Showing 30001 words to 33000 words out of 259198 words
Chapter 11 - Rudin Kuruciya Book Complete Original By Ayshercool.txt
guda kuma Usaman na sake ƙular da shi, yadda ya nannaɗe murya yana zuba taɓara a waya, duk haushi ya cika shi, se tsaki yake yana hararar Usman, wanda be san me Sadik ɗin yake ba.
"Jeddaty, kamar in janyo Ranar Auren nan haka nake ji, zuciya ta ta kasa nutsuwa da samun sukuni, am about to loose control fa"
"Na fika ƙaguwa Nurain, sedai kayi haƙuri mu jira lokaci, kamar yaune zaka ga yazo, duk abu in dai an sama sa lokaci yanzu zaka ga yazo"
"Hakane Baby na, are you not sleepy?"
"No am not, when am with you, i keep everything aside, kai kaɗai zuciyar take kallo"
"Hmm Beb, yakamata ki kwanta dare ya fara yi fa, But are you on bed?"
"Yeah"
"Are you sure?"
"Quite sure Dear"
"So how do you dressed up, for today's night"
"I just wear my night gound"
"Ok am going to my room now, let me have a 1picture of you with the night dress, so that I can sleep well"
"Ohhk my Baby, as you wish"
Duk wannan wayar da Usman yake a gaban Sadik yake yin ta ba kunya ba Komai, Sadik ya dinga binsa da kallo, harya ta shi ya bar falon gaba ɗaya.
Ji yai ya dena jin ɗanɗanon cake ɗin, dama cin da yake na dole ne, ya miƙe shima ya koma ɗakinsa, ya nemi guri ya kwanta, sedai ya shiga tunani me zurfi, da kwaɗaituwar son yaga hoton da za'a turawa Usman ɗin.
Ina ma Farhan na da waya, da ko ba komai idan yaji muryarta ze ji daɗi a ransa, amma dai yasan ko kusa Farhan ba zata turo masa hotonta a kayan bacci ba, duk da ba mace a gidansu, amma yasan kayan Bacci na mata ba wasu kayan Kirki bane suke sawa, dan mafi akasari kayan baccin yana bayyanar da wani sashi na jikin su ne.
Take zuciyarsa ta cigaba da azalzalar sa, da ƙawata masa abubuwa daban daban, mussaman Farhan ɗin sa, ina ma ko sau ɗaya shima yaga hoton ta a night gound, ko yaya yana son ganin wani sashi na jikinta, a cikin kyakykyawar fatarta me ɗaukar ido.
Rumtse idonsa yai sosai yana sauke ajiyar zuciya, a hankali ya furta Farhan, yai ruf da ciki ya rirriƙe pillow ɗin da yake kai, a hankali ya dinga faɗin "Subhanallahi wabi hamdihi, subhanallahil azeem"
A haka bacci yai awon gaba da shi, sedai kasancewar ya saka abun a ransa, se ga Farhan a cikin baccin sa, a yanayi me wuyar fassara.
Yadda ya kwanta da wannan matsanancin tunanin, haka ya dinga mafarkai barkatai har Asuba, kiran farko ya buɗe idon sa, ya jiƙe sharkaf da gumi, duk da A.C da ke ɗakin nasa.
Tashi yai yayi shiru yana tunanin mafarkin da yai, jinsa yai somehow abnormal.
Tunani ya shiga yi yanzu se yayi wanka kenan? Amma ai mafarki ne kawai, shiru ya kuma yi yana tunani, ya ɗakko wayarsa ya shiga yai searching, tabbas wanka ya kama shi since he has a dreams.
Tsaki ya ɗanyi, ya sakko daga kan gadon, a gurguje ya shiga banɗaki yai wanka yai alawala, ya fito ya zura rigarsa, sedai yana gamawa sega Faruk ya shigo ɗakin nasa, ya kalli Sadik yace "Au ashe ka tashi? Sarkin nauyin bacci, yau anyi abun arziki, dama Daddy ne yayo waya, amma ya nake ganin kanka kamar a jiƙe?"
Tsaki Sadik yai yace "Alwala nayi fa"
"Alwalar ce ka ke a jiƙe haka, kalli jallabiyar taka fa duk ruwa"
Banza Sadik yai masa, ya ɗau turare ya fesa a jikinsa, ya saka hullar tashi ka fiye naci.
