa na kusa dena saka wannan ɗan hijjabin ma, haka zan dinga yawo, mutum ya kalla ko kuma ya runtse idonsa"
Yasmin tace "to Allah ya temake ka abubuwa sun fara fitowa ace ba zakai gayu da abunka ba, wani abun ma se munje Final year lokacin sun gama fitowa, lokacin ne zega yadda ake abu, yadda zamu addabi makarantar nan, ai ya gani ya kasa shiru shine ya tanka miki, sun tsole masa ido"
Lilly tace "aikuwa in hakane ya shiga tara mutumin nan, dan sena ganshi ma zan dinga kasawa da gud"
Yasmin tace "ai base kinyi gudu ba, kya yiwa kan ki ɓarna ai, kina tafe kina ɗan bada style ma ya isa, ban gaya muku ba ma, na fa samo mana littafin nan, ku kunji abubuwa a ciki kuwa"
Haseena tace "dan Allah dagaske ko da wasa?"
"Wallahi dagaske nake, ke kunga yadda aka fayyace komai ban dai karanta ba, page ɗaya kawai na karanta, amma naji sena zo da wayata mu karanta tare, kai akwai tafasassun abubuwa a littafin nan"
Lilly tace "shegiyar kaya, ai a kawo mana littafin nan, muji abubuwa kawai"
Su kaita shewa, ita kam sam Farhan hankalinta baya kansu, hankalinta kacokan yana kan maganar da sukayi da Prince ɗinta.
Shikansa Prince har aka tashi jikinsa a sanyaye yake, yaje ƙofar makarantar ya tsaya yana jiran fitowar Farhan.
Aikuwa ya hangota ta fito daga cikin makarantar, idanunta sunyi jawur sosai, tana tafiya a hankali, daga inda yake tsaye yake kallonta, kullum ƙara girma take tana kyau abunta, sheɗan ne ya fara ƙawata masa ita, da ɗarsuwar wani abu daban a ransa, take yace "Subhanallah" ya dawo hayyacinsa.
Tana ɗaga ido sukai ido huɗu da shi, murmushin dole tai masa, yace "ke muke jira taho mu tafi gida"
"A'a zan tafi ai"
"Bana son gaddama fa"
Ba yadda ta iya haka ta bishi ta shiga motar, suna tafiya yace "Anya ba kuka ki kai ba, naga idonki ya ƙara ja"
"Ba kuka nai ba, dama ina ciwon ido wani lokacin"
"Ciwon ido, lallai ma ashe makauniya ce matar tawa, gaskiya sena rage sadakin da zan bayar" yai maganar yana murmushi.
Direba ko a ransa yace 'ikon Allah, ji wani kwaɗo da fitsara wai ita game saurayi ta shiga motarsa yana mata kalaman banza na RUƊIN ƘURUCIYA, banda haka ina Sadik ina wata budurwa dan kawai yana ganin ya na da tsawon ƙafa!?"
Seda suka kai Farhan gida sannan suka wuce gida, babban abunda yaiwa Sadii daɗi be wuce yadda yau gidansu ba mutane ba, hakan yai masa daɗi sosai.
A ƙofar shiga BQ ɗin su ya haɗu da Dr. Ya kalleshi yace "Sadii yau kamar ba ka dawo da wuri ba, ina ka tsaya ne?"
Sadik yace "mun sauke Farhan a gida ne, sannan muka taho?"
"Wace kuma Farhan?"
"My wife to be insha Allah" Sadik ya faɗa kansa tsaye.
Usman yace "kasan me kace kuwa?"
"Eh mana na sani, budurwata ce da nake burin Aure, kuma insha Allah daga bikinka se nawa"
Usman ya jinjina kai yace "ba laifin ka bane, tashen balaga ne da RUƊIN ƘURUCIYA, ke ɗibar ka"
Sadik yace "tashen balaga kuma? Oho koma dai menene, I mean what I say wallahi"
Yana gama maganar ya wuce Usman, ya shige.
