Showing 63001 words to 66000 words out of 259198 words
Chapter 22 - Rudin Kuruciya Book Complete Original By Ayshercool.txt
kallona ya fiye yi se inji hantar cikina ta kaɗa wallahi, ni yanzu ya zanyi?"
Yasmin tace "to ki sauri ki ksrɓa kiyi mana"
"Ke wallahi ba zan ba, note ɗin fa fa yawa, ba yi nake na Assignments ɗin sa ma bayi nake ba, sedai ya kashe ni ya huta kawai"
Class rep ɗin su yace "ba shakka kin shahara Lilly, mitumin nan ba raga miki ze ba"
"Aikuwa sedai ya kashe ni, ni bari ma in tattar maka litattafan, idan ka tashi sedai ka kai masa kawai"
"Aikuwa da kin kyauta"
Lilly ta tashi ta na karɓar litattafan 'yan aji, ta zo kan Farhan, ko littafin ba ta ɗakko ba.
Lilly tai murmushi tace "Sannu basarakiya matar Prince, a dole se an nuna mana sarauta, kina kallo ina haɗa litattatafai amma ko ɗakkowa baki ba"
Kunya ce ta kama Farhan, tai murmushi tace "Yi haƙuri, ba wata sarauta wallahi, hankalina ne yana wani gurin"
"Eh hankalinki na kan tunanin sa ko?"
Murmushi Farhan ta cigaba da yi, ta ɗakko littafin ta bawa Lilly.
Lilly ta karɓ ta fara buɗe littafin tace "Masha Allah, ke komai naki abun burgewa, kalli handwriting ɗinki me kyau kamar ke"
Murmushi ta cigaba da yai tana sunkuyar da kai, Lilly na cikin buɗe littafin ta tsinci takaddar haihuwar Farhan a ciki.
Farahn ba ta san takaddar ta na ciki ba, Lilly ta tsaya tana duba takaddar.
"Wow Masha Allah, Ashe akwai birthday me yaji a school ɗin nan, saura sati ɗaya birthday ɗin ki Ashe?"
Da sauri Farhan tace "A'a ni ba na wani birthday, ban ma san takaddar na ciki ba, bani in ajiye"
Lilly tace "ke kin isa, budurwar Prince guda ace ba za'ai celebrating birthday ɗin ta ba, wallahi dole ayi let me go and show him in case be sani ba"
Lilly tai waje da sauri da takaddar a hannunta, gaba ɗaya Farhan ta rasa abunyi, sam ba ta so abunda Lillyn ke shirin yi ba, meyasa za tai mata haka.
Cikin sa'a Lillyn na fita, ta hango squad ɗin su Sadik ɗin, suna tahowa da alama zasu fita ne, Sadik na maga duk sun bashi attention ɗin su.
Tun lokacin da Lilly ta bi Sadik, suka kai Farhan gida idan ya ganta ya kan ɗan sakar mata fuska, saɓanin da da ba ruwansa da su, hasali ma Juniors suna tsoron sa, kuma ta fanni guda ana son sa saboda yawan kyautarsa.
Ta ƙarasa in da suke, Sadik ya ɗan kalli Lilly, amma be ce komai ba.
Miƙa masa birth certificate ɗin tayi, ya karɓa yace "wannan na menene?"
Tai murmushi tace "nasan wataƙila ba ka sani ba, birth certificate ɗin Farhan ne, on 8th ne birthday ɗin ta, nasan maybe ka shirya wani abun"
Murmushi yai ya fara duba takaddar, yana bawa duk wani abu da ya shafi Farhan mahimmanci.