Faruk ya kwashe da dariya yace "inyee, Su Auta an girma, iyee sekace wani magidanci wanka da Asuba haka, Lallai ka girma ka isa Aure, na yarda da batunka na cewa da kake ka isa Aure"
Haɗe rai Sadik yai yaƙi cewa uffan, a falo suka haɗu da Usman shima ya fito, suka fito suka tafi masallaci, sedai suna tafe Faruk yana tsokanar Sadik, Sadik ya ƙulu matuƙar ƙulewa, amma yaƙi cewa komai dan kar Daddy ya fuskanci wani abu.
Da suka dawo daga sallar ma Sadik be koma bacci ba, ya nemi guri ya zauna yana ta tunani kala kala daban daban a zuciyar sa.
Haka ya zauna har gari yai haske, ya shirya ya fice dan tafiya makaranta, ba tare da ya shiga ko cikin gidan ba balle ya karya yai musu sallama, direbansa ya fara jan motar kenan ya hango Nana ta fito, se yanzu ya tuna abunda tai masa daren jiya, tabbas ba dan ya riga ya shiga mota ba da Allah kaɗai ze iya raba shi da ita yau, se kuma ya tuna yana taɓata ze sha tujara a gurin kakarsa, kuma Daddy ma ze masa faɗa, ƙwafa yayi dan ko me za'ai sedai ayi amma se yai maganin ta.
Haka ya tafi makaranta yana ƙananun sambatu.
Farhan ta shirya tsaf cikin Uniform ɗinta, sedai a jikinta tana jin tana ƙara ƙiba, dan skirt ɗin da ta sa tana jin yadda ya matse ta sosai, ta juya ta juya ta ƙarewa kanta kallo a madubi, ji take kamar ta cire shi ta canza wani, amma ɗaya skirt ɗin ba a goge yake va gashi ta makara sosai.
Ta ɗakko ƙaton hijjabin ta ta ɗora akan Uniform ɗin sannan ta fito tsakar gida, ta kalli Ummanta da ke kaiwa tana komowa a tsakar gida tace "Umma na tafi"
Ba ta kalli in da Farhan take ba tace "Allah ya kiyaye" cikin yanayin sanyin halin ta, ta wuce ɗakin mahaifinta, se da tai sallama akai mata izinin shiga sannan ta shiga.
Tace "Abba ina kwana"
"Lafiya ƙalau Farhan, za'a tafi makarantar ne?"
"Eh Abba zan tafi"
Ya saka hannu a aljihunsa ya ɗakko Naira ɗari ya bata yace "ga kuɗin makarantar ki, Allah ya tsare kin karya dai ko?"
"Eh Abba na karya"
"To shikenan, Allah ya kiyaye hanya, ki kula da kanki ki kula da addinin ki da mutuncinki kinji Farhan"
"To Abba insha Allah, nagode Sosai"
Ta miƙe ta fito, a soro ta tsaya ta buɗe jakarta ta ɗakko turaren da ta siya da kuɗin da Sadik ya bata, ta shashshafa a jikinta, dan tana matuƙar son ƙamshi a rayuwarta, sedai ummanta bata damu da ta ɗorata a hanya da yadda zatai amfani da kayan gyaran jiki ba, ko da yake yaushe ma ta kulata balle ta koya mata wani abu makamancin haka.
Ta gama shafawa ta maida shi jakarta, sannan ta fita ta nufi titi.
Gaba ɗaya Sadik yau kamar mara lafiya haka yake jinsa, yama rasa gaba ɗaya meke masa daɗi, duk yadda abokansa suka so jansa da surutu amma yaƙi magana, ƙyaleshi su kai, dan sun san haka yake yi wasu lokutan.
Ana ta shirye shiryen fara jarrabawa a makarantar, wasu malaman duk sun ƙarƙare darususskan su, wasu sunyi teses ɗin da duka zasu yiwa ɗalibai, zasu fara jarrabawa.
Farhan ta kasa fita daga ajinsu ma, gani take kamar ita za'a dinga kallo idan ta fita saboda yadda skirt ɗinta ya matse ta sosai, gashi bironta ya ƙare tana son siyan wani, haka ta daure ta fita siyan biron, sedai shop ɗin a kulle yake.
Kawai ta yanke shawarar zuwa gurin Prince ta karɓi aron nasa.