Usman ya bishi da kallo, kawai ya girgiza kai, ya juya ya nufi in da motocin gidan suke.
Sadik yai wanka yai salla, ya tafi ganin Mummynsa, sedai yana zuwa ya tarar ba ta nan wai ta fita.
Haushi ne ya kama shi ya shiga Kitchen, ya tarar Khairat na dafa indomie, tana yi tana bin wata waƙa da ke tashi a wayarta.
"Ss ke 'yar bainu" yai maganar da sigar tsokana.
Waiwayowa tai ta kalli Sadik, tace "ka ga karka kuma cemin 'yar bainu"
Yai murmushin yace "ke dallacan uwar fushi, ina Mother ta tafi ne?"
"Nima ban sani ba, da Mummy ta ɗakkoni daga makaranta tazo ta ajiyeni suka fita tare"
"To dafa indomie da ni, tunda Mother ba ta nan"
"Baza'a dafa ɗin ba, 'yar bainu ta dafa maka"
Dariya yayi yace "ke akwai zazzafan party da bikin dr. Fa, zamu shirya na 'yan school ɗin mu, kema za'a baki Card in da wanda zaki gayyata"
Tsalle tai tace "wow, dole muje ai, kai za'a cashe fa Prince"
"Ke dalla can, har wata rawa kika iya?"
"Taɓ kaji ka, wace kalar rawa ce ban iya ba? Wallahi na iya rawa"
Sadik yace "To yi mu gani, kuma in baki iya ba ba inda zaki"
Yai maganar yana ciro wayar a aljihunsa, ya duba wayar ya saka mata waƙa, take Khairat ta fara rawa tana juyi, tana karairaya jikinta.
Tafi ya fara yi mata yace "ba ƙarya kin iya, zaki je gurin partyn nan, let me join you"
Nam suka shiga rawa shida Khairat a Kitchen, ya riƙe hannun Khairat yaana juaya ta suna rawa tare, kamar yaran turawa.
"Lalalala! Innalillahi taɓɗijan, dama abunda kuke yi kenan? To wallahi sena gayawa Inna kuna abunda be dace ba, kuna taɓa juna bayan tace ba kyau.
Ayshercool
07063065680.
[6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
RUƊIN ƘURUCIYA
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Writer of
WATA KISSAR..(Sai mata)
ABDUL JALAL
AƘIDATA (paid book)
WUTA A MASAƘA
NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book)
_Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_
⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️
13-14
A tare Khairat da Sadik suka juyo suna kallon Nana, dake tsaye tana musu kallon banza.
Khairat tace "is this girl serious?"
Sadik yace "A beg forget about her, she's mentally abnormal"
"Nima na gani"
Cikin tsiwa Nana tace "Wallahi Inna ta hana, tace babu kyau, kwata kwata babu kyau irin wannan abun, amma kai kuma kazo kana taɓata, tace marasa tarbiyya ne suke haka, kuma Allah ze fushi da mutum, Allah ya hana amma ka ke aikatawa, wallahi se na gaya mata"
"Dan ubanki tsayuwar me kike a gurin baki tafi gayamatan ba? Kifi ruwa gudu banza da baki kamar mazirari"
"Kaine banza bani ba wallahi"
Ta juya ta tafi ɗakinsu da sauri dan ta sanar da Inna.
"Innarmu, Inna" ta shiga ƙwalawa Innan kira.
Inna tace "Ya akayi meye kike kirana haka?"
Se kuma Nana tayi saroro ta kasa Magana, kawai ta basar tace "kawai nemanki nake"
"Dan kina nemana seki biyoni da wannan kiran Kamar wata sa'arki?"
"To yi haƙuri"
"Naƙi haƙurin"
Nana ta ɗan sosa kai, ta nemi guri ta zauna.