Ya shafi sumar kansa yace "Wow, naji daɗin wannan Albishir ɗin, nasan ba dan kin gayamin ba ba zata faɗan ba, dole ai celebrating, kina da kyautar wannan Albishir ɗin"
Lilly tace "godiya nake Allah ya raya mana Farhan, ya kaimu lokacin abun"
Sosai Sadik yai murmushi har seda haƙoransa suka fito yace "Ameen"
Ya kalli su Nas yace "guys kuyi gaba, let me go and see her first"
Aminu ne ya fara jan uban tsaki yace "what a shit! Wallahi tun fa Yarinyar nan ta zo school ɗin nan ka zama wani bita zai zai, ni na rasa uwar me kale bi a Yarinyar nan, ni banga wani abun burgewa a tare da ita ba, amma kai ta wani ɓare ɓare a kanta"
Wani ɗan fito Sadik ya ja, me cike da rainin hankali yai gaba abunsa ya nufi ajinsu Farhan"
Nas yace "ƙyale shi, nasan abunyi, nasan dole ze haɗa mata birthday ai, tunda kuɗin banza gareshi be san cuwon su ba, da wannan damar zamuyi amfani musa shi a hanya"
Amin yace "what a good idea, shi banda wawanci ma, wannan 'yar talakwan kawai ya sarara ya watsar da ita, ko wani abun yai mata ba mataki zasu iya ɗauka ba, amma ya kankane ya hana kowa wai shi Aurenta zeyi"
"Bar banza za muyi maganinsa ne"
Ya na zuwa ya tarar da Farhan ta cika tai fam tana zumɓura baki, Lilly na mata dariya.
Yana zuwa ya kaɗa paper a fuskarta, ta miƙa hannu zata karɓa amma ya ɗauke yana murmushi.
Yace "ke yanzu birthday ɗin naki ya kusa, amma baki gayamin mu fara shiri ba"
"Ni ba wani shiri, ni bana wani birthday fa"
"Wannan karon zaki fara, hall zamu kama ƙarami ai shagali kamar ana bikinmu"
"Dan Allah ka bari, base anyi ba fa, ni a gida baza'a barni ba ma"
Tsuke fuska Sadik yai yace "in dan gida ne, ba matsala zan san yadda za'ai a fitomin da ke, amma sekin zo gurin nan, in kuma ba kya so ne ki gayamin"
Ɗago fararen idanunta tai ta sa a nasa, amma ta kasa sake musa masa se shiru da tai ta sunkuyar da kai.
"Idan ina Magana, ko ince ayi abu kina mun gaddama, I will....."
Se kuma yai shiru, ya juya ya fita.
DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA
07063065680.
[6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
RUƊIN ƘURUCIYA
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Writer of
WATA KISSAR..(Sai mata)
ABDUL JALAL
AƘIDATA (paid book)
WUTA A MASAƘA
NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book)
_Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_
⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️
SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA?
MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI.
TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU.
INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS.
KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN.
29
Bayansa Farhan ta bi da kallo, ta na shakkar bijirewa abunda ya ke so, da kuma hatsarin aikata wani abu ba da izini ko sanin iyayenta ba.
Muryar Lilly ce ta dawo da ita hankalinta.
"Haka kurum, zaki mana sagegeduwa, ai nasan in dai ya sani akwai shagali na gasken gaske, dan Prince akwai son harkar girma"
Ita dai Farhan ba tace uffan ba, se tsunduma kogin tunani da tai.
Haseena kam tsaki ta ja, dan ta tsani duk wani abu da ya danganci Farhan, haushin ta take ji nesa ba kusa ba.
"Fatima Hakeem Yola, lambarki ta fito" cewar class captain ɗin su Farhan.
Lilly tace "lambata ta fito a ina? Me nayi?"
"Sir Nazir ke nemanki"
"Innalillahi wa innalillahi raji'un, kashina ya bushe nasani"
Kwashewa da dariya Yasmin tai tace "kaga 'yar iskar ƙarya, ke da kike cewa zaki dinga abun da zaki ɗaga masaa hankali, se kuma gashi kin tsure dan ance yana kiran ki"
Hararta Lilly tai tace "ke dalla ƙyaleni, ni mutumin nan wasu lokutan tsoro yake bani wallahi, gashi jarababbe"
Class rep yace "to yanzu zaki je ne ko kuwa?"
Murguɗa baki tai tace "wallahi ba zani ba"
"Au ba zaki ba, idan ya zo ya ritsaki fa?"
"Wallahi ba zanje ba, fecewa zan gida, sedai komai za'ayi ayi, haka kurum"
Suka dinga yiwa Lilly dariya, ta ɗauki jakarta ta bar ajin gaba ɗaya.
Ko da aka tashi daga Makaranta, ba wanda ya nemi wani a tsakanin Sadik da Farhan, sedai ta tafi gida tana ta zullumin abunda Sadik ɗin ke shirin yi, tana tsoron iyayenta su gano, bata san wani irin hukunci zata iya fuskanta ba.
"Nana wai shirin me kike yi ne haka?"