Ta ɗau littafinta ta fita, taje ajin nasu sedai tana shiga ta duba gurin zamansa ta ga baya nan, ita ba iya sakewa take da 'yan ajinsu ba, dan haka ta nemi guri kawai ta zauna tana jiran dawowar Prince ɗin.
Gudu gudu sauru sauri take hawowa step ɗin benen, jacket ɗinta na riƙe a hannunta ɗaya, ɗaya hannun kuma na riƙe da jarkar youghurt, yana daga saman benen a cikin malamai yake hangota tana hawowa, ilahirin jikinta na rawa, kanta a ƙasa ba tsammani tai karo da shi a tsaye yana kallonta.
Ƙoƙarin kaucewa tayi amma yaƙi ba ta hanya, yace "What did I told you last day?"
Kallon hannunta tai da ta riƙe jacket ɗinta, ta kalli jikinta ta ɗan yatsuna fuska tace "sir zafi nake ji shine fa na cire ta"
"Shut up! Bance karki sake cire jacket ɗinki ki tafi haka ba?"
Ta yatsuna Fuska tace "kace"
"Shine kika cire rigar kike yawo da ita a hannu dan rashin kunya ko?"
Shiru tayi tana zumɓura baki taƙi Magana, yace "oya wear it back"
Tana harararsa ta gefe haka ta maida rigar, sannan ya batta ta tafi.
Tana barin gurin tace "ɗan rainin hankali kawai" ta sake cire rigar ta tafi aji.
Corper Nura yace "Nayi matuƙar mamakin ganin irin wannan dress code ɗin na student, a garin Kano"
Nazir yace "ai ba kai kaɗai ba, abun da mamaki kam kamar ba garin musulmi ba, kalli yadda suke yawo kamar ba musulmai ba, kuma babban abun takaicin an rasa me musu magana akan wannan shigar ta yaran, kuma su kansu iyayen suna kallo amma sun yi shiru"
Nura yace "amma hakan be dace ba, ze iya buɗe ƙofar ɓarna a tsakanin malami da kuma ɗaliban kansu"
Nazir yace "ai kai kaga haka, su ba wannan ne a gabansu ba, su makarantar burinsu yadda zasu samu kuɗi, su kuma iyayen burinsu ace yaransu na makaranta me tsada, amma ɓarna kam a makarantar nan sedai ai shiru kawai"
"Subhanallah, Allah ya kyauta"
Nazir ya amsa da "Ameen"
Farhan kuwa gajiya tai da zaman jiran Prince, ga shi 'yan ajin se fitsara suke kala kala a gabanta, dan haka ta tashi zata bar ajin, harta fito taji yace "See me here"
Ta waiga taga yana tahowa a hankali kamar mara lafiya, tai murmushi tace "ina ka tafi ne na daɗe ina jiranka fa"
"Naje cin Abinci ne ina jin yunwa, kuma nasan idan nazo ma nace ki rakani ba zaki bini ba"
Tai murmushi ta koma ajin nasu, tana gaba yana binta a baya, sedai shima ya lura da yadda take tafiya a kunyace saboda yadda skirt ɗin ya matseta sosai.
Seda ta tsaya ya zauna sannan itama ta zauna, tace "dama pen nazo ka aramin, naje in siyo shop a rufe"
Murmushi yai yace "in baki pen dai ba in baki aro ba"
Ya zura hannu a aljihunsa ya ɗakko sabon biro ya bata ta karɓa tace "Nagode sosai Allah ya saka da Alkhairi"
Be magana ba se jinjina mata kai da yayi, ta zauna tana ta 'yan rubuce rubucen ta, da alama tana solving maths ne, shikuma ya ƙura mata idanun sa, ko ƙiftawar kirki ba ya yi, se wata irin ajiyar zuciya yake.
Ta kalleshi "baka da lafiya ne?"
Ya girgiza masa alamar a'a.
"Amma na ganka wani iri yau"
"Am sick" ya bata amsa a hankali.
"Meke damunka"
Be magana ba ya lumshe idanunsa, ya kuma buɗe su a kanta.
Cikin damuwa tace "dan Allah meke damunka?"
"Nothing, cigaba da aikin ki"
Jiki a sanyaye ta cigaba da rubuce rubucen ta, tana monitoring ɗin Sadik ɗin.
Can aka jima ya tashi ya bar seat ɗin, ya koma baya ya kwanta akan wani benci.
Gaba ɗaya Farhan ta damu, ta tashi ta bishi tace "Ko Clinic zan raka ka su dubaka?"