A yanzu Kusan duk lokacin da Sadik ze shiga gida ya haɗu da Inna, se tai masa faɗan wani abun, kodai na sumar kansa, ko rashin son mutane, ko kuma taɓara, saboda haka yana dawo wa daga makaranta, yake ficewa yawon sa baze dawo ba se dare, se ya tabbatar da Inna tai bacci, se ya shigo ya ɗau Abincin sa ya fice ya bar falon, in ma Mother ze gani ya ganta a lokacin.
Wasu lokutan da ya fara ɓuruntu ze ɗau Abinci Nana ke farkawa daga bacci, ta fuskanci baya shigowa se kowa yai bacci, dan haka ta sa ido sosai ta lura be zo ɗaukar abinci da wuri ba, dan haka ta gane se daren ze zo ya ɗauka.
Har sun kwanta bacci, Nana ta daidaici Inna tai bacci, ta miƙe cikin sanɗa ta fito falon, ta janyo ƙofar falon ta rufe, ta kulle da mukulli ta ciki, ta nemi guri ta kunna TV tai zamanta tana kallon cartoon.
Wajen sha ɗaya da rabi na dare, Sadik yazo yana murɗa ƙofa ze shigo dan ya ɗau Abinci, amma yaji a rufe gam.
Ya jinjina ƙofar yaji ta a kulle, nan ya shiga ƙwanƙwasawa, nan ma ba wani respond.
Yayi mamakin yadda aka rufe ƙofar falon haka, dan ba'a cika rufeta ba, ko da yaushe tana buɗe, saboda ita ce babbar ƙofar da zata sada ka da kowane sashi na cikin gidan, amma abun mamaki yau an rufeta.
Ya zaga ya ɗaga labulen window, yaga koda wani a falon, ya hango hijjabin ta akan 2 seater, yana ganin hijjabin yasan itace, saboda kullum haka take yawo cikin hijjabin nan kamar me takaba, be taɓa ganin ta cire shi ba, kullum da hijjabi take yawo.
"Ke malama zo ki buɗe min ƙofar nan"
Banza tai dashi taƙi ko waigo wa balle ta kalleshi.
"Wai ba magana nake miki bane?"
"Ka nemi ke ta zo ta buɗe maka" ta bashi amsa
"Dalla ki buɗe zan ɗau Abinci"
Tasowa Nana tai, ta nufi inda yake tsaye a window tace "ba za'a ɗakko ba ɗin, idan kana son cin Abincin ka dinga zuwa da wuri kana ɗauka, base ka gama gantalin ka ba sannan kazo kana ɓuruntu kamar ɓera ka tasheni daga bacci ba"
Buɗe baki yai yana mamaki yace "tunda gidan ubanki ne ai dole ki samun doka"
"Ai dama bance Gidan babana bane, gidan babana yana ƙuaye ya mutu, ya barni a gidan Hakimi"
"Ke bana son iskanci, dalla ki buɗemin"
"Wallahi ba zan buɗe ba taimako ɗaya zan iya yi maka"
Ta juya ta nufi dining, ta ɗakko ragowar bredin safe, taje kitchen ta buɗe fridge ta ɗakko ruwan sanyi, Sadik ya zuba mata ido yaga me za tayi.
Ba kunya taje ta zura masa bredi da satchet water tace "ga shi nan, amma kar ka sake zuwa ka damemu"
Galala yabi bredin da kallo da tsananin baƙin ciki da takaici, Nana kuma ta kashe fitilar falon tai tafiyarta.
Ji yai tamkar ya karya ƙofar ya shaƙe Nana, yai mata dukan da seta kasa motsi.
Cike da ɓacin rai ya koma BQ, ya tarar dr. Na zaune yana waya, se wani kashe murya yake cike da tsantsar shauƙi da Soyayya.
Sadik ya kalleshi ya ɗanyi guntun tsaki, ya wuce ya duba fridge ya samo cake, da lemo ya koma ya zauna akan 3seater, yana tura cake ɗin nan kamar ze fashe da kuka.
Gefe