"Inna kin manta ne, babar 'yar ajinmu ce fa ta haihu yau suna, nace miki zamuje, bana tambayeki ba kika ce kin barni ba?"
Inna tace "ai na manta ne, kuma baki tunamin ba, se ganin ki nai kina shiri kawai dole in tambaya ai"
"Ai na gayamiki kin manta ne"
Inna tace "Allah ya taimaka"
Nana ta cigaba da shafe shafen hodarta tana shiryawa.
Inna na aiki a tsakar gida, sega ƙawayen Nana sunyi sallama.
Inna ta amsa musu tana ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya. Daga bisani tai musu nuni da ɗakin da Nana take.
Kai tsaye suka nufi ɗakin suka shiga.
"Ahh su Nana 'yan mata irin wannan ado haka?"
Nana tai fari da ido tace "to a garin nan idan ban ado ba waze yi?"
"A'a ba wanda zeyi ta Jamilu ba da kanki a sare, ai idan muka wuce ta hanyar gidan me unguwa ya ganki seya rikirkice"
"Wallahi kuwa, dan mun haɗu ɗazu na kai niƙa yace min ina Nana? Nace masa kina gida amma da yamma ta layinsu zamu wuce zamu suna, ina ga ma yana nan a bakin layin yana jiran mu"
Nana tace "ke Hannatu, kama kanki, ni ba sa'ar wannan yaron bace"
Hannatu tace "ke! Jamilun ne yaro?"
"Eh mana ban da ya rainawa kansa hankali ni zece yana so?"
"Ke Nana shikenan kowa yana da saurayi amma banda ke?"
Nana tace "To Alawiyya meye dan bani da saurayi? Ke nifa wallahi ɗan Birni zan aura insha Allah, amma se nayi karatu me yawa, in auri saurayi ɗan gayu ɗan birni"
Hannatu tace "eh lallai kin ɗakko da zafi, ko da yake kuna da 'yan uwa a Birni ai"
Alawiyya tace "Amma ki tsaya ku gaisa da shi, kinga ba daɗi wulaƙanci"
Ɗan shiru Nana tai tana tunani, dan harga Allah ta na son taji ance ita ma ta na da suarayi, ta na son sanin me ake ji a soyayyar idan ana zance me ake cewa?"
Ba ta kuma cewa komai ba ta tashi, ta ƙarasa shirinta suka fito tsakar gida.
Nana tace "Inna zamu tafi?"
Inna ta kalleta tace "zaku tafi ina kenan?"
"Haba Inna, ɗazu fa nace miki ga inda zamu"
Inna ta ƙare musu kallo tace "ba inda zaki"
Saroro Nana tai tana kallon Inna, Cikin rawar murya Nana tace "Inna meyasa? Na tambayeki fa kince kin barni"
"Yanzu kuma nace ba zaki ba"
Ƙwalla ta taru a idon Nana tace "Inna meyasa ba zani ba?"
"Saboda na isa, kin wuce kin ban guri ko senai fatali da ke a gurin nan? Ku kuma maza ku kama hanya ku tafi"
Sumi sumi suka nufi hanyar fita daga gidan.
Nana kam da gudu ta bar tsakar gidan tana kuka, ta rasa wace irin rayuwar takura ce haka, wasu lokutan gani take kamar Inna ba ta ƙaunarta Saboda yadda take takuramata, da hanata sakewa.
Su Alawiyya na fita suka fara gulmar Inna.
"Taɓ Hannatu, dama haka kakar Nanan take, wannan mata anyi jarababbiya, ji yadda ta koremu"
"Hmm kedai bari, shiyasa Nanan ma gata nan jarababbiya, wallahi idan nice ba zan yadda da wannan abun ba, ai kakata ce ba uwata ba"
"Wallahi kuwa balle kuma ni"
Suka tafi suna cigaba da tattauna maganganun su.
Nana da mayafinta, da jakarta da takalmin ta duk a tsakar ɗakin ta watsar da su tana kuka.
Inna ta shigo ɗakin, ta kalli kayan da ta watsar ɗin, ta kalli in da Nana ta dunƙule ta na kuka tace "dan ubanki zaki tashi ki kwashe wannan kayan da kika zubar ko sena saɓa miki? Ni zan miki Magana ki min zuciya ki zubarmin da kaya a tsakar ɗaki, kiyi kukan jini ma tashi daga gurin nan ko in haɗa miki jikinki yanzun nan, mara ɗa'a kawai"
Nana tana share hawaye, ta miƙe ta shiga tattare kayan da ta zubar ta maida su mahallin su, ta cire kayan jikinta, ta ɗakko masu datti ta saka dan ita ma ta ɓatawa Inna rai, ta ɗakko hijjabi ta saka, ta tafi turakar Hakimi tai kwanciyarta.