"No zan ware insha Allah"
"To kaƙi gayamin meke damunka"
"Idan na gayamiki zaki min wani kallo na daban, just forget about it, kije class ɗinku kar Malami ya shiga"
Taslim ta kalli in da suke tace "lallai yau ana jin soyaya, sedai naga fuskokin masoyan ɗauke da damuwa"
Kallonta kawai Farhan tayi, ta tashi ta bar ajin cike da damuwa tana tunanin meya sa Prince a wannan mood ɗin haka?.
A ƙofar ajinsu taga Dodon nata wato Sir Nazir, ya tsareta da ido ta maze tare da ƙi ɓoye tsoronta, "Allah ya shiryeki, ina tausayawa rayuwar ki a nan gaba"
Farhan ba tace Komai ba ta wuce cikin ajin nasu, dan ita bata damuwa da duk surutun da Nazir ze mata akan Sadik.
Seda duk aka koma aji sanna Meena ta kalli Taslim tace "Ke nifa na tafi in je inga ta ina zan fara kaiwa gayen nan hari"
Taslim tai murmushi tace "jarababbiya idan me taurin kai ne kamar Naziru wahala zaki sha a banza a wofi"
"Shi ya isa ma, shi ma Nazirun dan ban dage bane, amma da shi ɗin banza"
"Hmm to ai shikenan maji ma gani"
Meena ta miƙe ta gyagyara zaman Uniform ɗinta ta fice.
Sadik ya rasa abunda yake masa daɗi, ya taso da niyyar ya koma gurin zamansa ya zauna, sedai idonsa ya sauka akan Taslim, da ta ɓalle botir ɗin sama na rigarta, wanda hakan ya bayyana wani sashi na ƙirjinta, dan kana iya ganin jar kalar brezia dake jikinta, ta nutsu tana danna waya.
Wani uban tsaki Sadik yaja ya kauda kansa, wanda seda ya janyo hankalin wasu daga 'yan ajin kansa.
Cikin muryarta me cike da iyayi Taslim tace "Prince what's going on ne? Gaba ɗaya yau ajin nan ba daɗi saboda mood ɗinka, what happens ne?"
Be ce mata uffan ba ya ɗauke kansa daga kallonta, mafarkansa na jiya ne kawai suke dawo masa kansa, zuciyarsa na ta raya masa abubuwa daban daban, na arziki da na banza.
Ganin Sadik ba shi da niyyar yin magana yasa Taslim ta ƙyaleshi, s cigaba da danna wayarta.
Mubarak Babba ne ya shigo class ɗin, ya nufi inda Taslim take, yana zuwa ya kalleta yace "you look sexy today Beb, kinyi kyau sosai"
Wani killer smile tayi, ta ɗan kashe masa ido, ta cigaba da danna wayar, zama yai kusada ita yasa hannu ya karɓe wayar yace "kalleni mana, ina Magana kina danna waya"
Hararsa tai tace "dan bani wayata"
"Sekin kalleni zan baki"
Idonta cikin nasa ta kalleshi tace 'na kallka yanzu bani wayata"
Wani irin kallo yake mata sanna yai murmushi yace "kinga abunda na turamiki jiya?"
"Ban gani ba"ta bashi amsa.
"Why?"
"Z" ta faɗa tana hararsa.
"Naga dai alama haryanzu fushi kike dani, duk da na baki haƙuri, shikenan in kin huce ma daidaita, But before ya kamata a rufe nan"
Ya kai hannu ƙirjinta, ya rufe botir ɗin ta dake buɗe tare da kashe mata ido.
Zumɓura baki tai taƙi kallonsa, ya gama surutansa ya fita.
Meena kuwa safa da marwa ta dinga yi a sashen Office ɗin da Corper Nura yake, can cikin sa' se gashi ya fito da litattafai a hannunsa, da marker da alama aji ze shiga.
Tace "good afternoon sir" waigowa yai ya kalleta yace "Afternoon how are you"
"Fine sir"be jira abunda za tace ba yai gaba abunsa, haushi n ya kamata na tafiyar da yai b tare da ya sake kallonta ba.
"Hey fine girl, what are you doing over there?"
Ta juya ta a wake magana, ɗaya daga sababbin corpers ɗn da suka zo tare da Nura ne, me suna George.
Ta ɗan haɗe rai tace "Nothing"
"But you are suppose to be in your class now, Why are you here?" Yai maganar yana sake ƙare mata kallo kamar maye.
Tsaki taja ta bar gurin, shikuma yabi bayanta da kallo yadda take tafiya, ƙwaurinta duk a waje ga matsatsen skirt da ɗan ƙaramin veil.
Ya jinjina kai yace 'lallai makarantar nan akwai 'yanmata'
Tana tafe tana tunanin ya zata ɓullowa Nura kuma.
Ta koma ajinsu tana zancen zuci.
Farhan ana tashi ta tafi ƙofar ajinsu Prince ta tsaya, tana nan tsaye se gashi ya fito, ta kalleshi tace "Sannu"
Yace "yawwa"
"Kawo jakar in riƙe maka"
"No kar in ƙara miki nauyi mu tafi kawai"
"A'a ka kawo tunda ba ka da lafiya"
Ta karɓi jakarsa ta haɗa da tata, Nas yace "shege Prince, a ɓoye dai ka gama da zuciyar ƙwailar nan, ta gama faller maka wallahi"
Wata uwar harara Farhan taiwa Nas, Nas yace "ke ni kike harara? Dan kina zuwa ajinmu ki zauna na ƙara ganinki a ajin sena ɓallaki"
Prince yasa hannunsa ya kamo na Farhan, sedai yana yin hakan yaji zuciyarsa tana harbawa da sauri, ita ma nata ɓangaren hakan ne, bugun zuciyarta ya ƙaru sosai.
Sadik ya dake yaja hannun ta, su kai gaba.
Nas yace "Lallai Prince Mugun ɗan rainin hankali ne, yanzu har wannan 'yar ta fara wayewa ni zata harara"
Mubarak babba ya shafa fuskarsa yace "Yarinyar nan ba ta taɓa burgeni ba sam, ni hasali ma haushinta nake ji, amma yau tunda na ɗora idona akan hips ɗinta raina ya biya, Uniform ɗinta na yau sunyi pitting ɗin ta sun mata kyau sosai"
Amin yace "kaifa Babba wani lokacin Akuya ne, Kamar ya ranka ya biya?"
"Kamar yadda na faɗa mana"
Nas yace "Allah yasa Taslim ta jika"
"To taji ɗin seme? Dole wannan yaron ya liƙe mata, shiyake ganin abunda ya gani, sedai na ga shi kamar soko ne"
Wani wanda suke aji ɗaya da Mubarak me suna Ahmad yace "kai me kake nufi ne Babba?"
"Zan kauda damuwata ne" ya faɗa yana murmushi.
Nas yace "kai kamarya, wai kana nufin kai a yanzu haka kasan mata?"
"Me za'a fasa? Kana tunanin kowane ke iya tsallake sweet sixteens ƙalau? Ga wannan mata muna shiga muna fita a cikinsu, suna dressing kamar a turai, mu zauna guri ɗaya da su, mu ci Abinci tare dasu, muyi raye raye da wasanni tare, kai this is not easy fa"
Amin yace "taɓ ashe mu bamu san komai ba, ai mu iyakar mu romance da 'yan kallece kallace"
Nas yace "baka san komai ba dai, dan nima kawai dai eh"
Nan suka saka shewa, Amin yace "ashe ni kuka bari a tasha?"
Nas yace "tunin ma, amma fa nima zuciyata na ƙawata min budurwar Prince ɗin nan sosai wallahi"
Babba yace "What so ever, kan in graduation a school ɗin nan, Wannan Yarinyar sena san abunyi a kanta, she looks sexy in her every movement"
AMIN AFUWA KWANA BIYU NAYI BUSY NE SOSAI, AMMA INSHA ALLAH ZAN ƘOƘARI IN CIGABA DA KAWO POSTING AKAI AKAI
You can start subscribing now @₦300 only, Free pages are not much.
DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA
Ayshercool
07063065680.
[6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
RUƊIN ƘURUCIYA
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Writer of
WATA KISSAR..(Sai mata)
ABDUL JALAL
AƘIDATA (paid book)
WUTA A MASAƘA
NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book)
_Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_
⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️
15_16
Suka sake kwashewa da dariya gaba ɗaya.
Farhan kuwa har gaban mota ta raka Sadik, ya kalleta yace "shigo mu tafi mana"
Ta girgiza masa kai tace "A'a, na ga ba ka jin daɗi,