Inna tai banza da ita bata tanka mata ba, ta cigaba da hidimomin ta.
Ko Abinci dare Nana ta ƙi ci, Inna kuma ba ta takurata taci ba.
A haka Hakimi ya dawo ya tarar da Nana, taci kukanta ta godewa Allah, tana kwance tai shiru a ɗakinsa.
"Subhanallah shalelen ba lafiya ne?" Yai Maganar yana taɓa goshinta.
Girgiza masa kai tayi alamar a'a.
"To meyafaru?"
"Inna ce" tai maganar tana fashewa da kuka.
"Me Innar tai miki?" Kasa Magana Nana tayi, se cigaba da kukanta da tai"
Hakimi yace "shikenan, ya isa dena kukan haka share hawayen.
Suna cikin haka Inna ta shigo ɗakin, ɗauke da kwanukan kayan Abinci.
Kallo ɗaya tai musu, ba tace komai ba ta ajiye ta cigaba da harkokin ta, yasa Nana a gaba suka ci Abincin su tare.
Seda ya tabattar ta ƙoshi, sannan yai mata umarnin taje tai sallar isha'i ta kwanta.
Hakimi ya saba da irin wannan rigimar ta Nana da kakarta, dan haka be takura akan se ya san meya haɗa su ba.
Har washegari Nana ta shirya za ta tafi makaranta, amma ba ta wani shiga sabgar Inna, saboda a ganin ta ta gama dizga ta a gaban ƙawayenta.
Tun da Lilly tai ido huɗu da Sir Nazir a gurin Assmebly gabanta yai mummunar faɗuwa, dan tasan tai masa laifi gagarumi, Allah kaɗai yasan yadda ze da ita.
Ga mamakinta ko kallonta be sake yi ba, balle yai mata Magana ya shareta.
Ita ma share shin tayi, sedai ƙirjinta na ta dukan uku uku.
Aka watse daga gurin Assembly, suka nufi classes ɗin su.
Farhan na tafe sannu a hankali, taji an riƙo hannunta ta baya, cikin hanzari ta waiwaya zaton ta Sadik ne, se dai ba kamar yadda tai tsammani bane.
Salma ce ƙawar Nasreen wanda suke a Ss3, wanda ta gansu tare da su Nasreen ɗin ranar da Nasreen ɗin tai ɓari.
Murmushi taiwa Farhan tace "Farhan ko?"
Farhan ta jinjina mata kai alamar eh.
"Dan Allah in ba zaki damu ba, ina son ki zama sister na a school ɗin nan, if you won't mind"
Saroro Farhan tai tana kallon Salma.
"Anyway, idan an fita break ki zo Class ɗin mu ina son ganinki please"
Farhan ta jinjina mata kai, ta juya ta tafi tana tunanin ita kuma wannan meye haɗinsu, da zata wani ce ta na so ta zama sister ɗin ta?.
A ɗarare Farhan take gudanar da al'amuranta na yau, kasancewar ta na cikin period ne, wanda wannan shine karonta na biyu da farawa, gaba ɗaya ta kasa sakin jikinta, ga shi ƙasan cikin ta na ɗan mata ciwo kaɗan kaɗan, wani lokacin kuma ya ɗan tsananta takura mata.
Ga wata uwar kasala da ke damunta, babban abunda yake ɗaga mata hankali be wuce yadda take jin ƙirjinta wani iri ba, zafi zafi ciwo ciwo, ba ta san wa zata gayawa ba, tafi tunanin ko Cancer ce ta kamata, gaba ɗaya ta kasa gane kanta.
Ana musu lesson amma zuciyarta fal tunani daban daban, a ranta take addu'a idan mutuwa za tai Allah ya nuna mata ta auri Sadik kan ta mutu.
Har aka fita break tana wannan tunane tunanen.
"Yau kuma tunanin me kike yi?"
Firgigit ta dawo hayyacinta, ta kalli Sadik dake kusa da ita a zaune.
"Bakomai"
"Bakomai kamar yaya? Kin san lokacin da na shigo?" Girgiza masa kai tayi alamar a'a.
"Ke kin ma yi min laifi ko ki neme ni balle ki bani haƙuri ko?"
"Lefi kuma?" Ta faɗa a ɗan shagwaɓe kamar za tai kuka.
"Eh laifi mana, na yimin gaddama"
"Ba fa haka bane, ni tsoro nake ji a gida kar ai min faɗa"
"Zam bi hanyar duk da ta dace, ba wanda ze san anyi, kawai za'a ɗan yanka cake ne aci a sha, mu tayaki murna shikenan fa"
Sunkuyar da kai tai ba tace komai ba.
"Ko dai haryanzu ba kya so ɗin"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"Yarinya kin taimaki kanki, da faɗa za muyi"
Ɗan murmushin gefen baki tai, dan ita yanzu halin da take ciki ne yafi damunta, na wannan ciwace ciwacen da take fama"
Idanunta ne suka kuma sauka a hannun Sadik, a ido kawai fatarsa abun sha'awa ga wannan gargasar ta jikinsa da take burgeta.
A hankali ta ɗauke idonta daga kallon hannun nasa ta ɗaga kai ta kalleshi, karaf sukai ido huɗu yace "me kike kallo a hannuna?"
Mamaki ne ya kamata, dama yaga hannunsa take kallo.
"Ni ba hannunka nake kallo ba fa"
"Yanzu kuma ƙarya nake kenan?"
"Wai kai komai nayi lefi ne" tai maganar kamar ta rushe masa da kuka.
Cikin kwaikwayon muryarta yace "kawai ina son in dinga tsokanar ki ne"
Littafin gabanta ta ɗauka ta kwaɗa masa a hannu, ya cigaba dai mata dariya yace "naga hannun nan kamar wani abun kike kallo a jiki, bari in ciro miki shi sosai ki gani" ya kama botir ɗin gabar rigarasa ze fara ɓallewa.
Zaro ido tai ta ja da baya daga kusa da shi, tana kallonsa dariya yai yace "ke da shagwaɓar ki, da tsoron ki, duk ba sa ɓuya, tashi muje ki rakani shop"
"Ni ba zani ba banda lafiya"
"Ke kullum ba ki da lafiya ne? To sekin rakani"
"Ni bana son bi ta wajen SS3 ɗin nan"
Yace "meyasa?"
A ɗan marairaice tace "Kasan wani abu kuwa?" Sadik yace a'a sekin faɗa.
"Kasan wannan Salma ɗin ta SS3?"
Yace "eh na santa"
"Ita ce wai tace wai tana so in zama ƙanwarta, idan aka fita break wai inje"
Take ta ga annurin fuskar Sadik ya ɗauke, wani gumi ya tsatstsafo a goshinsa, cikin kaushin murya yace "meya haɗa ki da ita?"
"Ni ba abunda ya haɗani da ita, kawai ranar na gansu a toilet ne, wai wata ba ta da lafiya, Nasreen wai cikinta ya faɗi, naji tace ina burgeta shine yau tai min Magana"
"Cikin waye ya faɗin?" Ya tambayeta yana tsareta da idanunsa.
"Wai cikin Nasreen ɗin" ta faɗa cike da rashin wayo.
"I hope ba abunda sukai miki?"
Ta girgiza kai "ba suyi min Komai ba"
Be jirata ba ya tashi fuuu yai waje, hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba.
Kai tsaye SS3 ya nufa, hakan yai daidai da fitar malami daga ajinsu.
Ba shakka, ba komai ya kutsa kai ya nufi gurin zaman Salma.
Kallo ɗaya tai masa tace "lafiya ka zo ka tsaya min a ka haka kamar wani ɗan sanda?"
Dukan benci yai da ƙarfin gaske, sannan ya nunata da yatsa yace "kashedi na zo nai miki, nasan kin san Farhan, to idan kuna rashin mutuncin ku da ɓata yaran mutane, ku kiyayi abunda yake nawa, Farhan is my Asset, don't Cross your limit, kince kina son ta zama ƙanwarki, to ta gayamin, wallahi da wasan wasa kika kuskura wani abu ya sameta, wallahi tallahi I will show you what am capable of doing na gaya miki"
Miƙewa tsaye tayi tace "kai ɗan saurara, kar ka gayan